Muhimmancin Turaren Miski Ga Dan Adam Daga Zauren Sirrin rike miji Islamic Chemist and research center*
![]() |
Agajahub publisher |
Shi dai Miski turarene mai kamshi, kamshin kuma mai sa nishadi da
annashuwa.
Yana da kyau kwarai da gaske a ce a matsayinki na mace ko da yaushe ya kasance kina da miski a dakinki domin ana so ko yaushe ki rika amfani da shi.
Mun riga mun sani shi kamshi abu ne da ya ke kara dankon soyayya,
kuma yake dawwamar da ita, sannan miski yana dauke da sinadarai
da dama da suke ba wa farjin mace kariya daga cututtuka, saboda
haka ana so kullum mace ta rika amfani da shi.
Kalolinshi guda uku uku ne.
Akwai fari mai kamar madara mai kauri: Shi wannan ba’a sashi a
cikin farji, saboda a daskare yake bai fiya narkewa ba, sai dai a shafa shi daga wajen farji.
Akwai fari kal kamar ruwa, kamshinsa kusan daya ne da mai kaurin,
sai dai shi ba shida kauri, to shi za’a iya sawa a matsi da shi. Tabbas
yana taimakawa har a bangaren auratayya, kuma duk sanda mijinki
ya ji wannan kamshin ko bakwa tare ta zai tunaki Zai yi sauri sauri
ya dawo gida kinga miski yayi amfani kenan.
Akwai jan miski wannan masu fama da matsalan aljanu suke shafashi, domin yana fatattakar aljanu da iznin Allah. Abinda na sani
dai idan mai aljanu tana shafa shi in dai an riga an yi mata rukiyya, to
suna rabuwa da ita. Amma idan ba ayi ba to za ka ga bata san
kamshinsa, ba za ta yi amfani da shi ba.
Shi ana shafa shi ne a duk jiki da gabar da ta fi yi wa mai fama da aljanun ciwo. Kun san fa miski asali ya samo yana da kyau kiyi taka-tsantsan wurin amfani da shi, domin ba wai kawai dangwala za ki yi
da yatsarki ki saka ba a’a, Za ki nemi ruwan dumi ne ba mai zafi sosai ba, ki je ki kama ruwa da shi, ki wanke wurin sosai, sannan ki samu hankici mai kyau ki goge ko da Tishu. Daga nan sai ki samu“Cotton bud” wato abin sosa kunne.
Sai ki dangwalo da shi, sannan ki tura shi a gabanki, ki dan matse
kafarki sai ki cire ki jefar. To in sha Allahu ko ‘fant’ dinki kika cire
kamshi za ki ji ba Zai yi wari ba. Babu kunya cikin neman ilmi musamman ilmin addini, babban abun kunya a ce mijinki zai
kusance ki kuma ya ji farjinki yana wari, haba! wannan ai ba aji.
Zaki iya dafa ganyen magarya in ya huce ki zuba miskin kina kama
ruwa da shi. Sannan ana so duk sanda za ki saka ‘pant’ dinki to ki
diga miskin a kai duk wasu kwayoyin cuta za su mutu da yardar
Allah. Ana kuma shafa miski a jiki ana kuma hada shi a cikin Humra
yana kuma taimakawa macen da ta haihu kwarai da gaske. Yana da
kyau a ce a matsayinki na mace kar a rasaki da wadanna abubuwan
Miski:
Ganyen Magarya
Hulba
Habbatussauda
Man Zaitun
Man Tafarnuwa
Khaltufa
Lalle
Zuma.
SIRRIN NI’IMA
*TAKAITACCEN MATSI DA NI’IMA INGANTACCE*
yana kara matse gaban macce ya kara mata ni ima tafi sauran mata
*SIRRINA NA DAYA*
Kisamu bawon bagaruwa kidafa kirinka sit bath dashi mace mejego ko macen datajita a bude koda budurwace.
*SIRRIN NA BIYU*
Kisamu garin xogale da kwaro da man kadanya da man shanu da man xogale ki hada kicakudasu su hade jikinsu sai kirinka insert da la.asar xuwa magrib ko isha.i.
*SIRRIN NA UKU*
Kisamu furen tunfafiya da yayan bagaruwa d garafuni kitasfa ruwan ya huce ykoma dan dumi kirinka yin tsarki dasu.
