ZURFIN CIKI COMPLETE HAUSA NOVELS

 

Home / ZURFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 1 part 1

ZURFIN CIKI book 1 part 1

Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 02:16

UUmmi tana tafe tana yan wakokinta, tareda gudu

hade da tsalle. cinikin ummi ne gudu, sam bata

tafiya a hankali.daga can gefe ta hango wata

yarinya wadda bazata wuce sa’arta ba.

tace,”yauwa,ga firdausin data tsokane ni” ta nufi

wurinta ,tasha gabanta ta rike kugu. “fiddausi wa

kike tsokana? fiddausi tace “ban tsokane ki ba

fa”.cikin tsoro tayi maganar .ummi ta shako mata

wuya. ina jin lokacin da kika ce ummi tsiga.ban

ce ba inji fiddausi .ummi ta hankada ta tare da

cewa “Allah yaso ki.” nikan garin da fiddausin tayi

ya tarwatse a kasa tace “kin gani ko? wallahi sai

kin biyani”ta soma kuka,ummi ta sheka da

gudu,sai gida. tana ajiye man gyadan data siyo ta

nufi ba daki don fitsari ya matse ta .umma dake

zaune tana fadin. “da mutum!da mutum!!” saida

ummi ta bude . Ganin yaya Abba tayi,da gudu ta

juyo ta fada dakin umma,jiki na bari bayan tayi

bol da dakakken yajin da umma ta daka zata

soya mai don cin abincin rana. sai kuma ta tuna

cewa bata tsira ba,don Abba tsaf zai binciko ta.ta

fito da gudu ta nufi dakin tsohuwa. tsohuwar tana

sallar azahar.ummi ta tsallake ta ta kutsa kasan

gado.nan ma tayi ciki da furar da tsohuwar keson

sha da zarar ta idar da sallah. Alhaji babba tasa

ya aiko mata da furar daga kasuwa.don tasha da

rana. Abba ya fito wanka ranshi a bace.dakin

umma ya nufa yana fadin “ummi ke ummi zonan”

Ya samu Umma tana tattara yajin da Ummi ta

zubar, tana fada. Ya ce, “Umma ban san irin

dukan da zan wa Ummi ba yau. Ta ce,”Abba ka

mata dukan mutuwa, na gaji da halin Ummi.

Yarinya sai ka ce ‘yar fata? Ka dubata ta tafi

dakin Tsohuwa, don ta san zata hana a dake ta.”

Ya ce,”Allah sai dai Tsohuwa ta yi ta fadanta,

amma ba zan barta ba. Ya juya zai tafi, suka ji

muryar Tsohuwa tana fadin. Ba zan yi fada ba, ka

kashe ta ka ji mai sunan Malam, ba na son ka

barta da rai. Ta dubi Umma” ke kuma Suwaiba

dama kin san ba za ki daraja sunana ba ki ka sa

a ka sa miki don kiji dadin ci min fuska?” Umma

ta ce,” Ba haka ba ne Tsohuwa, Ummi ba ta yo

halinki ba. Ita fa rashin hankali ne da ita. Yayanta

fa ke wanka ta zo ta leka shi, nan kuma tazo ta

zubar min da barkono. Abba ya ce, “Umma don

Allah kiyi shiru ki kyale Tsohuwar nan, ai ita ta

6ata Ummin, duk abn da yarinyar nan tayi sai ta

hana a yi mata fada. Uhm duk fadanki yau sai na

dake ta, ba sunan ki ba in ma kece,”Tsohuwa

tasa kuka gami da salati. “Yanzu mai sunan

Malam ni ka ke fadawa haka?” ya ce, “An fada

miki.” Umma ta ce, “kai Abba zan sa6a maka

jeka.” Ta juyo wurin Tsohuwa, Don Allah kiyi

hakuri…………… Maman Fiddausi ce tayi sallama

tare da Fiddausin suka shigo. Ran Maman

Fiddausin a 6ace, ta tsaya rike da gari a

hannunta ta dubi Umma. Ta ce, Umman Abba

dubi abn da Umminki tayi min don Allah, yarinyar

nan tayo nika da kyar,” tun safe sai yanzu na

samu, amma ta zubar min.” Abba ya ce, Kinga

halinta ko?” Tsohuwa ta ce, “Wannan ba matar

Bala ba ce?” Maman Fiddausi ta ce, “Ni ce.” Ta

ce,” To kije kije ki nemi wanda ya zubar da

garinki, Ummi ko fita ba tayi ba. Umma ta ce, “

Ta fita Tsohuwa, na aike ta siyan mai.” Tsohuwa

ta ce,” Tsokanarta a ka yi to. Umma ta amshe

abin garin ta zuba musu, sannan ta ce, “Don

Allah Tine kiyi hkr.” Abba ya nufi daki. Sai da ya

shirya tsaf, sannan ya dauki belt ya nufi cikin

gida, dakin Tsohuwa ya shiga kai-tsaye kasan

gado ya nufa. Ya jawo ta, ta soma kurma ihu.

Daya ya lafta mata amma ta dane shi tare da

cukwikuye belt din tana ihu. Tsohuwa ta iso tana

dukanshi a baya, fadi take “Za ka kasheta ne?

Jama”a kuyo dauki. Haushin hakan yasa shi

damko kanta ya shiga zuba mata kola, ya

sirmiyota ya shiga lafta da takalminshi, tunda ta

hana belt din. Sai da ya mata tas, sannan ya fita

ya bar su, Tsohuwa na kuka Ummi na kuka. , Sai

da komai ya natsa ta leka ta jawo furarta don

tasha, sai ta ganta a zube. Ta ce, A” a ke ki ka

zubar min da fura?” Ummi ta ce, To ba shi ne

janyo ni ba Yaa Abban. Tsohuwa ta ce, “Ai ko sai

ya siyo min furata. Ta mike ta wuce Umma tana

rabon abinci, ta nufi soro in da dakin Abba yake

(Zaure) Ya fito yana rufe kofa, ta ce “Au za ka

fita ba? To ka sawo min furata da ka zubar. Ko

kallonta bai yi ba ya rufe kofarshi ya wuce. Ta ce

mishi “Aikin bana, in ba siyo min ba ubanka ai ya

dawo ko min dare ya sito min. Abba ya ce, Ku ku

ka sani. Ra ce, kaima ka sani, dan jakar uba. Ta

dawo ciki tana mitar ya cika bakin rai. Umma ta

ce, “Ina Abban? Tsohuwa ta ce, “Ya tafi, in bai

sai min furata ba ranshi zai 6aci yau a gidannan.

Umma ta ce “Ni bai ma ci abinci ba ya fita, ke

Ummi zo ki kira min shi, yunwa fa yake ji.

Tsohuwa ta ce, “Ba za ta kira shi ba, ya dake ta

sannan ta kira shi? Tunda bai barta taci da dadin

rai ba, shi ma ba ya ci ba.,, Umma tayi shiry,sai

haushin Ummi da take ji kamar ta shake ta ta

mutu. Ummi tayi wanka ta zura kayan Mkrnt,

tana saka sandal Umma ta ce, “Ina Ummi? Zo

nan.” Ummi ta tafi tana cewa a ranta. “ALLAH

YASA DAKIN YAYA ABBA ZA TA AIKE NI, SAI NA

RAMA DUKAN DA YA YI MIN JIYA, DON YANZUN

DUK ME YA MIN SAI NA RAMA……….” Umma ta

katse mata tunani da cewa,”dauki shayin Abba ki

kai masa kada yayi latti,kai shayin ki dawo ki

dauki dankalin,yau shi kadai ma nayiwa dankalin.”

Tace,”nifa?”umma tace “ke kina cin dumame

Abba ko ba ya ci,dan haka dan wanda ya rage

shi nayi wa.” Ummi ta figi kayan tea din ta nufi

dakin Abba tana tura baki.tare da sallama bata

jira amsa ba,ta daga labule ta fada. Dabi’ar da

yake mata fada akai kullum,ya gama saka

singiletinshi kenan yana kokarin saka riga. Yace,

“wai ke wace irin majanuniya ce?ban ce miki in

kinyi sallama sallama sai na amsa za ki shigo

ba? sai kawai ta saki tiren,ruwan zafin ya zube

masa a kafa,dankalin ya watse kan rigar da zai

saka. tayo waje da gudu,sai dakin tsohuwa.ya

fito da sauri yana cewa,”umma ta kona ni! ta

kona ni!!” da sauri umma ta fito daga dakin Alhaji

babba,shima Alhajin na biye da ita yana fadin

“wacece ta kona ka?” Yace “ummi ce! ummi

ce!!.”nan take Alhaji babba ya rike kafar yana tofa

mishi addu’a. Umma ta debo kullun kamu ta zuba

mishi,amma duk da haka sai da yan yatsun

kafarsa suka kumbura. tsohuwa ta fito daga daki

tana fadin,”kai ummi bata ji? wai ni meyasa aka

sa mata sunana?” Abba ya kalli tsohuwa cikin

takaici yace,”duk ba ke kike daure mata gindi ba?”

Umma ta shiga dakin tsohuwa ta janye kayan da

tsohuwa ta jera don kada aga ummi,ta janyota

tun daga dakin take kwallo da ummi har waje.

Alhaji ma yau har dashi aka zane ummi,tsohuwa

dai sai yan mitoci take yi,wai yanxu haka ma

bata sani bane. Abba dai ranar dai bai je

makaranta ba,haka nan da yamma sai da ya saka

ummi a dakinshi ya bata gwale-gwale sannan ya

zane ta. misalin hudu da rabi na yamma,Ahmad

abokin Abba yayi sallama a kofar gidan,Abba ya

amsa ya fito. Suna zaune kan dakalin kofar gidan

suna hira,sai ga ummi ta yanko da gudu tana

waiwayen baya. Ya ce,”zo nan.”tazo yace,”kinyo

tsokanar fada ko?” tace,”a’a.yace in har tsokana

ki kayo zaki sani shegiya mummuna kazama. Ta

murguda baki,yasa takalmi ya jefeta,ta shige gida

sai ko ga wani yaro jiki duk kwata yayyanshi na

biye dashi. ya tambayesu,suka ce “ummi ce ta

jefa shi kwata”ya taso yaron har cikin gida ya

kamota dakin tsohuwa ya tsareta ta wanke ma

yaron jiki,ta kuma wanke kayan. sannan ya

zuzzuba mata kola a kai.tsohuwa tana ta yiwa

yaran fada,wai ita ma su daina tsokanarta Umma

ko lekowa bata yi ba,ya fito ya samu Ahmad yana

cewa “kayi hakuri na barka kai kadai.” Ahmad

yace,”ba komai” sai Abba ya zauna sannan

Ahmad ya dube shi. Abba wannan kanwar taka

kuwa bata da Aljanu? Abba yace,”ba kowa

akanta,sai iskanci.” Ahmad yace.”a’a,kai dai ku

kaita ayi mata rukiyya.” Abba yayi dariya,sannan

yace kasan Allah ba kowa akan ummi,saboda

Alhaji karami ya taba yin wannan tunanin. ya

dauke ta yakai ta rukiya bata da komai.”Ahmad

yace tabdi!,gaskiya in ta isa aure duk wanda ya

aureta akwai aiki babba a tare dashi. Abba ya

ce,”wane mahaukaci ne ma zaya dibar ma kansa

ummi?”Ahmad ya ce,”sai ai muku hadin ggida…”

ya kaima Ahmad naushi a gefen ciki,Ahmad ya

kauce yana masa dariya. Abba ya ce,”ka cuce

ni,ace in auri ummi ai sai na hada kayana na bar

garin nan. nan. Ahmad ya s heke da dariya har

da rike ciki.sannan ya ce,”don me? Abba ya

ce,”to wannan yarinyar ba sai ta hada maka

gobara gida ba?gata kazama ga muni.” Ahmad ya

ce,”kama dai kuke yi.” Abba ya bata rai,”Ahmad

bana so.in har da gaske ina kamada ummi ba sai

na koma ciki an sake haifana ba. Don Allah ni

tashi ma ka tafi,don wallahi da don kai bane kake

fada min haka da sai munyi rigima,na tsani

ummi,bana sonta sam! Zaune suke a kofar gidan

Alhaji babba kan katuwar tabarma,sun jere abinci

suna ci. kullum Alhaji babba da Alhaji karami nan

suke zama tamkar tagwaye,suna matukar kama.

mafi yawancin lokuta ma kaya iri daya suke

sakawa,domin Alhaji babba duk kayan daya saya

tare yake sai musu. haka nan hula ko

takalmi,haka nan matansu baya

bambantawa.shima Alhaji karami duk da bai kai

samun babba ba yana koyi dashi. Alhaji babba ya

kalli karami yace,”Aminu ya zancen makarantar

bashir?” Alhaji karami ya dubi wansa ya ce,”Alhaji

bashi fa ya fadi jarabawa,jiya na tsare shi da

maganar sakamakon jarabawarshi yace bai duba

ba,saida yaji nace zan hada shi da Abba suje

sannan yace min yaje wai duk ya fadi. Alhaji

babba yace,”Ash sha! sai ya maimata shekara

kenan?”Alhaji karami ya ce,”to in ma ba zai

maimaita ba Alhaji shi ya sani,ba sahura ta bata

su ba? shi Abba ai ba haka yayi ba,ka dubi fa

yadda yaki aikin kanikancin nan,uwarshi ta zuga

shi wai yayi karatu kadai yayi aikin gwamnati.

kullum haka sahura take kitsa ma yaran.”Alhaji

babba yayi yar dariyar takaici,sannan yace”in

banda abin sahura yadda kasan nan tamu ta

zama waye zaici alwashin aikin gwamnati? ina ce

masu digree ne ke yawo ba aiki?” “har masu

masters.” inji Alhaji karami.ya tashi zaune daga

kishingidar da yayi,yace dubi misalin dan

abokinnan naka Alhaji buhari.” Alhaji babba ya

ce,”kwarai kuwa,mas’ud ba.yanxu ma fa kasuwa

yake zuwa,sai yanxun yake koyon kasuwancin.”

