Babbar mahana: Gwamna Ya Sha Alwashin Rushe Gidaje a Jiharsa Saboda Masu Garkuwa da Mutane

 Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun, ya sha alwashin zai rushe duk wani gida da aka gano masu garkuwa suna buya a cikinsa, kamar yadda daily trust ta ruwaito.

Gwamnan yace ba zai yuwu mutanen da suka hana jama’a zaman lafiya kuma ace suna samun wurin É“oyewa ba.

Gwamna Abiodun ya roÆ™i al’ummar jihar musamman masu gidajen haya, su tabbatar sun san waÉ—anda suke baiwa gidajen su.

Gwamnan yayi wannan gargaÉ—i ne yayin da yake jawabi a wurin wani taron kiristoci karo na 11 a Yewa, jihar Ogun.

Wannan ba shine karon farko da gwamnan Ogun yayi wannan gargaÉ—i ba na rushe duk wani gida da masu garkuwa ke amfani da shi.

A shekarun baya gwamnan yayi wannan gargaɗi, inda har yayi barazanar kama mamallakin gidan, wanda ya baiwa baragurbi maɓoya a gidansa.

Source: Isyaku.com

Agajahub publishers

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top