*SIRRIN NA HUDU*
Kisamu ganyen magarya da bagaruwa ki tafasa kitace sai ki xuba turarem miski a ciki ki rinka sit bath d tsarki
*SIRRIN NA BIYAR*
Kisamu lalle 1cup ki dafa kirinka sit bath dashi.
*SIRRIN NA SHIDA*
Ki samu xuma ki rinka dangwalowa kina insert nata, sanna kisamu man zaitun da beby oil ki rinka shafawa a kasan HQ xakiga gyara
*SIRRIN NA BAWKAI*
Ki samu tagargaje ki daka kidama cikin ruwa ki rinka wanke HQ, sanna kisaka xuma.
bayan nan kuma idan xako kwanta sekiyi insert n almiski orginal.
*SIRRIN NA TAKWAS*
Ki samu nonon rakumi da garin ridi sai ki hada ki rinka sha akai akai.
*SIRRIN NA TARA*
Ki samu man hulba da pure madara ta shanu kota ruwa peak da xuma kadan ki hada ki rinka sha kafin barci d 3haurs
*SIRRIN NA GOMA*
Ki sami kankana da madara ki tace kisata a fridge kita sha.
kirinka hada gurji da xuma d madara ki sha..
kirinka kunun aya dayaji kayan kamshi.
yawaeta cin kayan marmari da kayan lambu..
sanan kirinka amfani da sabulun zaitun da habba.
yawaita amfani da ruwan dumi lokaci sanyi xaki iya amfani dana rijiya ko bamfamo saboda bayada sanyi.
*Daukewar sha’awa*
ki samu nonon rakumi da garin kanumfari ki hadasu kisa rabin karamin cokali na kanumfari da kofi 1 nabi nonin rakumi…ki rinka sha safe da yamma.
[2/6/2020, 1:50 PM] Talali: *TSAFTA DA GYARAN JIKI*
wasu matan duka wadannan na marmari akeyi da zaran anyi aure an fara haifuwa shikenan amma ki gwada rike gyaran jiki kamar yanda kike lokacin kina amarya Za kisha mamaki karin ni.ima matsi gyaran nono idan kin haifu sarrafa miji akan gado kiga tayaya zaiki kulaki?ai kullum mararin dawowa zaiyi
YAWAN ROKO kafin aure mace kunyar rokon namiji take harma idan zai mata kyauta saiya dage ta karba to amma da zaran anyi aure an dauki lokaci saita rinka ganin ai wata dama ta samu wanda kullum zata tatsi kudi daga gareshi wannan shine zaisa da kin tambayeshi ya bata rai ya fice yabar gidan ahaka kuma harma yaji bayason shigowa gidan to wannan shima ki rage kisha mamaki shida kansa zai rinka baki to wadannan abubuwa hudu sune abu na farko da zaki fara dasu idan kika binciki kanki kika tsallakesu sai kuma kizo ki karanta mataki na gaba bari mu fara da namiji me jaraba wanda yafison kwanciya da mace fiyeda komai shine wanda kullum baya fashi to idan kika samu kanki agidan irin wannan kuma kinason samun soyayyarsa kada ki rasa abu biyu wato ni.ima da matsi daga baya kuma kina kula da nono da hip da dai sauransu bari mu fara da ni.ima zallah da mallaka wanda shi wannan hadin har yanzu ba asamu garin ni.ima da yake mallaka ya samarwa mace ni.ima da ba kakkautawa kamarsaba idan har kika shafe mako guda kinashan wannan baki wadatu da ni.imaba to ki bincika kinada matsalar infection kinemi magani Itatuwane guda goma ake hadawa da dabino da gyada da aya da ridi da gyadar mata adaka ayi garinsu anasha da nono ko madara kullmu
safe da yamma….✍🏽
GYARAN / TSAFTAR FARJINKI
tsaftar farji Ana so mace Tun tana karama iyaye su rinka yi Mata tsarki da ruwan dumi domin ruwan dumi yana Hana kwayoyin cut a shiga cikin farjinki har lokacin da Zaki mallaki hankalinki ki Dora Daga Inda iyayenki suka tsaya.
Ruwan magarya Miski Sannan Daga lokacin da kika Fara al’ada kuma aiki ya karu sai ki rinka amfani da ruwan magarya bayan kin gama al’ada sannan Zaki iya saka miski saboda karni wato Zaki tafasa ruwan tareda ganyen magarya danyensa ko bushashe ki saka miski sannan Kiyi tsarki dashi kamar na kwana 3 zai kashe kwayoyin cutarda Zaki iya dauka a wanna lokacin kuma zai hanaki warin gaba wanna matar aure yana da kyau ta rinka yinsa.