Alhaji karami ya ce,”to daya dora shi a kasuwar

fa tun farko?shi yasa na fada ma sahura ta bar

yara su hada da sana’ar hannu. Donni dai yaro

kamar bashir yanxun ba zan dauki kudina in ba

shi ba.”Alhaji babba yace,”shi yasa kulum nake

kara son Abba,yaron nan da kanshi yace min in

kai shi shagon dinki. Har naki suwaiba ta

ce,”Alhaji ka kai shi in ya iya sana’ar hannu ko

bai samu aikin gwamnati ba zai rike kanshi da

sana’ar nan.” Alhaji karami ya ce,”to ai kasan ita

suwaiba tasan abinda take yi.amma sahura sai

addu’a.” Sallamar Abba ce ta katse su,ya zauna

can gefe sannan ya gaishe su,duk suka amsa tare

da tara hankulasu gurinshi. Ya mika ma Alhaji

babba kullin takarda tare da cewa “Alhaji gashi

maganin (ulser)ne” Alhaji babba ya amsa ya

ce,”Abba sarkin amsa magani, a gurin wa ka

samo wannan kuma?” ya ce,”Ahmad abokina na

raka ya amso ma babanshi,shine nace bari in

amso muku” yace to Allah ya saka da

alkairi.”Alhajikarami yace”dame ake sha?” Abba

ya ce,”da madara peak.” suka ce”to” daya mike

zai shiga gida Alhaji babba yace ya shige da

kwanikan abincin. yau kam Abba bacci yake ji da

wuri,don haka ya baro shagon dinkinsu wanda ya

kan kai goman dare a ciki ya nufo gida. Ya bude

dakinshi ya shiga ya cire riga sai singileti da

gajeren wando na jeans.ya nufi ciki don ya kama

ruwa ya kuma yi wa ummanshi sallama. tsakar

gida ya sameta zaune ta zabga tagumi,inda

abinda Abba ya tsana shine,yaga ummanshi cikin

damuwa. da sauri ya isa wurinta,”umma

lafiya?”ta dube shi “ina fa lafiya,ummi ce tunda

tayi sallar isha’i ta fice kusan awa guda zance

jiya ka mata dukan fita wasan dare?” Abba yace

“to wai me za’a yi wa ummi ne ta zama irin

sauran yara?” umma tace,”addu’a ce Abba,kuma

muna yi kullum.” ya juya cikin bacin rai,layin su

Amina kawarta ya nufa,don bata wuce can.duk da

cewa Amina bata kaita rashin ji ba. can din kuwa

ya sameta,ta tara zugan yayan layi sai tsokanar

fada suke yi,ita ce shugaba. wata falwaya Abba

ya samu ya jingina yana kallonsu,don yana iya

tunkararta su diba da gudu. shi kam ba za ya iya

guje-gujen nan ba,duk wanda yazo wucewa sai

sun tsokane shi,wani su jefe shi,wani kasa zasu

watsa masa su gudu wani kuma rigarsa zasu ja.

c can wani shida budurwarsa sun zo wucewa ta

fizge ledar hannunsu ta watsar,sannan suka ruga

da gudu. tayo gurin da Abba ke tsaye bata zaci

da mutum a gurin ba,sai dai taji anyi caraf da

ita.sai da Abba ya zabga mata koso a tsakiyar

kai har tayi fitsarin wuya,sannan ya tasata har

gurin mutumin data yaga ma ledar. suna

tsugunne suna tsintar lemunsu da ayaba ya

ce,”malam ga wadda ta yaga muku leda.” da

zafin nama mutumin ya mike,Abba ya

ce,”gata”mutumin ya shakota yace yau sai naga

ubanki.” Abba ya ce,”ko kara ka kai gidansu nine

zan hukuntata,don haka gata na kawo maka

kanwata ce kuma naga lokacin data tsokaneka.”

jikin mutumin yayi sanyi ya ce,”na gode bawan

Allah,taje taci albarkacinka.” Abba yace “daka

nade ta.” mutumin yace,”ba komai,ke kuma ki

canza hali ke mace ce.” Abba yace nagode”

sannan ya tasa ta zuwa gida. Bokiti ya cika da

ruwa ya dora mata,,umma rasa bakin magana

tayi daya sanar da ita tsokanar daya tarar da

ummi suna yi. Daga karshe ta ce,”Allah ya

shiryaki,abind ya sameki kada ya sami sauran

dangi. Alhaji kuwa daya sameta dauke da bokitin

tana kuka tana fadin “yaya Abba na tuba,bazan

sake ba.” ya ce,”uwata bakya ji ne fatan Allah

yashirye ki.”ya nufi dakinshi.tsohuwa takaicin

Abba ne ya hanata fitowa tayi magana. nata

ganin,ummi bata wuce fita tayi wasa da

kawayenta ba,a cewarta ba laifi ba ne. amma an

bi an tsangwami yarinya,an hanata walawa.sai da

Abba ya gaji dan kanshi sannan ya sauke mata

ruwan. Sannan ya mammaka mata

takalmi,sannan ta shige dakin

tsohuwa.tsohuwana daga kwance ta dubeta.

“yaga dama ya kyaleki?kai mai sunan malam

akwai mugunta.zo ki kwanta.” cikin kuka ummi

tace,”kayana sun jike,bokitin ruwa fa ya dora

min.”tsohuwa tace,”barshi da halinsa,ace mutum

ba zai sake ba?” ummi tace,”ai sai na rama,shima

din sai yayi kuka.”tsohuwa ta ce,”a’a,kada ki

soma zancen ramakon nan.kin san ko kin rama

ke ce zaki kwan ciki.” ummi ta ce,nifa sai na

rama.”tsohuwa ta ce,”baki gaji da shan wahala

ba kema da shegiyar gaddama,ga zanina nan

kikin raki ciro ki daura kizo ki kwanta.” ummi tayi

lamo bayan tsohuwa tana tunanin dame zata

rama abinda Abba yayi mata jiya.har bacci yayi

gaba da ita waiwaye…………. SULAIMAN shine

asalin sunan Alhaji babba,Aminu kuma shine

Alhaji karami. tsohuwa itace mahaifiyar su,kuma

su kadai ne yayan data haifa.Asalinsu yan

zamfara ne a kauyen daji a karamar hukumar

kauran-namoda. malam Idris mahaifinsu shine ke

zuwa yawon fatauci,har Allah ya zaunar dashi a

garin kano,da matarshi Habiba. sunzo da

yayansu guda biyu,sulaiman da Aminu.sun yi

karatun muhammadiyya mai zurfi,amma basuyi

karatun boko ba. sannan ya dora sukan harkar

kasuwanci,Allahya albarkaci kasuwancin Sulaiman

inda harkoki suka bude mishi cikin kankanin

lokaci. matsalar shi daya rashin boko,malam

idrisu mahaifinsu yana daya daga cikin wadanda

basu amshi boko ba lokacin da tazo. Don haka

sam bai saka yayansa ba.Sulaiman ya auri

Suwaiba wadda suka dauki watanni suna

soyayya,ita yar unguwar sheka makaranta ce.

Amma asalinsu yan Daura ne jihar Katsina.kafin

aurensu sai da yayi gini a unguwa uku gidaje

guda biyu iri daya. Ya ce Aminu kaninsa ya zabi

gida duk da cewa a lokacin baiyi auren

ba,wannan abu yayi wa mahaifisu dadi. yayi ta

shiwa Sulaiman albarka,don haka sai aka rufe na

Aminu,yayin da sulaiman ya tare a nasa da

matarsa Suwaiba. / ZURFIN CIKI book 1 part 2

ZURFIN CIKI book 1 part 2

Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 21:40

Kwanci tashi 5yrs ta miqa suwaiba bata taba ko

batan wata ba. awannan yr ne mahaifinsu ya

cimma 1yr da rasuwa. saida aka watse makoki

danginsu na qauran-namoda suka koma. sannan

sulaiman yace da aminu, to ni xan dauki tsohuwa

in maida ta gidana,kai kuma aminu ka fito da

mata kayi aurenka dan mu xauna kusa da juna.

tsohuwa ta saka kuka tace wannan yaran nidai

da ka barni na xauna da gidan xai xama kufai.

sulaiman yace tsohuwa kiyi haquri, sai a saka

haya.aminu yace haka xa ayi. daqar tsohuwa ta

yarda dan tace ita wannan gidan mutuwane xata

rabata dashi, dan gidane me tsohon tarihi a

gurinta. ta ce gidan da mijinta ya rasu gidan da

ya kawo ta tun tanada jajayen sawunta. suka dai

lallabata. lkcn da aminu ya gabatar da sahura a

matsayin matan da xai aura, tsohuwa ta tuma ta

ce ba ta laminta ba, don kuwa kowa yasan

mahaifiyar sahura gun masifa. sanna sahurace ta

gajeta. aminu sai ya watsar da mgnn auran

gabaki daya har tsawan lkc. sulaiman yanata

roqan tsohuwa ta amince, dan ya lura aminu yayi

nisa. Ba yadda tsohuwa ta iya, dole ta amince,

aka sha biki ta tare gidan aminu. mai hali dai

baya fasawa, dan sahura batasan hulda da

suwaiba da surukarta, gashi daga kawota ko

2mth bata yiba ta kama fada da yan unguwa. a

cikin 3yrs sahura aka samu ciki. lkcn sulaiman ya

samu xiyarta qasa mai tsarki shida tsohuwa dan

sauke farali. sunyi addu’a allah ya bashi xuri’a

shida aminu.suna durowa gida suka samu lbrn

cikin sahura, murna a gun sulaiman tamkar

matanshi ne keda cikin.lkcn haihuwa tahaifi da

namiji murna gun yan uwa biyu ba’a magana,

anyi shagalin suna inda yaro yaci sunnan mahai

finsu wato idris shine suke kiranshi abba. Sannan

Ahaji Sulaiman ya biyama qaninshi kugeran

makka daga nan ne aka samu ahj Babba da ahj

qarami tun abba yana jariri ahj babba da

matanshi suke dawainiya dashi Sahura ba taso

saidai ba yan da xaitai da ita. domin alj qarami

na gama shirin fita xai saba shi sai gidan sai yayi

kukan nono ake maida shi, saidai tayi ta mitar

cewa anriqe mata yaro gidan,sahura dai in an

kawoshi bata isa taxoba dan tasan tsohuwa

tafita danja.duk da gugar xana da haibaici da

sahura take antayo ma suwaiba ta katanga ko

inta je gidan, baisa ta daina dawainiya da abba

ba. cikin hakane sahura wata ran sahura ta tashi

da xaxxabi mai tsanani da amai, shine taje asibiti

ganin likita ya tabbatar mata da tana dauke da

ciki.ko da ta fadama alj qarami ba qaramin murra

yayi ba ita kuma ta batarai, yace tunda abba

yana tafiyan shi ko ina ayaye shi. Da yamma

bayan yadawo kasuwa ya shiga gaida tsohuwa

shine yake gayamata xa’a yaye abba. tace

saboda me? ku barshi yayi 2yrs. sai yace ai uwan

tanada juna biyune, shi yasa, daman sha waran

da nakesan fada maki shine xanba yaya shi

kyauta har abada.tsohuwa tace kai amma ka

kyauta. Washegari da safe shine ma yayi ma

abba wanka tana kwance ya shirya shi, sannan

yace mata ta hada kayanshi duka dan xan kaishi

gidan ahj babba gaba daya. tace kana nufin kayi

kyauta dashi gaba daya? yace ea. tace tabdi!,ba

xai yiwu ba. infishari banxane kaxa tayi mana. su

wa yace kada su dage su samu nasu dan? nima

wahala nasha na haifi dan, ba shago na bude ya

fito ba….sam bai kulata ba, ya hada kayan yaran

ya fita. ya shiga gidan ahj babba da shi. dakin

tsohuwa ya shiga, nan ya samu ahj babba suna

gaisawa, yace yauwa, dama gurinka naxo yaya.

abba ya sauka daga jikin babansa yaje jikin ahj

babba da gudu, ahj ya dauke shi ya rungume. Ahj

qarami ya keqa ya kira suwaiba,ta shigo ta xauna

sai ahj qarami ya soma jawabi da cewa. tsohuwa

ina san ki xama sheda, yaran nan na ba yaya da

suwaiba har abada.ahj babba yasake rungume

yaran a jikinshi wani saban son shi ya ratsa shi.

idanshi suka kawo qwalla, suwaiba ta sa kuka

tace mun gode da wanna abu da ka yi mana.

Allah ya bamu ikon riqeshi da amana. ahj babba

yace bani da bakin da xan maka godiya, saidai

ince allah ya qara xumunci. ahj qarami yace haba

yaya dana nakane, saidai inasan abba ya xama

xaka kai daya. tsohuwa tace allah ya maku

albarka daku da yayanku, kaima allah ya baka

haihuwa. sukace amin. Sahura kuwa mijinta na

fita da yaro, itama ta xari hijabi ta nufi gidan

iyayanta, ta shaida ma mamanta cewan aminu

yayi kyauta da danta, kuma yaba mutanan da

basa qaunan ta. nan da nan uwar tahau masifar

cewan ba xai yuyu ba, ai dole ya baki danki.

shiko uban cewa yayi ai ikon sane, dan haka

baiga laifinsa ba dan yaba dan uwansa dansa.

sannan yace ,ta tashi ta koma. uwar tace ba xata

koma ba, ya ce ta xauna. bai sake bi ta kansu ba,

ya ci gaba da harkokinsa. shiko ahj qarami cewa

yayi baxai bita ba, lokacin da ya dawo ya samu

batanan, sannan bai fadama dan uwansa ba har

aka kwana. sukuma su suwaiba basu fahinci

sahura batanan ba dan ba hurda suke ba, saida

kukaxo cin abinki ahj qarami bai futo da kwanu

ba. sannan wan yace iyalin naka bata nanne?

