Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun, ya sha alwashin zai rushe duk wani gida da aka gano masu garkuwa suna buya a cikinsa, kamar yadda daily trust ta ruwaito.
Gwamnan yace ba zai yuwu mutanen da suka hana jama’a zaman lafiya kuma ace suna samun wurin É“oyewa ba.
Gwamna Abiodun ya roÆ™i al’ummar jihar musamman masu gidajen haya, su tabbatar sun san waÉ—anda suke baiwa gidajen su.
Gwamnan yayi wannan gargaÉ—i ne yayin da yake jawabi a wurin wani taron kiristoci karo na 11 a Yewa, jihar Ogun.
Wannan ba shine karon farko da gwamnan Ogun yayi wannan gargaÉ—i ba na rushe duk wani gida da masu garkuwa ke amfani da shi.
A shekarun baya gwamnan yayi wannan gargaɗi, inda har yayi barazanar kama mamallakin gidan, wanda ya baiwa baragurbi maɓoya a gidansa.
Source: Isyaku.com