BUDURWA KO YAR’UWA
a takaice dai kina ( budurwa ko bazawara ) babu ruwan ki da saka komai a farjinki da sunan matsi kedai ki kiyaye da wannan wato amfani da ( ruwan magarya da miski ) lokacin al’ada….✍🏽
TSARKIN MACE MUSULMA 010*
DAGA CIKIN HUKUNCE- HUKUNCEN DA SUKA KEBANCI MACE MAI AL’ADA
NA UKU: DAWAFI A DAKIN KA’ABA.
Dawafi na farilla ko na nafila a dakin Allah da ke makka (Ka’aba) shima haram ne ga mai al’ada, kuma ko tayi ma bai inganta ba, saboda fadin Manzon Allah sallalahu alaihi wasallam ga Nana Aisha Allah Ya yarda dai ita ya yin da tayi al’ada -a hanyarsu ta zuwa Makka- sai ya ce da ita: ((ki aikata duk abin da alhazai ke aikatawa, sai dai kada kiyi dawafi a dakin Allah har sai kinyi tsarki)).
Amma sauran ayyuka kamar: Safa da Marwa, tsayuwar Arfa, kwana a Muzdalifa, da kwana a Mina, da jifan shedan, da sauran ayyukan hajji ko umara duk ba haram ba ne ga mai al’ada,- wato za ta iya yin su a lokacin da ake yinsu babu matsala-.
Saboda haka in da mace za ta yi dawafi tana cikin tsarki, gamawarta ke da wuya sai al’ada tazo mata, ko kuma ta gama dawafinta harma ta fara safa da marwa sai al’adarta ta zo, to bata da wata matsala, za ta iya ci gaba da safa da marwarta. –matukar dai baza ta bata wurin ba, in kuwa bata da kyakkyawan kunzugu to sai ta fita ta kintsa kanta sannan ta dawo ta ci gaba-.
TANBAYA: mace ce ta dauki niyyar aikin hajji ko umara, sai kuma al’ada tazo mata kafin ta yi dawafi, ga shi kuma ba ta da damar ci gaba da zama a Makka har zuwa ta yi tsarki, to ya zata yi?
AMSA: Sheikh Uthaimin ya ce: ta yi dawafinta haka; saboda yanayin lalura. Wannan kuma ita ce maganar da shehin muslumci Ibn taimiyya ya rinjayar, kuma shi ne zance mafi dacewa, sai dai wajibi ne ta kula sosai ta yadda jini ba zai ringa digowa ba har ya zama ya lalata masallaci.
NA HUDU: SARAYAR DAWAFIN BANKWANA.
Idan mace ta kammala aikin hajjinta ko umararta, amma sai al’ada ta zo mata kafin lokacin tafiyarta garinsu, kuma bata yi tsarki ba har lokacin tafiyar ya risketa, to ya hallata ta tafi koda kuwa bata yi dawafin bankwana ba, dalili kuwa shi ne hadisin Abdullahi dan Abbas Allah Ya yarda da su, ya ce: (( an umarci mutane da su sanya dawafi a dakin Allah karshen abin da za su yi, sai dai an yiwa mace mai al’ada rangwame)).
Haka nan zuwan mace mai al’ada bakin kofar masallaci mai alfarma ta yi addu’a yayin da za ta bar makka, ba mustahhabi bane, saboda rashin dalilin yin hakan daga Manzon Allah sallalahu alaihi wa sallam, ita kuma ibada ana gina ta ne bisa dalili, yin hakan ma ya saba ma abin da ya zo daga Annabi sallalahu alaihi wa sallam a cikin kissar Nana Safiyya Allah Ya yarda da ita lokacin da al’ada ta zo mata bayan ta gama dawafin Ifadha (dawafin aikin hajji), sai Annabi ya ce da ita (( ba komai, mu tafi kawai)) bai umarce ta da zuwa kofar masallaci don yi wata addu’a ba, da kuwa yin hakkan ibada ce abar so, to da manzon Allah ya bayyana a wannan lokacin.
Amma dawafin aikin hajji ko na umara, su basa saraya akan mai al’ada, za ta jira tayi tsarki ne, sannan ta je ta yi,- ko kuma in tafiya ta zo kafin tsarki, sai ta yi kunzugu taje ta yi haka, kamar yadda bayani ya gabata-.