yace yaji tayi, niko baxan bita ba. ahj babba yace

akan wani dalili ne? ahj qarami yace ban sani ba,

na dawo gida ban ganta ba. da safe ahj babba ya

tashi gaba sukaje gidan, sahura ba kunya tace

danta takesan ya dawo mata dashi, inhar yana

san xama da ita. Ahj babba yace, indai danta ne

xai maido shi. ahj qarami yace shi kuma inhar sai

an dawo da dan to ya haqura da auranta. kuma

na cikin ta ma inta haife shi xaixo ya ansa ya

qarama wansa inya so yaga yadda xatayi. duk

juyin da akayi yaqi yarda daga qarshe ma tafiyan

shi yayi. ubanta yace da ahj babba kaima jeka

yadda suka so haka xasu yi. satinta guda taka

abincin kirki gagaranta yake yi, ita kuma uwan ta

daina samun wani abu daga gun sahurar ke kawo

mata. dan haka suka yanke shawaran ta koma,

duk da haka saida ya shareta na kwana uku

sannan ya sakar mata. haka ta haqura saidai

tasha alwashin dun runtsi sai danta ya dawo

hannunta. sannan ta kulla sabuwan gaba da ahj

babba da suwaiba kuma tace duk tsohuwa ce

takitsa abin. abba yana samun kulawa tare da

tarbiya mai kyau.sahura ta haihu ta sake samun

da namiji aka samasa bashir, daga nan haihuwa

akai akai.. Tun abba yana qarami ya koyi wasu

halaiya na ahj babba. da farko, sallar

asuba,axahar, laasar, magrib da isha. ahj babba

kan tasa abba suje masallaci da rana kuma

umman sane ke turashi. ranan jumaa ahj na

dawowa gida dan ya tafi dashi. dan haka sallah

ta xauna ma abba da xaran lkc yayi xai fara shiri

yi. sannan ya iya sadaka dan dasunje yana bashi

kudi ya rabama almajirai ko yasa a asusun

masallaci. sai xumunci aduk lkcn da ahj babba

xashi xanfara yana tafiya da shi. ya tashi da san

iyayan shi matuqa bai taba sanin basu suka haife

shi ba. duk da cewan duk lkc da ya shiga gidansu

umman bashi takan cemai bafa umman kace ta

haifeka ba, nice na haifeka. riqonka muka basu. in

yaji haka sai yace allah kiyaye. sai ya baro gidan

ita kuma taita xakinsa. inya fadama umman shi

saitai murmushi ta rungume shi. ya ce aidai kece

ummata ko? ita kuma tace nice ummanka rabuda

ita kaji. abba yanada tausayi dan haka ya

taimaka ma ummanshi aikin gida. shekara sha

biyu ya sauke kur’ani.a lkcn ne ya gama pry ya

samu xuwa js1 Abba makarantan masu kudi ya

ke yi.ita kuma sahura duk yaranta ta batasu,

musamman bashir. duk lkcn da akace yaje

makaranta inyace ya gaji, saitace ya xauna kaje

gobe. ko ahj babba ya korashi sai dai ya labe

inya tafi shi kuma ya dawo. yafi san xuwa qwallo

ko shagon game. to hakama qannansa duk sun

dau irin tarbiyyan uwarsu. cikin haka wata ran

umman abba ta tashi da matsananciyan mura,

lkcn ahj babba yaje legos don taho da kaya. ahj

qarami ne yakaita asibiti bayan gwaje gwaje, an

gano ciki wata biyu da yan kwanaki. murna gun

ahj qarami tamkar yayi tsuntsuwa yaaje ikko ya

fadama ahj babba. suna isowa ya shiga gun

tsohuwa ya sanar da ita. nan take tasa kukan

murna.ita kuwa suwaiba tamkar mafarki, sai

kunya ta isheta. lkcn da ahj qarami ya fadama

sahura, sai cewa tayi um, bana an tabuka, ni dai

gani da cikin na shida amma sai yauxu ta samu

daya. ahj qarami yace kinji matsalanki, ke ba dai

kiji wani ya samu qaruwa ki taya shi murna ba,

sai dai baqin ciki. ta ja tsaki bakin cikin me

xanyi? tunda ni ga nawan. ciki mai laulayi

suwaiba ta samu, wanda duk abin da taci sai ya

dawo. wannan lamari ya daga ma ahj babba

hankali da abba, duk aikin gidan abba ke yi, ga

makaranta, ko an hanashi sai yayi.dan haka aka

dauko harira qanwar suwaiba, wanda mijinta ya

mutu. umman abba dai bata samu kanta ba saida

cikin yayi wata biyar. sannan ta samu sauki.lkcn

sahura tanada cikin wata bakwai, lkcn haihuwa ta

haifa mace, murna gurinta kamarme, dan sai

yanxu ta samu mace. safiyar talata umma ta

tashi da naquda, hankalin ahj da abba ya tashi

matuqa. duk da tsohuwa tana ta kwantar masu

da hankali, ranan abba ko makaranta bai jeba,

duk da san makarantansa, har suka dawo sallan

axahar shuru. ahj babba yace tsohuwa bari na

samo mota akaita asibiti. tace to. yana fita ba

jimawa ta haihu. ta santalo yarta mace mai

matuqan kama da ahj babba. tsohuwa tace da

abba,mai sunan mlm bi su ahj kace sudawo ta

haihu. dama harira tasa ruwan wanka lkcn da

suka xo ta fito daga wanka.nan aka wanke

yarinya yan barka sai xuwa suke amma sahura

saida aka. Sahura saida aka kwana sannan ta

shigo. ta dauki yar ta taba baki tace wannan yar

baqinqirin haka sai idanu daqwa daqwa. wata

mata da taxo barka tace ai wannan yar sak

abba,suna kama sosai. sahura ko kunya ta ce

basa wani kama da abba. da tasamu kyan abba

da tayi kyau, umma tayi ma matan alama da

haunu tai shuru. ranan suna taci sunan tsohuwa,

wato habiba, dan haka umma ke ce mata ummi.

abba yana ji da ita, saidai in yanasan tsoka nanta

sai yace dubeta ta ba ummata wahala, sai na

xaneki kika girma kika qi mata aiki. umma taita

masu dariya. tsohuwa ma naji da ita dan guta

take wuni. tunda ga kan ummi umma bata qara

haihuwa ba. abba yana aji uku suna qoqarin xana

(j.s.c.e)ya dage sai ahj ya saka shi shagon dinki.

ahj yace abba kabar batun dinkinnan ka tsaya a

karatunka. yace ahj nidai ina so kaga inna iya su

umma sun huta dakai dinkin su gidan laminde.

umma tace ka barshi yayi ahj sana an hannu ai

tanada dadi, kaga in ya gama bokon ba bai samu

aiki ba xaya riqe kanshi da sana anshi. ahj yace

to shi ke nan Ahj yace, to shi kenan, wane shago

ka ke san shiga inkai ka? yace, na can bakin titin

nan, in da kake saya na lemo. ahj yace shi kenan.

mafarin shigar abba gurin koyan sanaa kenan.

ummi ta taso da rigima, tsiwa tare da tsokana,

wanda yasa suka daina shiri da abba sam. abba

ne ya kaita makarantan boka da islamiya, kullum

yaje daukota sai ya raba fada ko ya bada hakuri.

umma kullum addua take fili da xuciya da lokutan

sallah, allah ya shirya mata ummi. ita kuma tata

kalan quruci yan kenan inta girma xata daina.

tsohuwa takance aini me sunana kingama min

komai, domin banasan ragon da, da in kai qara

gara akawo min na bada haquri. duk lkcn da tayi

wannan kalman sai sunyi fada da abba, dan cewa

yake ai dama tsohuwan nan tuni na ane kin daure

mata gindin ta siqa tsokanan yayan mutane. ita

fa mace ce ba namiji ba, shi kenan bata da aiki

sai dambe? tsohuwa takance batta tayi. tunda

ganan abba basa shiri da tsohuwa. ita kuma fati

yar sahura kamar ummace ta haifeta dan bata da

hayani. ummi kuma kamar sahura ta haife ta.

Wata rana abba ya ke cewa, umma da ace lkc

daya kuka haihu da umman bashir, allah cewa

xanyi kunyi canjin yaya. umma ta dube shi dan

me kace haka? yace sbd masifar ummi irinna

umman bashir ne, fati kuma ba ruwanta kamar

ke.dariya kawai take yi. kwanci tashi ummi ta

gama pry, lkcn abba yana shekaranshi ta qarshe

a jamia. yana karantan (mass comm)ne dan yana

san xama dan jarida. umma tasoshi da likita

amma yace baida raayi. tace kaga kai bakada

hayaniya abba aikin jarida na masu maganane.

yayi murmushi yace umma kenan. ummi ta samu

shiga aji daya a qaramar sakandare. maimakon

hankali abin nata sai gaba yakeyi. aduk lkcn da

tai laifi abba ya daketa sai tayi wani abun dan

tabashi haushi, da sunan ta rama. ahj babba ya

bude mai shago, tare da xuba mishi kekuna.

tsohuwa tace dakai wanine mai sunan mlm, saika

tafi da takwarana ta koya. abba yace ko a

kwafan shago na na ganta ba sai na karya mata

qafa ba. ummi ta murguda baki, sai daya tafi

sannan tace allah ya kiyaye inje wannan qaxamin

shagon nashi. Tsohuwa ta ce,”tafi can kema da

baki son ci gaba, in banda abinki da zaki kwantar

dakai ki koya in an tashi auranki basai a saya

miki keken ba. in kuma shi kika aura kinga

shikenan inya samo dinkin da yawa saiki taya

shi, ta ce”Allah ya kiyaye me xanyi da yaya

Abba,yayi ta cin xalina?ni bana son shi” Umma

dake gefe tana jinsu ta ce,”ke in kin samu kamar

Abban ma ai kinji dadi,shine zai ce mai zaiyi

dake? mara hali irinki.” Ummi dai tayi shiru tasan

inta cika surutu kan Abba yanxun nan umma ta

doddoketa,umma tafi son Abba fiye da ita. watan

ramadan ya tsaya,duk daukacin musulmi sun

dauki azumi ranar da akai na uku Abba ya shigo

gida karfe daya saura. daga shago yake zaiyi

wanka yaje makaranta don yanada darasi karfen

biyun rana. Gidan shiru kowa na bacci,don haka

bai shiga dakin umman shi ba don baya son ya

tasheta ya shige bandaki. Da ya gama ya fito ya

nufi daki kamar ance ya kalli madafi, ummi ce

tsugunne tana cin abinci. ya tsaya yana kallonta,

dagowan da xatayi suka hada ido, yace ke! karya

axumin kika yi? ta toshe bakinta sannan nace

dan allah yaya kayi haquri. yace fito muje. ya

kaita dakinshi yasata gwale gwale. da xashi

masallaci ya kulleta ta baya. ya ce inyaso ki

tashi kafin na dawo, xan gane. yana fita tahau

binci ken abinda xata lalata mashi. ta ciro bidiyon

da yake kallo xata doka da qasa, sai taga kwalin

wani kaset tana kallon hoton jikin kwali, na

tsiraici ne. ta xare ido kicin mamaki, tace lalle

yaya abba, daman shi dan iskane? to kuwa xan

tona mai asiri. ta turashi cikin xaninta, da taji

motsin shi yana bude qofa sai ta koma inda take.

ya shigo ya kalle ta ya ce nasan kin xauna dan

kinga bananan. ya xauna bakin katifa, sannan ya

dubeta fuska daure. ummi meyasa kika karya

axumi? tace ba komai. yace tunda aka fara axumi

kike karyawa ko? tace yaune kawai yaya abba.

yace kinsan hukuncin wanda ya kasya axumi da

gangan. Tace eh an fada mana a islamiya, amma

mlm yace sai wadanda axumi ya wajaba akan su.

ya kalle ta cike da mama ki, a xuciyanshi yana

cewa, yanxu har yarinyan nan tasan akwai

wadanda axumi ya wajaba akansu? afili kuma

yace lalle ummi kina buqatan sa ido. dama

saboda bai wajaba akanki ba shiyasa kika karya?

to daga yau xansa maki ido, kuma xan fadama

umma ta sa maki ido. hakanan duk wani abu da

akeyi lkcn axumi an daina qyale ki, xaki ringa

sallar tarawi, ke har tahajjud sai kinyi shi. sannan

bayan axumi saikin rama wannan axumin. ya

xuba mata ranqwashi a tsakiyan kanta ,tare da

cewa tashi ki fita munafuka. daga dakinshi bayi

ta shige ta qara kallon kwalin, sannan ta maida

ta soke shi, tace sai na tona maka asiri. da dare

bayan angama bude baki, abba xai tafi tarawi ya

shigo dakin umma yace ina ummi? umma tace

gatanan kan kujera tayi sharkaf, wai yau taji

axumi. abba ya shiga ciki yana kallanta. yace

umma xaki yaudara ko yar rainin wayau, tafa

karya axumi daxu da rana na ganta tana cin

shinkafa. Yace shine kika xube wai ke kin sha

wuyan axumi ko? umma ta dube ta tana mamaki,

tace abincin da kike kinba almajirai da ma qarya

ne? ya dubeta yace biyu kenan ga larya axumi ga

qarya, xaki sani. tashi muje salla ko in ballaki.

umma tace allah ya shiryi halinki. abba yayi

dariya tare da cewa, kema dai umma yaxaki

amince da batun wai tac almajirai abinci, su basa

axumi ne, umma tace tunanin haka sam bai xo

min ba. saida ya sakata sahun salla, sannan ya

nufi gun maxa. bayan ya gargadeta da cewa in an

idar ta jira shi, inyaxo batanan sai ta sani. koda

aka idar da yaxo bata nan gurin ya kaure da

dambe da wata yarinya wai da suna sallah tana

bigeta. shine daga idarwa ta cakume yarinyan da

fada. bai tsaya sauraranta ba ya cire ta kalmi ya

shiga dukanta, sannan ya tasata xuwa gida. sai

da ta shige dakin tsohuwa sanna ya koma nashi

dakin. hakanan suka ta xuwa masallaci har

axumi yakai ashirin. Ahj ya kawo masu shadda

da leshi da atamfa na sallah ita da umman su

bashir da fati. ya suya masu takalma da mayafai,

abbane xai masu dinki, ran ummi baya son dinkin

abba, domin wanda take so bashi yake mata ba.

ta ce umma dan allah nidai a bani dinkina na

kaima laminde, yaya abba baya min ne kyau.

umma tace kije ki karbo da kanki. tace ai baxai

bani ba ne, xai dakeni. umma tace ai nafi san ya

dake kin, lamindan finshi dinki mai kyau tayi ne?