INKIKA GA BAKYA JIN DADIN RAYUWAR AURE TOH KI BINKICI KANKI KEMA*
Yar uwa idan kinason kiji dadin aure ki dena kallon rayuwar gidan wasu, kece zaki sauko kasa daidai da karfin mijinki ku gina rayuwa bisa gaskya da amana. Babban makamin ribace mu shine ki kokarin sanin bukatun mu wato (NEEDS) Inkika san wannan kika cire kasala kika kula dasu, koma kurum ki kwanta kin mallake mugun kingama komi girman kansa🌻
Karkice komi sai kinjira yai magana, kema rika fadamasa cewa wane ina kaunarka, hasali ma kike fadamasa wannan kalmar fiye da yadda shi yake fadamiki. Ina sonka tare da kaunarka fiye da komi koda hakan zai zamo karshen numfashina, duk sanda na bude ido na ganmu tare nakanji na kara samun nutsuwa, ko bani lfy naji ka dafa ni kaimun murmushi tun kafin kai mun addu’a na kanji sauki ya fara samuwa. Damuwarka – damuwata ce my King, dade sauran kalamai komi talaucin mijinki kuwa, kike farautar maganganu, sannan ki lura da tsafta saboda namiji ko baida cikakkiyar tsafta yakanso mace mai tsafta.
SAI SAURAN TRICKS DIN DON INGANTA ZAMANTAKEWAR
➡Kina son mijinki kar yai sha’awar wata ?
💚Toh zamo mai tsafta kamar yadda nace.
➡Kina son kada mijinki yake yin zina ?
💚Ki kusance shi, ki zamto tare dashi ko yaushe, karkike jiran sai shi ya nemeki shimfarda ko yaushe.
➡Kina son hira da mijinki ?
💚Ki zamo mai auna magana kafin ta fito, tare da tanazar sabon mau’du’i kullum
➡Kina son kyauta daga mijinki ?
💚Ki yawaita godiya agaresa adukkan abunda ya kawo ya baki.
➡Kina son mijinki ya aminta dake ?
💚Kar kike yi mishi sata, kar ki yawaita roko, da dora lalura mai nauyi da kikasan ba dole bace a kansa.
➡Kina son mijinki ya rika yi miki fara’a ?
💚Ki kiyayi aikata abunda baya so.
➡Kina son mijinki yake hadawa da kunyarki ?
💚Ki zamo mai hakuri, ladabi da nutsuwa
➡Kina so mijinki yaga girmanki ?
💚Ki zamo mai rike sirrinsa, mai kwantar masa da hankali yayin da ya shiga damuwa, haka zalika ki zamo mai nuna kunya wasu lokutan
➡Kina son mijinki ya rika yabonki ?
💚Kar ki zama mai roko akoda yaushe, tare da fadamasa cewa ai mijin wane kaza yake mata shi.
➡Kina son mijinki ya zama mai gaskiya a gareki ?
💚Kada ki yaudareshi, kike rike sirrinsa, ki sani mijinki rabin jikinki ne don haka kyautata zama a tsakanin ku shine rahama da jin dadi a tsakanin ku.
Mata Aure da maza amana ne a gareku, kamar yadda kuke amana a garemu.
Aurene kadai halattacciyar hanyar karuwar yawan jama’a a duniya, inta sami matsala ya’yan banza ne zasu cika duniya su addabi kowa kamar yadda aketa wai wai yanzu. So muke kowa sha’awa abun ya kamasa ta yadda za’a kange 6arna🌺
Allah ka karama rayuwara aure albarka, ka kau da dukkan sharri, ka hada kowa da abokan xama nagari amin🌻
[2/6/2020, 1:56 PM] Talali: *ABUBUWAN DA KO KUSA KARKI YARDA KIYI SU A GABAN MIJI*
1) Tsifar kai. Musamman idan kitson ki yai tsufa.
2)Daurin kirji, sai dai in wanka kika shiga.
Ko wankan ma, make it stylish & sexy. How?
Ki kama bakin zanin duka biyu, ki daura a kijiki ki kulle, yanda zai zauna das a kirjinki yayi kuma lebatu wic looks very sexy.😃
3) Karki yarda ki tauna kashi a gaban miji.
Domin taunar kashi da shan rake kan canza yanayin mutum.
In har kina so kici kashin bari sai bakwa tare.
4) Idan ke maici ce sosai, karki bari miji ya ganki da tulin abinci a gabanki.
Yi kokari kici rabi kafin ya dawo don kinga in zaki kara kadan zaki diba.😃
5) Don Allah karki gyatsa ko tusa a gaban miji.
I beg you.
6) Karki sakace ko kaki pls.
7) Karki kuskura kiyi soshe soshe domin Bera ce kawai take wannan halin.
Allah kiyashe ku.😃
8) Karki yi karya a gaban sa.
9) Karki zagi, karki kuskura ko da kuwa an bata miki.
Musamman Ashar.
Karki ki yarda.
10) Kar ki kawo masa gulma domin zaki zubar da kimar ki a idonsa.
11) Karki yarda ya ganki da kaushi don Allah… yasa ku dace da fatan zaku gyara rayuwar aure ba abin wasa bane..
Daren angwanci
Daren angwanci wani dare da ake farinci, idan an wayi gari cikin sa rana ce masoya basa mantata ranar fari ciki.
zaku kasance awani hali mai tattare da shauki da zumudi na kasance warku a matsayin abu daya daren daraja ga ma’aurata kenan da zarar an kai amarya gidan mijinta ango kenan, Iyayanta da kawa yanta zasu barta a daki tana jimamin kasancewar ta a wannan yana yi Na zama amarya
akan so bayan an watse ambar amarya ta tashi ta dan gyara abin da take ganin bazai kayatar mata DA ango ba a wasu guraran kawayan amarya suna tsayawa har sai an kawo ango wannan baya cikin al’ada an fison abar amarya daga ita sai ango
suci amarci kai ango kashigo kuyi abinda addini Ya yarda dashi Na sanarda ita yaya addini kuyi sallah muna godiya ga Allah kuci daga abinda Allah Ya baka a wannan dare domin more amarci
Na biyu shine kokarin tafiyar da kunya tsakanin ma’aurata kasancewa sababbin ma’aurata duk baki suke ga wannan harka ta ibadar aure, dole Ya kasance akwai kunya da yar fargaba game da daren, don samun cikakkiya nasara daren farko, sai ma’aurata sun rage jin kunyar dake tsakaninsu, Ya kasance suna tattaunawa kan batun ibadar aure, da yadda suke fatan daren farkonsu Ya kasance
DA kuma dokinsa dasa kyawawan tunani cikin zuciya game da shi tun kafin zuwan ranar a Nan aikin ango ne Ya rikka Bi a hankali, cikin wasa da raha da zolaya ta hanyar amfani da kalmomi makimanta ba masu nauyi ba, kuma Ya kasance suna cike DA shauki, har yaga Ya zakulo amaryarsa ta rage jin kunya, in ma dai ba ta daina ba, fada matan zai sa ta zama cikin sanin abinda ka iya faruwa, haka kuma yana da kyau ma’aurata su nema tare da karanta littafai dasu kai bayani kan ilimi ibadar aure don a fahimce su.
SHIRYA JIKI DA JINI: domin dai jiki da jini kamar inji ne ga fetur din gabatar da ibadar aure: don haka yana da alfanu ga ma’aurata su inganta lafiyar jikinsu da ta jininsu ta hanyar cin abinci mai kyau DA gyara jiki musamman ganyayyaki da ya’yan itatuwa da yawan motsa jiki da sauran shirye -shirye makamanta wadannan yin kyakkyawa zato game da juna: ango Ya sani abubuwa da yawa Na iya ballewa mace murfin budurci ta daga cikinsu akwai
1. Jinin haila mai nauyi
2. hawa sama,itace,gini da sauran su.
3. tsalle-tsalle,kamar wasar tsalle-tsalle da sauran su.