ummi tace nidai gara ita. tsohuwa tace ai banga

lkcn da mai sunan mlm xai faranta ma takwara

ba, kullun burinshi ya quntata mata. umma tace

tsohuwa ummi fa ba a mata gwaninta, inace dinki

in yayi mata har aro ake xuwa yi? ta dube ta

tace keda shine inya jiki kyayi biyu babu, yaqi

maki dinkin luma ya hana kayan bare kiba

laminde inga ta tsiya. qarfe dayan dare ya tura

dakin tsohuwa tana xaune a kan sallaya tana

addua, abba yayi murmushi. tsohuwannan kina

birgeni dama kina ibadan dare? ya kalla kan

gadonta, ummi taya dai dai tana ta bacci./ ZURFIN CIKI book 1 part 3 ZURFIN CIKI book 1 part 3 Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 21:42 Ya kalla kan gadonta, ummi taya dai dai tana ta bacci. Yace, ummi ke! ummi!! tashi. tsohuwa tana yi masa alama da hannu gami da gyaran murya, wai ya bar ummi maimakon haka ma sai ya dauki wani kofi nan gefansa da guntun ruwa a ciki ya watsa mata a fuska. ta farka firgigit, yace taso, da sauri ta tashi yace dauko hija binki maxa. ta dauka suna fita tsohuwa tana sallamewa. tace kai mai sunan mlm ka lafama yarinyan nan haka, wai axumi wajaba akanta yayi da xaka tasheta da tsohon darannan xuwa masallaci? yace kema in xaki, xo muje. ya tasata suna tafiya tana hada hanya suka tafi tahajjud. sai qarfe hudu na asuba aka tashi. ummi har kuka tayi saboda tsananinjin bacci, amma tana tsoran kar ta kama bacci yaxo ya same ta. tun tana layin bacci har ta gyagije. sakamakon tashinta da matan kusa da ita keyi. kafin kwana uku ta saba da sallan dare, lkc nayi xata farka. abba yana xaune ga dinki gabanshi amma yana can tunanin bushira, yarinyan da yake matuqan so ce. amma yana shakkan fada mata,dan iyayanta sunada kudu matuqa. kuma shine yakema duk yan gidansu dinki. Ahmad abokinshi da ke gefe kuma sai yayi murmushi, yasan tunanin bushiqa ne ke damun sa, dan haka sai ya ce, abba kasan allah, abari ya huce shi ke kawo raban wani. haka kuma ZURFIN KICI, ba xai kai ka gaci ba. ka fada mata kawai. abba ya ce hum ,ina tsoron kada ta ce bata sona, dan bansan ina xansa raina ba. ahmad yace daga ganin yadda take jin kunyanka tana sanka. abba ya kalli ledan da ke dauke da dunkunan su bushiran, yace ina xatan yau xasuxo amsan kayansu, dan tun jiya nace suxo.ahmad yace to in sunxo kayi qoqari ka fada mata mana, indai ba ragon namiji kake ba. abba ya tsurama qasa ido yana tunanin in sunxo mai ce mata? kusan awa biyu sukaje sukai sallan axahar, tungan motan ta tsaya yasan tasu bushurane. shi kadaine a shagon sauran basu dawo ba. bushura ta shigo da qannansu da yarsu aisha. ya taresu da faraa, suka gaisa kan bushura na qasa, sam bata iya kallan abba tela kamar yadda suke kiranshi. Ya tura masu kayansu suka duba sunata murna dan ya masu wadda sukeso. aisha ta aje masa cikon kudinsa kan table. har sun fita yagadai baxai iya hakuri ba, yace bushura xo gashi. ta juyo tana dariya taxo. yace bushura inasan na fada maki wata magana gashi kuna sauri ko? ta kalli motan tace fada min. yace kina sona? ta xare ido sannan ta ruga da gudu. gabanshi na faduwa, bata tsaya ba sai mota. ya kwantan da kanshi akan keken yace menene maanan gudun da yarinyannan tayi? ya tambayi kansa, qarfe uku sunada lecture, amma baya xatan xashi makarantan. ahmad ya dubi abba wanda daga ka dube shi xakasan yana kin damuwa. yace wai banaga sunxo ba? ko ba motan su bane? shiya bandawo ba nakuma hana yaran dawowa dan ku sasanta. abba yace um, inaga yarinyannan gara na haqura, dan bana san insa kaina cikin tunani. ahmad yace ban gane ba, abba yace, to naga daga tambaya tana sona, saita kwasa da gudu ta shige mota. ahmad yayi yar dariya sannan yace ,amsan ta baka. tana nufin tana sonka. abba ya harare shi kada ka maidani dan iska, ina ta magana ta xabga da gudune shine tana sona? yace jeka tambayi manya .yaci gaba da cewa kaine baka mata magana da hikimaba, ka fito mata kai tsaye baka sakaya ba. abba yace, kai nifa ka sanni ba ruwana da wata kwana kwana, idan abu yayi min bana kwana, inko bai min bama haka, ni ba ruwana. Ahmad yace sai xurfin kici ko? da ya aka shawo kanka ka fada mata,abba ya mike tare da kallan agogo, yace inada lecture. gida ya nufa dan shirin xuwa makaranta, har yayi kamar ya tambayi ummanshi cewa in ka ce ma mace kana sonta taji kunya ta gudu wai alamun so ne? sai kuma ya kasa, yana jin nauyi amma in bai samu wata manufa ba dole yaxo ya tanbaye ta dan baya boye mata komai.bushura yar ahj sale ce kwamishinan gona na wannan xamani, gidansu yana karkasara. danqareran gida ne ginin xamani, sun san abba ne sanadin dinki da yayi wa wata qawansu jamila.dinkin yayi matuqan birge su dan haka suka fara kawo masa dinki, tun ranan da ya fara ganin su bushura ta kwanta mashi a rai. to ashe ita ma yamata.shiyasa yau daya furta mata take ganin kamar anmata gafara da aljanna.wata xuciyar tace ,to yanxu da kika gudu in ya xaci baki sansane fa, nan take hankalinta ya tashi har tana rayawa ga abba can da wata.dan haka taga dolene ta koma gun sa inhar tana sansa. dan tasha ganin mata na masa tayin kansu in sunxo kawo dinki.nan ta soma tunanin wace dabara ce xatayi ta fita?saiko ta warware daya siket din kayanta cikin dare.da safe ta nunama momynsu tace mata telan ya manta bai hada wannanba,dama yace xai gwada nine kafin ya hada.momy tace direba ne xai kai mashi.bushura tace momx xaifa gwadani ne muje dai xa kaini.tace to kuje, bushura ta danyi gayunta suka tafi.saidai kash! bata samu abba ba ance mata yana gida. tace gidan da nisane, aka ce mata babu nisa,dan haka ta sa aka rakata.tacema direbansu tana xuwa telan na gida.gidan ba nisa. A qofar gidan su abba ta tsaya, sai ga ummi ta sheqo da gudu tana dawowa daga aike.ta tsaya tana kallan bushura, sannan tace lafiya?bushura ta dubeta. yauwa abba yana nan?budan bakin ummi sai tace yaje kashi ya fada a masai.bushura ta dafe qirji, yaushe? ummi tace oho.sai ga abba ya futo sanye cikin shadda bulu mai duhu yana ta qamshin turare.shawara ya yanke lkcn da yake xaune a shago kan cewa yaje gidan su bushura,tunda gidan kwamishina ba boyayye bane,suka hada ido da bushura,ta saki faraa sannan ta dubi ummi,kince ya fada ina? ummi tayi ciki da gudu.ya bita da kallo sannan ya kalla bishira,me tace maki?bishira tace, ba komai.saidai dariya da maganan ummin tabata.yace tunda baxaki fada min ba xomuje ki gaida ummana.cikin muryan jan hankali tace ina jin kunya.ta bude jakanta tace kamanta baka dinke wannan siket dinba.yace mugani,yaga yadda aka warware shi aka cire xaran da kyau. murmushi yayi dan yasan ya dinka siket din,kusan shinema na farkon dinki.ya gane yaran nata qila san ganinshi take san yi. Ya dinke siket din yana cewa”to amma sai dai ayi min izini inzo gida in kawo da kaina in na gama.” tace haba dai,ya za ayi in taso ka?”ya ce,”ba komai,in dai anyi min izini sai inzo,” ta ce,”to in maka kwatance?” ya ce,”a’a huta kada ki bata bakinki,nasan gidanku zanzo anjima bayan tarawih.” ta ce,”to.” sai mun zo” tace”ku dawa? ya ce,”abokina mana,kinga zo muje gurin ummana ku gaisa.” Bishira ta bishi cikin jin kunya.tun kafin su shigo daman ummi ta shiga gurin umman da gudu tace mata”umma ga budurwar yaya Abba.” Umma tace budurwa kuma? tace eh ai zama su shigo.daga nan ta kara kyallawa dakin tsohuwa tana fada mata. Umma dai jim tayi dan bata da wani burin da ya wuce ta baiwa Abba ummi,kuma da tasan har zai ga wata can da wuri haka data fada masa kudurinta,sa tay ‘ZURFIN CIKI’ gami da nauyin baki……. sallamar Abba ce ta katse ta ta ce,”shigo Abba.” ya ce Umma bakuwa ce taxo gaisheki.Umma ta fadada fara’arta tace to shigo,ba dai surukar tawa bace?” ya ce,”ai ita ce kam” Bishira ta shigo tana sunne kai,ta gaida umma Umma ta ce,”masha Allah,Allah yasa rabon muce.”Abba yana dariya ya ce,amin ummana.”ya dubeta,”tashi ki gaida kakata.” suka nufi dakin tsohuwa,umma ta jinjina kai .tabbas Abba nason yarinyar,in ta dubi yanda yake fara’a da zumudi. a fili ta ce,”Allah yayi mana zabin alkairi.”ummi na kwance kanta na cinyar tsohuwa,sai ta kalli bishira ta tuntsure da dariya,lokacin da suke gaisawa da tsohuwa. Abba ya ce,”dariyar uban me kike yi?” sai ko ummi ta sake shekewa da dariya. ya nufota ya suri kafafunta,tsohuwa ta ce haba mai sunan malam yanxu in bata yi dariya ba kuka zatayi?” ya ce,Bishira tashi muje” Tsohuwa tace to yanmata mun gode ki gaida magabatan naki,sannan kiyi ta hakuri da halin wannan miskilin.” Umma ta ce,”tsohuwa kodai kishi ne?suka yi sallama,ummi wadda tunda ya shureta ta rigasu fita sai ta dauki takalmi Bishiran guda daya takai soro (zaure). don haka da suka fito suka shiga nema ummi ta kule uwar dakin umma tana ta dariya tana lekensu. Abba ya ce,”ummi! ummi!!” taki amsawa ya nufi waje da niyar dubota don yasan ita ce zata dauki takalmin,sai ga takalmi a kofar shi. Don haka ya dauko kawai ya dawo ya bata umma ta ce,”ka kaita su gaisa da umman Bashir.” Abba ya ce,”a’a ba yau ba.”ya rakata wurin direbansu,kusa da shagonshi sukayi sallama da alkawarin zai zo washegari. yaje kuma bishira ta fada masa lallai tana sonsa sai dai tana tunanin iyayenta ko zasu amince? ya ce,to shi dai zai turo magabatansa su nemar masa izinin zuwa zance kamar yanda yake a shari’a Bishira tace a’a ya bari tunda yanxu shekarar farko take a babbar sakandare(s.s.1)ba za a bari ya dinga zuwa ba,amma zasu dinga haduwa gidan yarta dake na’ibawa. Abba baida zabin da ya wuce ya yarda da hakan tunda tace baza a barta yin tadin ba.sai dai fargabar shi kada nan gaba sunyi zurfi cikin soyayya ace ba za’a bashi ba. ta ce,”Babana bashi da matsala,amma momy dinmu ce abin tunani.”Abba ya ce,”shikenan Allah ya shige mana gaba.” soyayya ce mai karfi ta kullu tsakanin Abba da bishira,wanda har ummanshi da kanta tasan cewa Abba yana son yarinyar. Domin duk lokacin da zaije gurinta tana lura da zumudin da yakeyi,kazalikain tace ka gaida surukar tawa, bakinsa baya rufuwa. Don haka sai ta tattara batun ummi ta aje a gefe addu’a ce kadai bata daina ba.ana sauran kwana uku sallah.Abba ya siyo fenti yazo da mai fentin nana ak fente gidansu ciki da bai. Da yamma kuma ya kawo dinkunan su ummi da fati,ummi tasa ihu,sam irin dinkin da ta aro gurin kawarta Amina ba shi yayi mata ba,ya zai mata dink iri daya da fati? ya ce,”kin isa ki sani in miki dinkin da kike so?ta ce to ni dai bazan sa ba umma ta rafka salati tana kallon ummi ta ce,”ummi kina da hankali kuwa? kudi kika biya ko ko Abban sa’anki ne?” tace cikin kuka to ni umma ya zai min iri daya da fati? ya dubeta a fusace,”in kin bari na dauki kayannan wallahi bazaki sasu ba.” Umma ta ce,”ni da zaka daukesu ma da naso”tsohuwa ta fito ta ce,”saboda me? akan wane dalili zaka amsar mata kaya?tunda baka mata wanda take so ba sai ka kyaleta.” Da hannu Umma tayi mishi alamar yayi shiru,sannan ya fita waje.Abba ya kada kai ya fita. washe gari kuma ya shiga da me fenti har cikin gidan Alhaji karami,sahura tana daki lokacin da yake nuna ma mai fenti guraren da zaya fara. Ta fito daga daki ganin Abba sai ta hade rai sannan ta ce,”mune kashin baya? ai dama ka bar shi tunda baka mai da mu wani abu ba,mu ne dai baka so din mahaifanka. Ta dalilinmu zaka shiga aljanna,ba dalilin wasu banzaye ba da sauri ya nufi hanyar fita waje don baya son yaji zagin da zata yiwa Alhaji da Ummanshi. wannan na cikin dalilin dayasa baya son zuwa gidan Alhaji Babba da Umma,sune suka ci kashi da fitsarinsa. suka bashi tarbiya da ilmi,suka ci da shi suka shayar dashi.amma sam basa yi masa abinda umman Bashir ke masa. haihuwarsa ce kadai su Alhaji babba basu yi ba,sahura tana zuwa har shago tayi masa rashin mutunci,sannan ta ce ya bata kudi,ta ce ya ba bashir kudi ko ta aiko fati. Bai taba kin bata ba,amma duk da haka bai tsira daga zagin rashin mutunci ba.ta ce ya tare a gidan ummanshi komai nashike mata,wai da kuma sam ba haka bane. Umma bata taba tambayar shi sisi ba,haka nana duk lokacin da ya bata wani abu ko ya sai mata,sai tace ina na umman Bashir? kaje itama ka bata,in ko bashi da yawa ni naci girma ka bata. Ranar sallar idi kuwa ummi koda tayi wanka kin saka sabon kayanta tayi sai na bara. Lokacin da zasuje sallar idi,Abba ya fito daga wanka ya kalleta ina kayanki sabo? ta tura baki”ni baxan sa ba.” Yace,”to zanga wanda zaki bi masallacin,kuma ki kara magana saina fasa bakinki.”sai ta wuce kofar dakin tsohuwa,sannan ta ce,”to ai dai nima nasan hanya,kuma sai naje.”ta fada dakin da gudu. ya bita bata san yaga tsohuwa lokacin da ta shiga wanka ba,bayan fitowarsa.don haka ya ritsa ta ya kwakkwada mata mari,sannan ya rike mata kunne. zan kara fada ki fada? ta ce,”a’a kayi hakuri.” ya saketa ya wuce,ta zauna tana kuka. misalin karfe hudu na rana ,bishira ta iso shagon dinkin ita da direba,shagon a rufe.don haka ta ce su karasa gidan. Can dinma baya nan,amma sai ta fito ta shigj gidan dauke da tire babba cike da kuloli. cikin kunya ta gaida umma,ta kuma bada a aje masa.umma ta ce,”to ko ina Abba yayi? kila gidan su Ahmad yaje.”umma ta ce,”ke uwar gudu ina yayanki?” ta ce,”nima na ganshi?” karar bude kofarshi suka ji,ta ce,”leka in shine kice yayi bakuwa.shine kuwa,jin cewa ga bishira ya shigo da zumudi. Umma tace ka kaita ta gaida umman bashir. yace to, ta fito ta tafi kicin ta bar masu dakin,ashe ummi tana uwar daki tana jinsu.ya ce,yanxun fa daga na’ibawa na ke,ina ta xumudi in ganki. tace,na xaci ba xa kaxo ba ne,nace bari inxo ni,dan baxan iya kai dare batare da idanuna sunganka ba.ummi ta toshe bakinta saboda dariyan da yakesan kufce mata,yace sai inga kamar bakya sona.bishira tace haba abba, in kace haka bakamin adalci ba.yace to wadannan kulolinfa me kika kawo min?ta ce bude ka gani.ya bude ya gani yace kai, lalle ashe ni dan gatankine? tace sosai ma.ya marairece murya yace to bani abincin a baki.ummi daga cikin dakin tace, la’ilaha illallahu.abba ya miqe da sauri.kafin ya ankara ummi tayi fitan bindiga tsakar gida tana fadin la’ilaha illallahu,dama yaya abba dan is….umma ta gwabe mata baki,bayan ta fito daga dakin ahj babba.ummi wadda inta s6a magana ko ana hanata sai ta kai aya.ta dafe baki,tace maci gaba da fadin,umma to kinji abinda yake ce mata ne? umma ta jefeta da takalmi tare da cewa,wai baxa kiyi min shuru ba? ummi tace,to fa cemata yayi xai bata abinci a baki,kuma daman xan nuna maki wani kaset da yake kallo. Abba ya riqe kai tare da cewa ummi in na kamaki xaki sani, kaset din wa kikaga ina kallo? tace na yan is….da gudu ya bita ,yayin da umma ta jefa mata murfin kwano,amma duk haka ko da ta fita waje saida tace masa sai na nuna ma ahj kwalin kaset din.take ya tuna da kwalin kaset din daya boye,wanda ya qwace a hannun bashir,kaset din tsiraici ne wanda laanannu sukayi.abba cikin takaici yace,kai ummi! kai ummi!! kinsan allah in kina wasa dani xa karyaki a banxa.ta ce to ba a dakinka na gani ba?yayi qwafa,allah ya sani ya tsani ummi kamar ya shaqeta ta mutu.sai ya samu kanshi da qin komawa gidan,kunya da nauyin umma yake ji,yasan dai ba xata kama xancan ummi ba,amma yasan xuciya da xargi,qila xuciyanta ta xargi wani abu.bashir ya fito daga cikin gidan su abba yace,yauwa bashir shiga gidanmu kace bishira taxo. Bashir rai bace ya shiga,dan yana jin haushi ya amsar me kaset.ya shiga umma na qofar kicin xugun tana tunanin halin ummi.bashir yayi sallama umma ta amsa.yace,abba ne yace in kira bira ne ni yace ne?umma tace gatanan ciki,taxo bakin qofa ta kalli bishira kanta na qasa tana mamakin ummi.yarinyan sam bata ji.umma tace kixo yana kira awaje.cikin kunya ta fita, yace da bashir rakata gun ummanka su gaisa.bashir yayi fara,a antynace ke nan?abba yayi murmushi. bishira ta xauna gaban ummansu bashir suka gaisa. bashir yace,budurwan abba ce. sahura tace,yau kika taba xuwa nan unguwan? kanta na qasa tace, xuwana biyu kenan.ta kalli bashir tace kaji ko? amma shine ko a turo ta nan gidan.nina haifi abba amma an gaje min shi.tace yarinya duba nan.bishira ta dubeta,ta dafe qirjinta ni na haifi abba nine uwansa.matan gidan can mai gidana ya bada shi a gunta,da ubansa da maigidan dan wa da qani ne amma sun gaje shi.bani da ikon sashi ko hanashi amma sun mallakemin shi. da muryan tausayi take maganar. Bashir yace, umma indai ya aurota xamu samu sauqi.bishira tace kada ki damu, insha allah komai xai warware. tace, to yan nan na gode.fati ta shigo ta gaidata cikin nutsuwa, bishira tace wannan qanwansa ce? umma tace eh, ai su ga sakamakon mugunta nan sun haifi yar muguwa mara jin magan. bishira tace, kai yarinyar bata ji. fati ta ce abba ya ce kixo.sahura tace kinji ko? shifa ko nan gidan baya qaunan shigo wa.bishira ta miqe ta balle jaka ta ciro sabbim kudi yan ashirin ko irgawa bata yiba ta bata, tace kinsaya goro.sahura tace harda abin arxiki?to an gode.bashir yace antyna inane gidanku?tace karkasana gidan kwamishinan gona.bashir ya raxo ido, nako san gidan,lalle antyna ina qara gaisuwa.bishiratayi dariya.abba na tsaye suka fito,yace mata to ki tafi xanxo amjima. tace baka kaini dakinka ba.ya girgixa kai, bai dace ba wannan ba mutunci bane,sam bai kamace yar mutunci suna xuwa dakin samari ba. bishira tace danme? yace sharia bata amince ba, damin duk lkcn da mutum biyu suka kebe,musamman mace da namuji. Abba yace na ukun su shedan ne. irin wannan yana haifar da xinace xinace a bayan qasa.tace hakane ta tafi.abba ya rakata har mota, bashir kuma tamkar maroqi, sai fadi yake allah ya tsare antina ki sauka lfy.bayan tafiyanta abba bai iya shiga gidan ba tunaninshi daya kada umma ta xargeshi.dan haka ya nufa gidansu ahmad.ya ba ahmad lbrn abinda ya faru.dariya ahmad yayi tayi.yace kai amma wannan ummin taku yar dirama ce. abba yace cikin takaici yanxu kai har kaga abin dariya?yaja tsaki yace allah na tsana ummi, namata muguwan tsana. dubi wannan yarfin da tai mani. ahmad yace xata bari, wata ranama ko ance tayi watace sam batayi ba.abba yace taf wannan yarinyan dawuya in xata taba yin hankali, duk wanda ya aureta ya auran ma kanshi fitina.ahmad sai dry yakeyi. da magariba ya shiga gidan,cikin saa ya samu ummi tana cin abinci.nan take ya kama hannun ta har saida tayi yar qara, yace muje ki dauko min kwalin kaset din da kika dauka, Umma tace, Abba na soma tunanin yarinyar nan tan da aljanu da gaske. abba yace hakama alhaji qarami yace, amma fa anje babu kowa akanta. ya saki ummi bayan ya ranqwasheta. sannan ya ce, in kika sake yarda ki kaga wani abu a dakina kika dauka sai na balla ki. washegari abba ya tasa ummi ya nufi gurin masu ruqiyya, amma da aka mata babu kowa a kanta kamar yadda ya xata. ya dawo ya sanar da umma,umma tace na gode allah.halinta ne ita kuma irinta kenan? yace irinta kenan umma,baxata canxaba saidai muyi ta mata addua, soyayyan abba da bishira ta bunqara,har dangin abba sun san da batun,sahura duk tabaxa ma dangi.sanadiyyan maganan da tayi ma bushiran na cewa an rabata da daxta. wata rana bishiran tace masa xata xo gaida ummanshi,yace to cikin xumudi sai tace, umman su bashir fa nake nufi, ba ance ita ce mamanka ba? abba ya ce inji wa? inji ummanka. abba yace sam, ummana ba xata fada miki ba sai dai ko ita umman bashir din. tabbas itace ta haifeni, amma ba itace ummana ba.tace dan me? nan take ya hada rai. Abba yace mata ba matsalanki bane, so ban so ki saka kanki ciki. nan take ta yarda da batun umman bashir.ta a mince qwarai umman da abba ke kira umman shine muguwa ce.kuma itace ta raba abba da umman shi.dan haka saita tsiri xuwa gun umman bashir, tare da yi mata kyauta.shiyasa suka saba sosai.duk xuwan da bishira xatayi sahura saita kukkushe umman abba, tare da yi mata sheri. dan kawai bishira ta tsaneta,kuma bata xuwa gunta koda taxo anguwan. abba bai taba sanin haka ba,ita kuma umma bata taba fadan mai ba, dan ummi ta taba fada mata cewan budurwan abba tana xuwa gun umman bashir kuma bata xuwa gunki. umma tace nida umman bashir duk daya ne intaxo gunta tamkan taxo guna ne. sai kuma habaicin da take jiyowa ta katanga sahura nayi.har ya kai umman abba na ganewa in bishira taxo, domin inxata tafi xakaji umman bashir tana cewa,to na gode yar albarka bakya gajiya da abin arxiki,ai ko baki kawo min komai ba yancina da kika fara qwato min kin biya ni. kuma ina tabba tan maki inkinga abba bai aureki ba baya ry/ ZURFIN CIKI book 1 part 4