4. Yawan hawan keke ko doki
5. Hawa jaki da dai sauran su.
Ya kamata iyaye su dinga hana yara mata irin wadannan matsalolin
don haka haramun ne Ya kawo wani mummunan zargi game DA matarsa har in Ya same ta ba da murfin budurci ba Ana iya samun matsala ma’aurata su sani cewa ba lallai bane su samu nasara a daren farko su domin gajiyar hada-hadar biki da fargabar yin wani muhimmi abu Na Karo Na farko Na iya haifar da kaduwar jiki har tasa ango yaji Ya kasa, don haka ba lallai bane ko dole sai an gabatar da ibadar aure a daren farko, in aka daga shi zuwa wani dare, bayan jiki Ya huta, abin yafi kayatarwa sannan ga sabon angon daya san yayi sabo da zinar hannu, Ya kamata yayi kokarin dainawa a kalla wata uku kafin daren farko, kuma Ya sababbin ma’aurata su sani, haramun ne gare su yin tunane-tunanen alfasha
kallon finan-finan alfasha
*LADUBBAN DAREN FARKO DAGA ZAUREN SIRRIN RIKE MIJI ISLAMIC CHEMIST AND RESEARCH CENTER*
DA farko idan zaka shiga dakin amaryarka, zaka shiga ne da alwala. sannan zaka nemi dan wani abinci mai daraja, misali: kamar kaza ko tsire da sauransu idan kashiga zaka umurceta itama taje tayi alwala sannan kuyi ma Allah godiya abisa cika musu burinku DA yayi kuyi addu’o’in abisa kanku da dukkan al’ummar da suka amsa gayyatar ku suka halarci wajen daurin aurenku daga nan sai ka dafa kanta ko goshinta sannan ka karanta wannan addu’a
” ALLAHUMMA INNEE AS’ALUKA KHAIRAHA WA KHAIRA MA JABALTAHA ALAYYA WA A’UZUBIKA MIN SHARRIHA WA SHARRI MA JABALTAHA ALAIYAYA ( ko kuma ma jubilat alaiha )
( abu dawud Ya ruwaito DA ibnu maajah DA nisa’i )
daga nan kuma sai kuci wannan abinda ka shigo dashi ku dan sha wani abu amma ba’a so mutum yaci abu mai nauyi sosai a irin wannan lokacin daga nan kuma sai ku kusanci juna, tare DA gabatar DA yan’wasanni DA juna kafin kufara gabatar DA ibadar aure kuma akwai addu’o’in DA ake karantawa daidai lokaci jima’i
“Allahumma jannibnash shaitan wajannibish -shaytana ma razaktana”
ANNABI ( S.A.W.W) yace “idan aka kaddara samun ciki a wannan saduwar to shaitan ba zai iya cutar dashi ba har abada ( bukhari DA muslim suka ruwaito ).
[2/7/2020, 10:13 AM] Talali: MATARDA TAFI #MARYAM_SANDA BASIRA. Mata Ku kasance kamarta.
Wata Mata a Yola jahar Adamawa ta dauki wayar mijinta ta shiga Facebook dinsa Se Kawai taci karoda chatting kalaman soyayya da sukai Da wata. Kawai seta zauna tana tunanin hanyar dazatabi wajen daqile alaqarsa da wannan matar. Setai tunani me kyau Kamar haka.
1. Ta copy dukkan Wani chat Wanda sukai Da matar
2. Ta bude sabon Facebook da sunan namiji
3. Ta turawa mijinta friends request, ya karba ba tareda yasan matarsa bace.
4. Bayan yayi accepted request Bayan sun Fara chat sannan ta Boye dukkan Wani abu daxe Iya ganeta. Sannan ta Fara gabatar da Kanta Kamar haka.
Tace “sunana Abu Dardaee Wanda yake member a BOKO HARAM Naga dukkan Wani chat dakai Da matata, sannan inaso namaka Gargadi Daka futa a harkarta Idan kanason cigaba da rayuwa a duniya, Domin cirema dukkan wni kokwanto ga chat din da kai Da ita, seta Tura abubuwan data cofa tace gasu.
5. Idan Baka Dena chat da matataba zamma yanka irin Wanda akewa Rago .
6. Nasanka. Da gaske nasanka sunanka Jamilu mahaifinka Muhammad mahaifiyarka Khadija sannan kanada Yaya 3uku Alamin, Zahra, Yusuf. Abdurrahman shine babban abokinka Usman Kuma maqocinka, kai mlmine lecturer a F.C.E sannan kana futa qarfe 9:30am Na safe tareda Usman sannan kanabin hanyar Jambutu. Ina gargadinka Idan kanason mutuwa Kira ko Kaci gaba da chat da ita Sena yankaka irin yankan Rago.
Matarsa tana can gefe dashi Yana karantawa. Bayan ya gama karantawa Se Kawai ya Fara karkarwa Wani Gumi ya keto mass ya Fara fadin “Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un” matar tasa tace “megida meya faru? Yace ba komai. Nan danan ya goge FECEBOOK WhatsApp Da sauran abubuwanda yake chat, washe gari ya sayarda wayar ya sayomusu abincin Dafawa.
. Kishi Halak ne. Mata pls Amfani da basira Banda kisa
Matso kiji wani sirrin
Kisamo mai zaitun mai hulba kihada wuri daya kinasha safe da yamma cokali daya safe daya yamma
Kuma kina shafawa a gabanki yanakara laushi tsantsi dadi idan me house zaishigar da banana 🍌zaijiwani dandano mai dadi banana 🍌 zaina shiga ahankali lokacin saiyamanta idan yake yana cikoda naman gaba sosai
Yanada amfani ajikinmu mu maya
INA FAMA DA CIWON KODA, ZAN IYA CIYARWA A MAIMAKON AZUMI ?*
*Tambaya*
Asalamu Alaikum malamai na inada tambaya macece bata da lafiya na ciwon koda yafara zama kuronik sai satinnan likitoci suka bata shawara duk bayan minti Talatin taci wani Abu daga Abinci kartakoshi to malam yaya za’a billowa maganar Azumi ciyarwa za’a cigaba da yi ko jira za’a yi sai ta warke ta rama ?
*Amsa*
Wa alaikum assalam, in har tana tunanin samun sauki kafin wani azumin ya zo, ba za ta ciyar ba, za ta bari ta rama bayan ta samu dama, saboda aya ta: 184 a suratul Bakara ta nuna cewa : wajibin mara lafiya shi ne rama azumin da bai yi ba na Ramadhana bayan ya samu dama a wasu kwanakin.
Mutukar likitoci sun tabbatar ba za ta samu saukin da za ta rama azumi daga baya ba, ya halatta ta ciyar a maimakon kowacce rana.
Allah ne mafi sani.
KUSKUREN DA MATA SUKE AFKAWA YAYIN ‘DAUKEWAR JININ HAILA*
______________________
Mafi yawan mata idan jinin al’ada ya ‘Dauke musu suna jinkirta wanka da niyar ko jinin zai Qara dawowa.
Wasu sukan Qara kwana ‘Daya zuwa biyu bayan haila ya ‘Dauke.
Wasu kuma idan suka ga alama guda ‘Daya na ‘Daukewar jinin, sai suce zasu jinkirta wanka domin su jira zuwan sauran alamomin. Misali: Mace taaga bushewar gaba amma bata ga Farin ruwa ba, wanda ake kiransa da larabci (قصة البيضاء), daga nan sai tace bari ta bari sai farin ruwa yazo sannan tayi wanka ta cigaba da sallah da azumi.
Duka Wannan kuskure ne babba ❌❌
Abinda yake wajibi shine: Da zarar taga jini ya tsaya ko taga alamomin Daukewar Jinin haila, toh wajibi ne tayi wanka nan take ta cigaba da ibadar ta. Qin yin wanka har lokacin sallah ya wuce babban zunubi ne.
Allaah ya tanadi Azaba mai tsanani ga masu wasa da sallah.
Allaah yace:-
” ﻓَﻮَﻳْﻞٌ ﻟِﻠْﻤُﺼَﻠِّﻴﻦَ (4 ) ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻫُﻢْ ﻋَﻦْ ﺻَﻠَﺎﺗِﻬِﻢْ ﺳَﺎﻫُﻮﻥَ “
{ﺍﻟﻤﺎﻋﻮﻥ : 5-4 }
Allaah ya qara da cewa:-
” ﻓَﺨَﻠَﻒَ ﻣِﻦْ ﺑَﻌْﺪِﻫِﻢْ ﺧَﻠْﻒٌ ﺃَﺿَﺎﻋُﻮﺍ ﺍﻟﺼَّﻠَﺎﺓَ ﻭَﺍﺗَّﺒَﻌُﻮﺍ ﺍﻟﺸَّﻬَﻮَﺍﺕِ ﻓَﺴَﻮْﻑَ ﻳَﻠْﻘَﻮْﻥَ ﻏَﻴًّﺎ “
{ﻣﺮﻳﻢ : 59 }
…… Da ayoyi masu yawa cikin al-Qur’ani.
daga lokacin da jini ya ‘Dauke, ibada ya wajaba ga mace.
idan mace ta jinkirta sallah toh sai ta rama su bayan tayi wanka, sannan tayi istigfarin jinkirin sallah
*_Idan kin karanta kiyi Qoqarin turawa yar uwarki musulma zaki samu lada in shaa Allaah._*
Ya kai dan uwa mai Albarka ka taya mu yada wannan karatu/sako zaka samu lada mai yawa, domin yada ilimi yana da daga cikin Abubuwan da suke kusan ta bawa ga Mahalicci
BU CUTAR DA BABU MAGANINTA ACIKIN ALQUR’ANI
Ibnul Qayyim Allah ya masa rahama yana cewa “Alqur’ani shine cikakken magani ga kowane irin cuta, na zuciya ne ko kuma na gangan jiki ne, cuta ta duniya ko ta lahira, babu wani da zai nemi waraka dashi face ya dace batare da jinkiri ba.