ZURFIN CIKI book 1 part 4

Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 21:45

Wannan furucin ke sa bishira na qara shige ma

sahura, duk wannan sha’anin da sukeyi abba bai

sani ba. wanci tashi abba ya samu digree,

sannan yaje kamp din shi a damaturu jihar

yobe.sati biyu yayi sannan ya dawo. cikin sati

biyun nan da baya nan ummi ta baxa iya

shegenta son ran ta, umma ta qosa abba ya

dawo saboda yanxune ta gane tsoran abba yake

sa ummi tayi mata aiki da aike.dan tasan in ya

sani baruwan shi da pushin tsohuwa,xai

nakadetane, amma ahj da umma duk abinda

ummi tayi daxaran xasu hukunta ta xata sa masu

kuka tace dan de aci mata xarafine.shi yasa suka

sakama ummi sunanta,sannan kuma suke

dukanta a gabanta,imba hakaba maisa basuyima

mai sunnan malan ba?dan dole suke qyaleta ,duk

da ummi ta soma tasawa amma sam bata yi

hankali ba. shekarun ummi sha uku tana js2

amma ko yaushe qara tirewa ummi keyi. addua

kurun sukasa agaba,kuma sunsan allah xai amsa

masu. Ranan da abba xai dawo ummi ta kama

yima umma aiki da aike, dan kar a fadama abba.

a ranan ne ummi taga wata alama da ta

tsoratata cikin fitsarinta. a rudenta da hauka ta

nufi gun umma tana cewa, umma na shiga uku

na, fitsarin jini nake yi. umma tace, wane irin

kuma fitsarin jini? ummi sai tsalle take tana fadin

ta bani ta lalace. umma tace ke xonan. ta jawo

ta xuwa cikin daki, tace ke yimin bayanin yadda

kika ga abin. ummi ta cire xani xata cire siket.

umma tace, ke dakata min bance ki nuna min ba,

yaya kalanshi yace? ko da tayima umma bayani

sai ta fahince girmane ya kama ta. dan haka sai

ta kamo ta ta xaunar kusa da ita, tayi mata

bayani game da abin data gani, sannan ta nuna

mata hadarukan da take ciki a halin yanxu. tace

ummi ki natsu kiyi hankali, kisani yanxu kinkai

wani matsayi wanda xakiyi taka tsantsa da

rayuwanki. hadari na farko shine wasan banxa da

maxa, kece mara hankali indai kin sama abokin

wasa ba ruwanki da maxane ko mata ke dai kiyi

wasa, Umma tace kisani yanxu xaki iya daukan

ciki, indai har kika bari wani namiji ya shiga

harkanki. ummi tayi xullo tace umma ciki irin na

bara’atun baito? umma tace, eh ummi tace

wanda har suka yar da yaran aka xo aka kama

su yan sanda? umma tace tabbas. ummi cikin

fargaba tace to ni umma baxan yi ba. ta soma

kuka, to a kaini asibiti a bani magani mana.

umma tace duk bayanin dana maki baki fahinta

ba? ai wannan kin dunga yinsa kenan har

qarshan rayuwanki, ko kuma in kinkai wani

mataki na tsufa. ummi tace, to shi kenan, yanxu

kuma inna yi wasa da maxa sai in xama irin na

bara’atu? umma tace qwarai kuwa. ummi tayi

tagumi tana tuna yadda suke tsokanan bara’atu

inta fito. suna cewa tayi cikin shege tayi cikin

shege! ta dubi umma tace xan daina ma yan

maxa magana. umma tace ki dinga maganarki da

kowa, kidai kula da kanki, sannan duk sokanan da

kikayi da xunubin da ki ka kwasa to fa ki sani an

bude maki fayel. Umma tace xunubinki xaki

samu,gashi bakya san sallar kan lkc, sannan ga

karya axumi.ummi ta sake tsurewa ,tare da fadin,

to ba tsohuwa tace min inna mutu baxa ayi min

hisabi ba,wai ni yarinya ce wai makarantan

annabi ibrahim xa a kaini.umma tace da kenan

kafin ki soma kalar wannan fitsarin, yanxun kam

in kin mutn xa a tambaye ki a cikin kabari,

tambayoyi uku masu sauqi, masu wuya agun

mara rabo.sannan xa a maki hisabi inkinyi mai

kyau kiga mai kyau. tayi tagumi, umma ta manna

mata tsumma a jikin pant. tace tashi kisa in

kuma kinje gun haukan guje guje ya fado mutane

sun gani shi kenan asirin ki ya tonu, kowa yasan

kin girma. ummi dai ranan lafewa tayi kan kujera

tanata tunani. tana kwance lkcn da ake hayaniyan

dawowan abba kannanshi ne suka shigo mai da

kayansa. qasa ya xauna a dakin umma, ya miqe

qafa domin duk a gajiye yake. umma tayi ta dire

mai abubuwan ci wanda tasan yanaso a gaban

shi. sannan ta ba fati kudi ta sayo mai lemun

kwalba, dariya yayi ya ce,ni dan gatane, shiyasa

ina can ina tunaninki ummana, har nace inama

ana tafiya da uwa da na tafi da ke.umma cikin jin

dadi tace allah sarki abba, niko ina nan ina maka

addua allaih ya baka abin da kaje nema,yace

ummana kenan. ummi dai tana jinsu sam baima

gantaba, sai can ya lura yace a,a kekuma lfy?

umma tace bata dan jin dadine. yace tabdi,lallai

kuwa ciwan nan yayi tsanani, ummi da ko a

gadan asibiti take bata daina halinta? umma tace

ai yanxuma nasan lafawa yayi ko ummi na?

ummi dai kallansu take yi. abba yace allah ya

yaye. suka ci gaba da firan su yana bata lbrn

camp tare da nuna mata hotunan da suka dauka.

yace dan ba kusa bane da kunje min kunyi kallo.

ummi da xata bayi sai tafiya take wani iri tare da

ware qafa. saboda rashin sabo. tsohuwa tace a,a

takwara lfy? ummi tace, fitsarin jinin nake yi.

umma ta fito da sauri tace ke ummi xo. tsohuwa

ta saka salati, tare da cewa yarinnan nan badai

faduwa kikayi ba. ummi tace nifa ban fadi ba

hakanan ya xo min. umma tayi mata daquwa

tace bayin kenan? tsohuwa tace ke suwaiba

yarinyan nan faduwa tayi? da yake umma ta

fahinci hausanta sai tace um,lkcn tane yaxo.

tsohuwa ta saka salati tace, ni habiba yau naga

abinda ya isheni? yarinyan yar shekaru nawane

kwata kwata. lalle xamani, to sai ayi axaman

aurad da ita. umma tace waxai kula ummi da

sunan aure ni suwaiba? ki kalla haukan data keyi

a gari. abba cikin daki yace umma wa tsohuwa

take cema ayima aure? umma tace ummi itama

cikin dariya. yace tabdi jam to wannan takwaran

taki waxai kwasa, ga muni ga rashin hankali.daga

bayi ummi tanata murguda mai baki tana cewa

eh din. Tsohuwa kuwa masifa ta hau yi,”gaka nan

mara mutunci a gabana kake zagin takwara?kai

mai sunan malam ka kiyaye ni” shi dai ya fita ya

nufi dakinsa don kintsawa,yana mamakin ummi

ta zama babba. Koda umma bata fada mishi ba

ya gane haka ne ta yadda tsohuwa tayi maganar.

tsohuwa ta dubi umma ta ce,”ki na daure ma mai

sunan malam gindi yana ci ma takwara kashi a

hannu,alhalin yana zaune a inuwarta.nan fa gidan

ubanta ne.” umma ta bata rai matuka,ta ce

“tsohuwa ni da Abba da ummi duk daya suke a

gurina,don Allah kada ki kuma furta haka har

Abba yaji. kai ni da za a ce in zaba tsakanin

ummi da Abba,na rantse Abba zan dauka.”bata

jira abinda tsohuwa zata ce ba,tayi ciki abinta.

tsohuwa ta gama yan mitocinta ta shiga daki.

Kwana biu kamar gaske,ummi an nutsu, amma

abinda ya takura mata na daukewa sai umminku

ta ci gaba da gashi, sai ma abinda ya karu. Abba

ya daga ido sama yana kallon wasu tsuntsaye

suna ta shawagi a sama, zuciyar shi tana cikin

matukar damuwa sakamakon sheshshekan kukan

da bishira keyi, bata san cewa ya fita damuwa da

tafiyarshi kaduna ba? in ma da don ta ita ne da

sauki tunda gidansu da waya zai iya zuwa

(telephone) na bakin titi ya kirata. damuwar shi

umman shi. ta katse shi “yanxu Abba haka zan

daina ganinka?” ya sake tausasa murya.”haba

bishira, ina kano ina garin kaduna?” ta ce, “tabdi,

nifa dalilin kukana taron matan kaduna nake ji, an

ce kwarjini garesu. kawai kaje ka sa samu wata

ka manta da batuna.” Yayi murmushi “bishira

kenan, kada ki dauka son da nake miki mai rauni

ne da har zan canza wata dake, ni dai ki min

addu’a.” ta ce,”sam ban yarda da wannan zancen

ba, ni dai bari in kira antina mijinta zai iya

taimaka maka a barka kano.” kafin ya ce komai

tayi ciki da gudu. yayi yar dariya. bishira tunda

ya ce kaduna aka tura shi duk ta damu. Anti ta

fito daga kicin, bishira ta ce, anti kizo inji Abba.

anti ta dubeta, “in zo?” bishira ta kama hannunta

“don Allah aunty taimako zaki mana, zo ki ji.” 49-

suka xauna sannan abba ya gaidaa anti cikin

girmamawa.bishira ta dube shi ka fada

mata.abba yace me?tace anti kinga fa kaduna

aka tura shi,ni kuma wlh ba xan so yaje garin nan

ba.anty ta sa dariya.to yanxu so kike yaqi xuwa

ko so kike ya tafi dake? tace,ni so nake ki yima

abban nasir bayani,nasan ba xai rasa sanin wani

da ya sani ba.abba da anty suka sa dariya,yace

kamar yaya?tace yayi magana a barshi anan

suka sake tuntsira dariya.tayi fushi ta miqe fuuu

ta nufi cikin falon gidan.anty tace bishira tana

matuqan sanka,dan allah ka kula da ita.ya kalleta

ya sunkuyad dakai,yace nima anti ina santa,kuma

tuni nasa manya susan xancan,saboda in samu

natsuwa,amma tace tana jin tsoron

mamanta.anty tace eh to,dole taji tsoro dan ba

dole bane hjynmu ta yarda,amma shi babanmu

bashi da matsala.abba yace to ni dai xan tura a

kowane lkc,dan ahjna yayi min magana tun kafin

tafi ta camp. Din nan yake ta min zancan.” Aunty

ta ce,”to in kun tashi fa ba gurinshi za’a tura

ba,gurin kaninshi ne dake jakara.amma kafin

hakan sai an nemi izinin Alhajinmu din.” Abba ya

ce,”to ni ko wa zai shige min gaba gurin neman

izinin?”aunty ta ce,”Abban nasir zan sanar

dashi,insha Allahu har wannan din ma batun

(service)din naka zan mishi bayani.” cikin murna

abba ya ce,”to na gode,Allah ya saka da

alkairi”anty ta ce,”ba komai” ta mike “bari in turo

ta don nasan tana can tana cika sai ka bata

baki.” yayi yar dariya tare da cewa”to”. ta zauna

tana kumbure-kumbureya ce”haba tawan har

yanxu baki huce ba?” ta sake kauda kai gefe,ya

ce”to shi kenan,yanzun dai na fasa barin

kaduna.” ta dube shi da sauri,”ka fasa barin

kaduna fa ka ce?” yayi yar dariya”au na

manta.kece duk kin ruda ni,cewa zanyi na fasa

barin kano.” ta share yar kwallarta,”to shikenan”

ya ce,”naji dadin kiran anty da ki ka yi.ina ganin

nan da yan kwanaki su Alhajinku zasu sanni,Allah

yasa ace an bani ke.” Wayyo dadi,ta tuntsure da

dariya.abbana nawa,bana zaton cewa zaka kai ni

murna a ranar.”ya mike zan tafi “ta ce tun

yanzun? to ka ce ina gaishe dasu umma.” Ya

ce,”umma bata cin mike,kullum sai ta ci in gaishe

ki da kyau.amma ke kin ki zuwa gaida ta.” ta

ce,”kasan fa ni bana iya sakewa da ita,nafi

sakewa gurin umman bashir.” ya ce,”kunyarta ki

ke ji?” ta dan tabe baki tare da daga kafada kila.

ya ce,”ina mamakin yanda kika saba da umman

bashir,alhalin ummana tafi saukin kai.” ta ce,”ga

wannan kanwar taka mara kunya.” ya yi yar

dariya sabida tuno abind ummi ta musu. ya ce a

hankali,”zaki saba da halin ummi.”ta dube

shi,”tun ranar dana soma ganin ummi din nan fa

ban taba jin cewa ina sonta ba.” ranshi yadan

sosu,har ma ya gimtse fuska,amma baice kala

ba.lura tayi da canzawarsa.don haka sai ta ce”ka

min afuwa in na bata maka.” nan ma bai amsata

ba.illa sai da safe. Tamkar Alhaji yasan yadda

abba suka yi da antin bishira,da safe Abba yaje

gaida shi ya ce,”babana zuwa yanzun ya kamata

a ce mun shiga maganarku da yarinyar nan.”

Abba ya sunkuyar da kai tare da ce wa,”um,dama

gidan antinta da naje dazu munyi zancen,yanzun

dai su ce sai an nemi izinin shi baban nasu. ta

ce,mijinta zai masa magana,in yaso sai kuji ranar

da zaku je din.” Alhaji ya ce,”to shikenan.Allah ya

kai mu.yanzu yaushe zaka tafi kaduna?” kafin

abba ya bashi amsa,ya ci gaba da cewa,ban so

ba sam da wannan yin nisan da zaka yi damu

Abba.” Abba ya ce,”ina hasashen cewa za a barni

nan kano da yardar Allah,bisa ga taimakon mijin

yayar yarinyar da nake zuwa gurinta.” Alhaji ya

ce,”to Allah ya yarda,sannan in an fada maka

lokacin da zamu gana da waliyyan nata sai ka

sanar dani.” Abba ya ce,”to.” Alhaji ya ce,”ina son

mu danyi bincike kan yarinyar amma mahaifinta

sannanne ne,anata yabonshi.” Abba ya ce,”to.”

Ranar juma’a da misalin karfe biyu da rabi Alhaji

ibrahim (wato abban nasir,mijin anty farida),ya

samu sirikinsa a gida. bayan sun gaisa ya

tambayi yan jikokinshi sai Alhaji ibrahim ya

ce,”suna lafiya.dama makasudin zuwan shi

ne,akwai wani yaro da ke zuwa gurin

bishira,yawancinan gidanmu suke zance. to

gaskiya na yaba da hankalin yaron,sannan ya

damu yana son ya turo iyayensa.to shi ne nace

bari in nemar musu izini tukun.” mahaifin bishira

ya kalli surukinsa ya ce,”aisha ko bishira?” Abban

nasir ya ce,bishira ce.” ya gyara zama. “bishira

ta gama sakandare ne?” Abban nasir ya ce,”ai

Alhaji ba yana nufin ayi auren yanzun bane,a san

dashi ne.” Alhaji ya ce,”bana haka,ka sani sai dai

tayi abu daya,in karatun karatun,in auren to

auran. Ibrahim kasan wani abu daya? duk lokacin

da kasa yarinya ta soma tsayawa da saurayi

bayan tana karatu,musammanirin bishira irin

wadda tasan tsarina amma ta danne ta turo min

saurayi to gara ayi mata auren. Domin doguwan

soyaryannan bata da ma’ana,qarshe sai wata

shedana ta biyo baya,balantana bishira tana da

rawan kai.ya matsa kusa da wayan tangaraho

wadda aka jona ta ke amfani a daukacin gidan,ya

dannan nanbobin sannan ya kira hjy.ta amsa

daga sashanta,yace bishira na ciki? tace tananan,

yace ki turo mani ita,tace to.gaban bishira ya

badi,ganin mijin yarta a gidan dan tasan abinda

ya kawo shi.ta xauna can gefe tace,gani dady,ta

gaisa da abban nasir.mahaifinta yace nasan

kinsan dalilin xuwan ibrahim ko? kanta a qasa

tace,a’a. yace.yace to saurayin da ce xuwa gunki

ne yake san ya turo magabatansa,kuma nasan

kinsan da batun?sai dai inasan kisan abu daya

bana san doguwan soyayya,da xara nagama

buncike akan yaran wanda shari’a tace.inna

gamsu,to fa aurad dake xanyi kije can ki qarasa

karatun in kina so.ahj ibrahin yace yaran yace shi

ba dole sai anyi yanxu ba.nufin shi a amince

mashi.shi kuma xai jira har ta gama

makarantanta. ahj ya katseshi ta hanyan daga

mai hannu,ibrahin kaidai sheda ne bewan bana

haka, kuma ba a haka dani ko?yace auran yata fa

kakeyi,ka san tsarina.ibrahinyace na sani ahj.

yace yauwa,ina nan ban canxa ba.yace yanxu

abinda nake san ka dashi kafin na amince da

xuwan iyayan shi.ya dubu bishira yace kinasan

shi kin amince dashi? tace eh yace tashi ki tafi

angama.kai kuma inasan kashiga unguwa uku ka

binci komin labarin yaran da usilin shi.ahj ibrahin

yace angama.yace naso ace sai ta gana

karatu,dan sai anyi sa’a xata qarasa,anma hakan

xaifimin akan doguwan soyayya kafin inxo inajin

haushi.ibrahin ya miqe to ni xan tafi.ahj shima ya

yunqura xai tashi sai waya ta kama ruri dan haka

sukayi sallama anan. ummi ta shiga gida daga

makaranta take,akuyan umman bashir tagani ta

gani a gidansu tana masu barna a kicin da sauri

ta koma ta saka sakatan gidan,sannan ta

dawo.ta kama akuyan ta kaita bakin fanfo ta tara

kanta sai kuka akuyan take tayi. Umman bashir

ta jiyo daga gidanta,da sauri ta fita taxo tana

buga gidan tana mashifa.yan baqin

ciki,mahassada,yanka min akuyan xaku yi?san

ummi bata ji ba, dan gidan ba kowa. umma taje

sheka can gidansu,hta kuma tsohuwa taje

gaisuwa n mutuwa nan kusa dasu.saida taga

akuyan ta galabaita sannan ta janyo wata leda ta

daura mata a bindi,sannan ta saketa.akuyan ta

tashi da gudu tayi hanyan fita,tace shegiya gobe

kixo ki bude mana abinci kici.taje ta bude qofar

ta jiyo muryan umman bashir,dan haka sai ta cire

sakatar sannan ta dan sanmata qofan akuya tayi

waje da gudu.saboda ledar da ummi ta qulla

mata,sai take ganin kamar binta ake,dan haka ta

nausa cikin unguwa da gudu.umman bashir na

ganin akuyarta tayi fitan bindiga,sai tabi tana

cewa,ku taremin.ummi ta koma ciki tana

dariya.ita kuma umman bashir daqar ta samu aka

ruqo mata akuyan ta.aka kwance ledan taruqo ta

xuwa gida.sai masifa take, tana isowa qofar

gidan umma na RFIN CIKI book 1 part 5

ZURFIN CIKI book 1 part 5

Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 21:54

Ita kuma umman bashir daqar ta samu aka ruqo

mata akuyan ta.aka kwance ledan taruqo ta xuwa

gida.sai masifa take, tana isowa qofar gidan

umma na isa. tace yar baqin ciki kun kama min

akuya kun jiqata xaku kashe min,ta ta allah ba

takuba.umma tace akuya kuma wani iri?ni bana

gidan dawowa ta kenan.ta ce kina nan muna

fuka.umma sai ta shige gida,amma duk da haka

sai da umman bashir ta bita har ciki tace sai ta

doke mace akan akuyan ta.umma ta shige daki

can qurya tasamu ummi a kwance,tace ke uwar

yan daukan magana, ke ce kika jiqa mata akuya?

umma tace cinye min abinci tayi.nan abba ya

riske ta tana ta tsine tsine.yace meya faru?tace

kai ja can ka bani guri,dan baka san darajata

ba,banda an raina ni yaya xa’a kama min dabba

a jiqa?in nai magana sai a maidani mahaukaciya

ko haquri baxa a ban ba.abba yace to kiyi haquri

in sha allah baxa a qara ba.tace baxan haqura

ba,tunda inta mutu nike da asara.umma tafito

tace to yanxu ya kike san ayi?ni dai bananan

ummi ce da wannan tsiyan wai ta sameta ta

cinye mata abinci. umma tace kinsan halin ummi

kuma nima haquri nake da ita.tace to ni baxan

iya haqurin ba.umma ta finciko ummi ta hanka da

mata.ta gata na ki rama mata.ta juya cikin daki

ta kama harko kinta.ba kunya ta kama ummi

tana ta jibga.abba takaicin mahaifiyan shi ya cika

mai xuciya,amma bashi da daman cewa ta

bari.shin baxa tai tunani ba takama yar matan da

tariqe mata danta riqon adalci da amana,tana

duka haka? sai data gaji dan kan ta sannan ta

fito.abba ma fita yayi cikin takaici,ummi kuwa

kuwa tayi tayi har tsohuwa ta dawo,ta sameta

xaune tana dirxan kuka. Dama taci karo da abba

a waje tace mai sunan mlm har ka dawo xaka

kuma fita?yace um.tace miskilin banxa saikace

mai ciwon hakori,ta riska ummi tana kuka,tace

umhum daman tunda naga ya fita yana ta

maxurai nasan yaci xalinci.kai na gaji da halin

mai sunan mlm.umma tace,ba ruwanshi.ummi

taqara satin kuka ba umman bashir bace taxo

tayi min duka.meki ka mata?wai din akuyan ta

taxo ta cinyemin abinci,shine na jiqata da

ruwa,shine taxo tamin duka kuma gashi banci

komai ba, ko qala bata ceba,ta juya sai gidan

umman bashir.ta sameta tana sinke kayan

miya.tace ke sahura saboda bakida mutunci shine

xakixo har gaban uwarta ki daka?sahura tace na

daketa,kamme xata jiqa min akuya?tace wane

shegen ne yace ki saki akuyan ki har taje taci

mata abinci?to kashedin ki mara mutunci da baki

san girman nagaba ba.bashir ya fito yace a’a

tsohuwa kidaina xagan mana uwa har cikin

gidanmu.tace iye!kaxone ka nuna min rashin

tarbinyan ka?nan har wata uwa gareka?nanfa sa

in sa ya tsarke a tsakaninsu.ummata juyo su

tarasa yadda xatayi,sai ga abba ya shigo.yauwa

abba shiga gidan can ka lallaso min tsohuwa taje

kasgedi ataba yar gwal dinta.ta dubi ummi tace

duk aka yar marajin can ni naji dadin dukan da

tayi mata,dan dukan algaki tayi.banda xalunci ya

xata kama dabba ta jiqa? abba ya fita ba tare da

yace qala ba. abba na shiga gidan bashir yana

tsigale tsohuwa tankar xai kai mata duka,abba ya

daga hannu ya wanka ma bashir mari,sannan

yace tsohuwa saankace da xaka dunga mata

wannan fadan.ya dubi umman bashir dan allah

kiyi haquri.sannan yaja hannu tsohuwa,shi kuma

bashir yana ta xagin abba yana cewa allah ya

isa. umman bashir ta ce abba tir da hauhuwan ka

tir!tir! kuma gab nake da in dagama ka nono.cak!