Idan mara lafiya ya kyautata magani da Alqur’ani, ya rikeshi da gaskiya da imani, ya karbeshi hannu biyu, da quduri nagartacce, sannan ya cika sharrudansa, to wallah babu wani magani kamarsa har abada, tayama za’a samu kamarsa bayan shine maganar Ubangijin sammai da kassai, maganan da idan an saukar dashi akan duwatsu zai narkashi, idan kuma akan kasa aka sauke zai rabata gida biyu, babu wata cuta cikin cututtukan dake damun zuciya da ganganjiki face acikin Alqur’ani akwai hanyar da za’abi wajen maganceta da hanyar rigakafi daga kamuwa da ita, amma kadai Wanda zai gano hakan shine wanda Allah ya azurta da fahimtar littafinsa”.
الطب النبوي ١/٢٦٦
GAMSARDA MIJI
Gamsar da namiji a jima’ince yafi sauki wajen gamsar da mace, duk kuwa da cewa dukkannin halittan da aka yiwa mace a jima’ince suma maza suna da irinsa. Kamar yadda ake samun harijin namiji haka nan ma ake samu harijan mace, yadda ake samu mazan da suke jimawa babu gajiya a lokacin jima’i hakama matan. Ana samun maza da mata ragwaye a wajen
jima’i da kuma wadanda sam jima’in ma bata damesu ba a dukkannin
jinsunan biyu.
Da akwai wasu mazan da basu cika son doguwar wasannin motsa sha’awa ba, wasu kuwa suna bukatan lokaci maitsawo ana masu wasa duk kuwa da
macen tafi namiji bukatar wasan motsa sha’awa mai tsawo.
Abu na farko daya kamata mace ta fahimta a tattare da mijinta shine
abunda yafi bukata a yayi wasannin motsa sha’awa da kuma lokacin kwanciya irin na jima’i, domin da akwai inda da zaran mace ta tabawa
mijinta maimakon ta motsa mishi sha’awarsa sai kawai sha’awar tashi ya gushe. Haka ma a kwanciyar jima’i, yana da kyau ki fahimci irin yanayin kwanciyar da mijinki yake so. Shi yasa malamai na jima’i suke cewa sadarwa a jima’i yanada matukar alfanu ga ma’aurata domin ta hanyar ce zasu iya fihimtar abubuwan da suke bukata a yi musu kamin, lokaci da kuma bayan jima’i.
Da akwai mazan da zaran mace ta fara wasa dasu nan da nan suke gamsuwa ba tareda sun shegetaba, da akwai wadanda da zaran azzakarinsu ya shiga shikenen kuma sun yi zuwan kai kenan. A akwai mazan da sukan
dauki lokacin mai tsawo suna jima’i da mace kamin suyi zuwan kai, wasu mazan kuwa a lokacin da suke kawowa a lokacin ne gabansu ke kara yin karfi har sai sun kawo sama da biyu koma biyar kamin suke gamsuwa da mace. Ke naki mijin yaya yake, domin dole sai kin fahimci yadda yake
kamin ki iya gamsar dashi.
Sai dai maza masu wuyan sha’ani a jerin mazan da na ambata sune masu saurin zuwan kai da kuma masu daukan lokaci mai tsawo suna gurza mace basu gamsu ba, sai dai kuma da zaran mace ta samun illimin sarrafa irin wadannan maza ta gama dasu. Maza masu saurin zuwan kai sune mazan da sukafi cutar da matansu, domin wata matan sai ta gurzu
take gamsuwa, don haka matsalar irrin wannan mazan yana tattare ne da
kodai suna da cuta da suke bukatar ganin likita, ko kuma sabbin shiga ne wato mazan da suka yi aure sabo-sabo ko suka jima basu yi jima’i ba
hakan na faruwa da su.