abba ya tsaya kalaman mahaifiyan shi sun shi

jeshi,a hankali ya saki hannun tsohuwa batare da

tasan ya tsaya ba.dan sababin da takeyi yaja

hankalinta.ya juyo har gabanta yace dan allah ki

yafemin ki ya femin.ba tareda ya jira amsan ta ba

ya fita. baiji muryan taba amma koda bata ya fe

maiba jikinta yayi sanyi.da yamma bayan su ahj

babba sun dawo kasuwa sai suka shiga dan

gaida tsohuwa.nan ta saka masu kuka suka rude

tare da fadin me aka mata?cikin kuka tace ni

sahura xatai ma rashin mutun ci tare da danta

bashir nan ta koro masu bayanin komai. Ahaji dai

sukai ta bata haquri,ahj qarami yace shi kam dole

ya cimata mutunci daga ita har bashir din.da

suka fito ahji babba ya ce kada gaje ka mata da

tsin hankali,nashihaxaka yi mata shi kuma bashir

ya girmama yayansa.abba kuwa yana fita sai ya

bar layin dan bacinrai,dakin ahmad yaje ya

kwanta duk da cewan ahmad din bayanan.tunani

yake tayi akan mahaifiyanshi,yadda ta runtse ido

da alkairin da umma da ahj suke mata.ahj qarami

cikin damuwa da takaici ya shiga gidansa,da

bashir ya soma yin karo,nan take ya rufeshi da

fada.sahura na ji ta taso cikin mashifa kada ya

xagan mata da,dan ya nemi tare mata

mutunci.ahj yace har wani mutunci ne dake

wanda xai kare maki?to da kinada mutuncin kin

tunkari mahaifiyata ki mata cin xarafi?tace har

gidannan ta shigo saboda na daki yar gwal

dinta,takan wannan wara mutuncin yarinyan xata

xo ta xage ni?umma tace ma ahj babba ka fito

gashi can fa ahj qarami rigima ta kaure

tsakaninshi da umman bashir.da qyar ahj babba

ya kashe wutan,abba da ya dawo yaji hayani ma

mahaifanshi sai ya qara barin layin sai can sha

daya na dare ya dawo ya kwanta,ranan ko abinci

bai ci ba.da safe yana gaban umman shi yana

fada mata kalaman da umman bashir ta masa

jiya,una ta ce ashsha,kai banji dadin wannan

kalaman na sahusa gare ka ba.saidai na gode

daka nemi yafiyanta,sannan ka kiyaye duk abinda

xaisa tayi maka munmunan furuci.dan bakinta

dafine a gareka.kada kaga cewan baka yimata

komai ba,to intayi ma mugun furuci sai

kamaka.yace xan kula,tace yauwa abba.saka

makon binci ke da mahaifin bishira yasa amishi

iri daya da wanda sirikinshi ibrahim yayi

mishi,ma’ana halayan kirki da mutuncin iyayanshi

da shi kanshi yaran.duk dadai ance masa ba

wasu masu hali bane?sai rufin asiri da suke da

shi.wannan bai dameshi ba tunda dai ance mashi

yaran yana neman na kanshi,sannan yana karatu.

to tunda tana sanshi ba ruwan shi. ya kira wayan

cikin gida ya kira hjy sai yaji sallamanta ta turo

qofa.yace yauwa dama ke xan kira.ta dire tire

mai dauke da kayan shayi akai,sannan ta xauna

tana gaishe shi. Ya amsa sannan yace ina jin

gobe masu neman auran bishira zasu je wajen

yaya a jakara. Hajiya zainu ta gyara zama,”ka ce,

bishira ko Aisha? ya ce bishira dai tayi yar dariya

yaushe bishira tayi saurayin da har zai turo? ya

ce,”a’a ba ki sani ba? ta ce,”na dai ji yanzun” ya

ce to na basu izinin turawa tun jiya tunda tana

sonshi babu ruwana da doguwar soyayyar nan

kin sani Hajiya zainu ta hade rai,”amma kana

sane da cewa ss2 zata je ko? ina laifin ta gama

sakandare? Tace ,”gaskiya ranka ya dade ka bar

batun auran bishira.” ya dubeta,”kada ki damu

kanki fa.don kin san ba zan canza ba” ta bata

rai,to dan wanene? shima ya daure fuska dan

babanshine.ta mike a fusace ta fita sai dakin su

bishira. Lokacin suka farka daga baccin da suka

koma bayan sallar asubahi.ta ce,”ke bishira,ke ce

kika turo saurayinki gurin dadynku? wai yaushe

ma kika yi saurayin? Aisha tayi zaraf tace, momy

kin ma san wanene? hajiya zainu ta ce,”wanene?”

Aisha ta ce telanmu Abba din nan.” Hajiya zainu

ta saka salati Abba tela? tela fa? Aisha ta

ce,”tela kuwa” hajiya zainu ta isa gurin bishira ta

rike mata kunne. “kece kika zabi auran tela? me

ya ci shi kansa bare ya baki? zai iya da

karatunki? wallahi tun wuri kije ki fada ma

dadynku bakya sonshi.” Bishira ta ce,”nifa shi

nake so momy.”hajiya zainu ta rufeta da duka.

washe gari su Alhaji babba da abokinsa Alhaji

sani,sai makocinsu malam ma’aru suka je

nemawa Abba auran bishira a jakara gidan Alhaji

musa wan mahaifin bishira. an amshesu hannu

biyu,sunyi magana ta fahimta an basu,kuma sun

karba.an yanka sadaki da dukiyar aure,sannan

sunce suna so za’a hada da yarta. Su Alhaji suna

ta godiya nan dai gemu da gemu suka rabu cikin

mutumta juna. Hajiya zainu ta dauki karan tsana

ta dora ma bishira,tunda tayi-tayi cewa ta janye

batun auran Abba taki,ta ce to bazan miki komai

ba.sannan in babu ta sameki kada ki ce kin

sanni,in ki ka zo nan gidan da sunan neman

taimako saina wulakanta ki. Duk bishira dai ta

yarda,nan aka sa rana kusan wata shida. Abba

ya iso kofar shagonsu da sauri don hangen da

yayi gurin ya cika da jama’a,yana zuwa sai yaga

ashe ummi ce tazo wucewa ta taba wani shagon

fale-fale ta taba sai yayi mata shocking. shikenan

ta tsaya tana jiran wa zai zo tasa shima ya

taba,can sai ga wani yaro,tace kai ka iya karatu?

yaron ya ce,”eh” ta ce karya kake in da gaske ne

nuna mun acan.da gudu yaro yaje ya dangwala

dan yatsa a kan A sai ko shocking ya debe shi ya

jefa kwata. Ashe yayan yaron na kallonta sai ko

ya biyota shine ta fallo da gudu ta fada

shagon,shi kuma y ce sai ya duketa. Abba ya

kalleta kallon tsana ya ce,”fito shegiya ya

hankado ma yaron ita ya ce ka mata dukan tsiya

yaron ya ce na hakura ta ci darajarka Abba ya ce

don Allah ka duketa,don wannan bata da wani

amfani daya wuce duka. yaron ya ce,ku dai ku ja

mata kunne don kar taje tasa dan wani a

matsala,ko ma ya rasa ransa,domin shocking zai

yi kisa nan da nan. Abba ya ce dama zai kasheta

ai da munyi murna.ummi ta kalleshi a ranta ta ce

sai kazo ka kashe ni. Bayan kowa ya watse na

nan yasata tsalle kwado. Ahmad abokin shi ya

shigo shagon ya ganta tana ta tsallen kwado ya

ce a’a Abba meye naka nasa mace irin wannan

horon? Abba ya ce kasan Allah da ace yarinyar

nan namiji ce da tuni na zuga an kaita gidan

horon yara,kaini da in kayi kisan kai babu laifi da

sai na ba yarinyar nan gamalan 20 tasha ta

mutu. Ummi cikin kasa-kasa da murya ta ce

nima da zaka mutu a dadina. Ahmad ya ce haba

Abba ya kake irin wannan maganar? ya dubi

ummi tashi ki tafi abinki.ummi taki tashi don

tasan in don Abba ne sai ta tashi ya ce ta sake

sabon lale don haka sai ta ci gaba da tsallan

kwadonta. kuma bata nuna kasalarta domin ya ce

sai taji jiki tukunna zai barta. wannan ya shigo ya

ce Allah sarki ai mata hakuri wannan ya shigo ya

ce don Allah a kyaleta.sai kurum ta saka kuka. da

kyar Ahmad ya shawo kansa har ya ce ta tashi

ta tafi.ya ce kuma inta yarda yazo gida ya samu

tayi wani laifim shi da ita ne.daf da magrib yana

sauri za shi masallaci sai ya ganta da dan tasi

tana kasa shi kuma yana tuko motar a hankali

yana ce mata an kusa gidan tana cewa eh. bata

lura da Abba ba saida ya ce ke ina zaki? da sauri

ta fice da gudu dan tasi yace ke yarinya zo nan.

Abba ya matsa gurin shi ya ce malam lafiya? dan

tasi ya ce yarinyar can ce ta taro ni tun daga

bakin titi.wai an aikota ta kira dan tasi za’a dauki

kaya zuwa wambai. nan na dibo fasinjan cikin

gari ne ma sauke su tare da basu hakuri,to da

mukazo hanya sai tace mun jaki ne za’a dauka

nace jakin lafiya? ya ya za’a iya saka jaki a tasi?

ta ce mun ita dai tashi aka ce mata ta taro,kuma

nayi-nayi ta shigo motar taki. Abba ya ce,kayi

hakuri karya takeyi,kanwata ce.wallahi bata ji.

dan tasi cikin takaici gashi ya sauke fasinjanshi

yajuya ya tafI. Abba ya nufi masallaci yana

kyalkyata dariya.don shi lamarin ummi tsoro ma

ya soma bashi jaki a tasi.kai shima dan tasin

mashiririce ne.banda haka tunda ta furta jaki ai

sai ya kama gabansa. yau bai ma bi ta kanta

ba.don yana sauri yaje gurin masoyiyar sa

bishira. Ummi ta shiga ajinsu na makaranta.kai

tsaye ta nufi kujerarta wadda babu wata yarinyar

data isa ta zauna duk ajin don suna matukar

tsoron ummi. Tun daga lokacin data bigi kirji ta

ce kujerarta ce,kowa ya sallama mata.malamai

ma da suka gaji da rabon fada cewa suka yi a

bar mata kujerar. duk makarantar babu wanda

bai san ummi ba,malamai da dalibai saboda

yawan fadanta da tsokana,har malamai bata bari

ba a tsokana. sun fita fitsari ita da kawarta

Amina,kafin su dawo malamin (social studies)ya

shigo. Amina ta ce ummi dubi har malamin(social

studies)din ya shigo. ummi ta ce,”ina ruwana,ko

wanene ma ni shiga zanyi abuna.”Amina ta ce,”in

dai tica hassan ne gara mun juya don sai ya zane

mu.” ummi ta ce,”tab ai gara dukanshi da in tafi

gida yanxun wannan mugun yaya Abban ya ci

zalina.” sam ummi bata kalli malamin ba,sanda

take takai kujerarta,yayinda Amina ta labe ta

kasa shigowa,kamar cikin mafarki taji muryarshi y

ce,”ke daga ina ki ke?” ta dubi gurin da

sauri,”yaya Abba ne ya hade rai,fuskar nan tashi

babu annuri sai kace mai bada mugun labari. ta

tsorata matuka,ya ce” zo nan kiyi ‘kneel down’.”

jiki na bari ummi taje ta zube gaban allon.nan

take yayi mata bulala guda goma masu kyau.

take yan ajin suka shiga taitayinsu,don sunga

ummi tsiga tana kuka irin wanda bata taba yinsa

ba.don ko an duketa daurewa takeyi ta kuma

shanye dukan. sannan sabon malami dan bautar

kasa kamar yadda ya gabatar musu da Kansa

daga zuwa yayi wannan duka.lalle dole su

tsorata. ya ce,wuce ki zauna dakikiya mai idon

jaki.wannan kalma ta daga hankalin ummi,domin

taga yan ajin sun guntse dariya. ummi ta koma

kamar ruwa ya cinyeta a cikin ajin duk tsokanarta

ta tsiya,tsunguli wancan,shuri wancan,duk an

samu saukinta. taimako daya Allah yayi mata,duk

da halinta ta da kan daukar karatu.a zaton Abba

bata iya komai ba,tun da basa shiri. don haka

baya ko duba takardunta,islamiya ne yafi tsarata

don tashi hikimar fannin addininta ne dole a

matsa mata ta sani,boko kuma in bata yi ba ta

yiwa kanta. duk rubutun da Abba yayi ummi yake

ta dawowa ya ce ta karanta shi in ko ta mike sai

ta karanta shi tsaf.in da ta dan samu saukin shi

kenan. tun daga wannan ranar ummi alkadarinta

ya soma karyewa gurin yan ajin,domin in suna

fada shh da yazo ba bin ba’asi ita yake horawa.

sannan in ta duki wani kafin ya shigo.daya shigo

za’a fada mishi,don shine ya basu damar cewa

duk wanda ta taba in yazo a fada mishi. duk da

sun gano kanwar shi ce,gashi kuma wani lokaci

tsokanarta suke tunda ya ce mata ummi mai idon

jaki. sam bataji dadin zuwan Abba ba amma

tasha alwashin itama sai ta mishi abinda zaiji

bakin ciki kwatankwacin yadda taji. wata rana

Abba ya siyo wayar sadarwa, lokacin tana farkon

fitowa,yazo da ita gidan yana nuna ma su umma.

nan akayi ta mishi murna umma ta ce,”kai

Abba,kai da zancen aurenka ke karatowa ina kai

ina siyan wannan abar har kusan dubu ashirin ka

ce?” Yace umma amfani kai,kema xan sai miki ai

tunda nan gaba kadan xata sakko.ahj babba dai

yace xaya bani kudi in sayo musu shida ahj

qarami.ummi na wanke wanke tana kallan

su,wayar ta birgeta,irin wanda suke gani a cikin

fina finan indiya, ta xata yan sanda ne kawai

suke riqe irin wannan wayoyin.kai ko na bakin

titin nan da take ganin mutane na bugawa birgeta

yake yi,har ta tuna ranan da sukayi doguwan

tafiya sukaje phone book.suna xuwa suka tarad

ana layi,haka suka koma gyefe saida kowa ya

gama sannan suka shiga sunata latsa latsan

nanbobi suna karawa a kunne.saida wani mutun

yaxo ya kore su,bayan ya dundungure masu kai.

tayi murmushi, sannantace a ranta, allah yasa ya

sai ma umman su,ita ko ta samu abin latsawa.

daya nunama tsohuwa wayan tace shirman

banxa,inba qarya ba da wannan xaka kira wani

daga nesa?yace kn da a saudiyya kike xan kira

ki.ta ja tsaki tayi daki shiko ya fice nana

dariya.cikin satin ahj babba ya ba abba ya hada

masu waya da layi,ahj babba yafi kowa murna da

wayan, saboda shi mata fiyine. Wata safiya abba

ya shiga wanka, umma na kicin tana soya masu

dankalin hausa. zirif ta shige dakin abba tanata

danna danne,da taji motsin bayi sai ta aje ta yi

waje da gudu.saida ta tabbata ya shiga daki sai

tayi xirif da shige gida.lkc da taxo kawo mai abin

kari tasame shi yanata danna wayan,ya dubeta

kinxo kin tabamin waya ko?da sauri tace a,a.yace

munafuka,kece gashi kinyi min delete din duk

numbers din dake cikin wayan, muguwa. tace to

ni na shigone?ya harare ta yace fita, da ace ban

rubuta lambobin na aje ba da yanxun kin min

asara, muguwa kawai. ummi ta fita tana dariyan

mugunta,domin in da abin da tafi so bai wuce

taga bacin ran abba ba,kamar yadda tayi imani

shima burinsa kenan. umma ta lakato man xafi

tana shafama ahj a qafa tana murxawa.yace

yauwa suwaiba kamar kinsan tun daxu yakemin

kwankwatsa.daxidariya tace in dan tamu ne

kariqa ware ranaku biyu a sati kana hutawa.yayi

yar dariya,ina wani hutu da xanyi a gidan

nan,matsalar ummina kadai ta ishe ni.umma tayi

dariya,sannan tace ai ummi sai addu;a Ta canya

xancan da cewa,af na manta niko yanxu auran

abba yayi wata hudu nangaba?ya ce hudu ne da

yan kwanaki.tace tofa!gashi ni uwarsa banida ko

kobo,bari naxo na kama sana’a. ya tuntsure da

dariya,sannan yace sai yanxu kika san da

sana’a?itama dariyan tayi tace, in ba haka ba ahj

ranar biki ko an kirani bana amsa ba.yace gashi

kuma ke xaki mishi lefe.tace,to na shiga

aljihunka,in yaso in an soma sana’a sai in biya

ka.yasa hannu ya dago fuskanta yace sannu

sarkin wayau.suka sa dariya.yace in san muje

yaga gidajen nan na layin gabanmu,sai ya xaba

guda daya a baiwa masu hayar notice sai a gyara

shi.tace ya xabi na farkon layin dan yafi

kxau.yace amma bashida girma.tace ya ishe shi

daga shi sai matarsa fa?wanda ke cikin gidan ba

mata bixu ne dashi ba?yace to xamuje dai ya

xaba.sannan akoma kan lefe,tace allah ya saka

da alkairi,allah ya kaimu.yace amin.wayanshi

dake caji ta soma ruri,yace dauko min wayar

can.ta miqe tana cewa har naji tsoro,na kasa

sabawa da wayan nan.yace kuma gashi na kusa

bar maki ita. tayi dariyan jin dadi,tana

kallanshi.to ni wama xai dinga kirana?yace ni

mana,bana iya yi miki wata magana in na kira

abba na ce ya kawo maki,sai inga kamar yana

tsaye,inko taki ce dana kira sai ki kebe daga

jama’a muyi hiranmu. tayi dariya, daidai lkcn da

kiran ya sake shigowa,ya daga. ahj buhari ne

wanda ke sarin kaya gun shi daga kaduna.suka

gaisa yace ahj ka kira kan in dauka ta katse.ahj

buhari yace,dama ina san ince maka ne dan allah

gobe xan shigo,kasa ahada min kayan nan da

wuri.yace ba komai xa a hada.bayan sunyi

sallama umma tace ni abin da yake bani al’ajabi

da wayan nan, har kullum yanda xaka kira wani

daga nisan duniya,kuma kuyi xance radau.ahj

yace ci gaba kenan,wata rana ma sai kinga

fasahan data ninka wannan.tace haka ne.abba

yana xaune gaban ahj da safe bayan sun

gaisai,sai ahj yace abba ina ganin da yamma ko

xuwa dare kaje ka duba gidajen nan ka xabi

guda,saboda a ba su notice dan a gyara

didan.yace ahj ba sai naje ba duk wanda aka bani

yayi.ahj yace ummanka tace ka xabi na farkon

layin. cikin murmushi abba yace,ta shi

kenan,nima shina xaba domin duk abinda umma

ta xaba min shine xabina. tuni sahura ta fito da

anko,xaqewanta da nuna isarta akan bikin sai

kace ba dan fari ba. duk dangi sai surutunta ake

yi,har danginta.umma kan cewa tayi anko ba

shine damuwanta ba,dan haka sam bata bi ta

kansu ba.abba a cikin ajin da yake koyarwa,ummi

tana 2n gefe in da yayi mata maxauni a qasa,can

in da ba knwa sakamakon ganowa da yayi in tana

ajin ba a xaman lafiya,sannan babu me ikon xama

a kujeranta.yace,in ma ya sake ganinta ko a wace

kujera ce bas,xai ballata.rubutunda yayi take yi

ranta bace.ya kalli gun datake yace ke!ta dago ta

dube shi,yace xo nan.taje yace,amso min bulala

acan ajin.kafin ta dawo sai da ta duke wata

yarinya ta rugo.nan kuwa yarinyan ta biyo ta har

aji,abba kam daya amshi bulalar saida ya xaneta

tas.sam abba ya sama uni ido ko ta ina,ba

makaranta ba, ba gida ba.dan haka ta matsu yayi

aure ya bar gidan sannan ya gama service dan

shi ya qara gaba. tabbas lkcn auran sa xata yi

party.RFIN CIKI book 1 part 6

ZURFIN CIKI book 1 part 6

Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 21:56

Tabbas lkcn auran sa xata yi party. Ummi party

xatayi na murnan barin gidan shi.ahj ya ba umma

wayarshi kamar yadda ya fada mata,ya ba abba

ya suya mata layin mtn kamar yadda ya fada

mata.ummi tafi kowa murna da wannan

wayan,domin in umma ta aje takan dauka tayi ta

latse latse,har dai ta iya abubuwa a wayan

saboda ta iya karatu.kwanci tashi bikin abba ya

rage saura yan kwanaki.duk gida biyun sai shirya

shirye suke,mu samman gidan amare saboda yan

mata biyu xasu auran.gidansu abba tuni ahj yasa

an masu fantin gidan biyun,gidan ango kuwa ya

sha gyara da fenti.ahj ya sabunta mishi qofofi da

wundunan gidan, batun lefe kam dama tuni ya ke

sayen xannuwanshi da kadan da kadan yana

kawo ma umma tana adanawa.dan haka ahj

karami yana kawo akwatuna umma ta fito da

kayan dan tasan me xa a qaro.sannan ya yaba

da hankalin abba.wannan ya nuna mishi cewa

abba xai iya riqe gidanshi.lalle sana’an hannu

tana da amfanh ga yayanmu a wannan xamanin

namu.umma tai mashi lissafin sauran abubuwan

da xannuwa da leshi xuwa shadda,tace ahj dan

allah adubo mana masu tsada, Ahj yace suwaiba

xan yi daidai qarfina,ba xan yi qarya ba dan sun

san cewa dana talaka ne,kuma suka ba shi.umma

tace,sai batun abin da xa a ci.yace suwaiba

kenan,saunawa xakimin lissafin kayan abincin?na

xata ma xakice kayan sawanku?umma tace suma

a kawo mana da wuri dan mu dhnka da wuri,ba

abba xan ba c saboda harkokin sun masa

yawa.saura sati uku biki aka kai lefe.hjy xainu dai

unguwa ma ta tafi a ranar,danginta na maigidan

su ne suka amsa.sai yatsina suke tare da raina

kayan da suka duba ma sai um da um suke

cewa,wata tace to an gode fa,tunda taji ta gani

mu menene namu?suka ba da tukuici, nan dai

yan kai lefe suka dawo jiki babu qarfi.koda suka

dawo suka sanar da umma sai tace ku qyale

su.mu dai mun yi daidai qarfinmu.umman bashir

kuwa da qannanta suka kai mata labari cewa,tayi

ina ko xa suyi maraba da kaya?suwaiba ta karbe

mishi kudi bada xuba kayan kirki ba,banga

laifinsu ba.ummi kam sai dibar ma umma kayan

abinci take a boye tana kaiwa gidan maman iman

maqotansu ne,matan suna shiri da ummi, don ita

rayuwar ummi dariya take bata,ta gwado shinkafa

ta kawo,taliya,ta tsiyayo mai,ta ce sauran kayan

miya da magi,har nama debowa zanyi. maman

imam ta ce lallai kawayenki zasu sha party.

ummi ta ce tab ai dole inyi party zan rabu da

alakakai sarkin mugancin duniya. maman imam

ta saka dariya,ummi ta kuma fita da gudu tana

fadina na tuna inda gishiri da maggi suke. daga

gidan amare anzo anga gidan amarya,nan ma sun

tafi suna mita,fadi suke “bishira batayi sa’ar miji

ba,wata ta ce ya aureta ne don kudin ubanta.

koda suka je suka fada ma hajiya zainu fasalin

gidan,daki uku ne duka falle dai dai sai kicin da

bayi a tsakar gida. kanwar zainu ta ce,”kai

gaskiya bishira bata yi dabara ba.hashimu dan

gidan Alhaji mansur ya jima da sanar dani ya

kamun bishira.” hajiya zainu ta ce,”shi kadai?ko

yayan abokan babansu nawa ke sonta?tunda taki

tsayawa tayi karatu ta zabi ta auri tela,ba shi

kenan ba?dubi gidan ubanta amma ta zabi zama

a wani gida dakuna jere sai ka ce ajin

primary.”lol. suka ce,”kwarai kuwa kamar ajin

makarantar gwamnati.”ta ce,”shi kenan ai kaya

dai asai mata daidai tsarin gidanta ba iri daya za

a sai musu da Aisha ba.” sun siyo sunje sun jera

komai ras,yanzun kam sai daura aure ya

rage,Abba da abokanansa walima kadai ya shirya.

can gidan ne suke ta bukukuwansu irin ma masu

hali.shi kam dai yasan yan’uwanta ba sonshi

suke ba. sam be je gurin shagalinsu ba. ranar

lahadi aka daura aure,misalin karfe goma na

safe,unguwar kam ta cika da mutane da motoci.

Abba da zugar abokananshi salisu yayan amare

yayi musu jagora cikin gidan. sun gaisa da

mutane sannan suka fito kowa fadi yake.”kai

amma angon bishira zankadede dashi

tubarkalla.”gashi Abba da iya daukar

wanka,tsafta ce dashi ga son kamshi. KAI MATA

IYAYEN GULMA. Can gidan ango ma anata

shagalin cin abinci, jama’a dangi da makota sa

gudunmawa suke ba umma tana a’a amma sai

ace ta rike sabida ita mutum ce mai kyauta.

umman bashir kam sai takaici take ji,kowa ya

shigo sai dai ya ce mata.”Allah ya sanya

alkairi”kawai musamman ta shigo gidan don taga

ko ana ba umman Abba ne. Nan fa na fita ta

koma gida babu ko kunya tana ta masifa, fadi

take “lallai suwaiba,gudunmawar auran dana duk

ita ce ke karbewa? gaskiya naga sai dai amin

Allah sanya alheri a wuce,to da sake,ni na haifi

abuna ta bari sai ta tashi auran wannan

figaggyar yar tata sannan ta amshi bikin.” ta

gama fadanta ta matsa,danginta suka soma yi da

ita,suka ce wa zai baki wani abu ke da ko dan

uwanki baki san ki bashi gudunmawa ba bare

kyauta.tsinanni yar rowarki ce taja miki.”

kanwarta ta ce,”sahura sai dai ta ci na wani ba

dai aci nata ba,dama irinsu sun cika son banza.”

ummi kam anci kwalliya an gayyato kawaye

anata party a gidan maman iman,an kunna rediyo

sai rawa suke yi,kafin a gama partyn an bige da

fada da dambe,da kyar aka rabasu,nan taro ya

watse. da misalin karfe takwas na dare,ango da

abokanshi sun taso sallar isha’i Ahmad ya ce don

Allah ango muje mu rakaka. ya ce,”Allah sai nayi

wanka.”mukhtara ya ce,”gidan cunkus da jama’a

zakayi wanka?” Aminu ya ce,”don Allah malam

kazo mu tafi,in ma kifi zaka zama a gidanka.”

Abba ya ce,”bari dai ku gani.” a zaure suka ci

karo da ummi,ya ce,”ke jeki ki wanke bayi ki kai

mun ruwan wanka.” ta sobare baki ta koma ciki

tana fadin. na dai kusan hutawa, masifaff. ta

wanke bayin sannan takai ruwan,yana shiga gidan

dangi sukayo kanshi,ga ango! ga ango!! abokan

wasa suka za na can zamfara suna tayi masa

tsiya. dan gidan ummanshi yau dai za a kwana

wani gidan ba na umman tashi ba.ya dai samu

ya shige wanka. bayan ya fito ya bude

dakinshi,ya shirya cikin wata shadda

mirror,lokacin su ake yayi.ruwan kasa mai duhu.

yasha hula mu hadu a banki ita ma kalar

shaddar,ya feshe jikinshi da kalolin turaruka.ya

shigo cikin gidan yaje kofar dakin umma. ya ce

umman tana nan.aka ce mishi tana dakin

Alhaji,yayi sallama a kofar falon Alhajin basu ji

ba,suna ta hira tsit ya yi lokacin da yaji umman

tana cewa Allah dai ya basu zaman lafiya da

zuri’a tagari. Amma har ga Allah naso Abba ya

auri….. ringing din wayar shi ce ta hana jin kowa

ummanshi ta ce,sai dai muryar Alhajin ya ce

wallahi suwaiba nima tsarina kenan. ahj yace ta

allah ya riga ya shirya ba ita ce matarshi ba.ya

daga wayar,ahmad ina xuwa mana. ba tare da

yaji abinda ahmad din xai fada ba ya katse

kiran,dan yaji haushi.yaso jin wacece iyayansa

suka so ya aura?ya sake doka sallama,suka

amsa.ya shiga ya xauna ya gaishesu,sannanya

dubi umma.dama naxo miki sai da safe ne.ahj da

umma suka yi yar dariya,umma tace to

abba,yanxu dai ka girma,dan allah kyawawan

halayenka dinnan kaci gaba da su.yace na

gode.ahj ma yayi masa nasiha,daga nan ya fita

jikinshi a sanyaye.da muwarsa me yasa umma

bata sanar da shi yarinyar da taso mishi ba

tuntuni?haka dai suka rankaya da abokanansa

dan xuwa dakin amarya. gidan kam tun daga

tsakar gida qamshi ke tashi.sun taradda

qawayenta biyu,ita kam tana lullube kan

gado.nan dai suka sayi baki akayi yan shaqiyanci

tare da barkwanci,sannan qawaye suka yi mata

sallama suka tafi,shima ya raka abokansa. ya

dawo ya xauna bakin gadan yana dubanta, itama

kallonshi take cike da so. sukayi ma juna

murmushi,ya janyo ledan kaxan da suka shigo da

ita. Ya warware takardar,y yago cinya ya mika

mata a baki,”ci,nasan yau kin wuni da yunwa

ko?” ta ce,”na koshi bana jin yunwa ma,ni kam

duk yau banji yunwa ba.” ya ce,”ni ma haka,dama

yau bai da ce muci abinci ba.”ta dube shi da

alamar tambaya a kwayar idanunta.ya ware

idanunshi. “taron da muka tara ko ina cike da

jama’a.” yayi yar dariya sannnan ta bude baki ya

saka mata kazar.ta dan figa.haka yayi ta bata

tare da zuba mata juice a kofi shima yana bata.

ta ce,”to kaima ka ci.” ya ce,nima ke zaki

bani.”ta sunkuyar da kai don kunya sannan ta

dauka ita ma ta soma bashi. sai da suka yi

dam.sannan ya ce mata kije kiyi alwala kizo muyi

sallah. ta ce ai tun dazun nayi sallah.ya ce

wannan ta ma’aurata ce,zamu gode wa Allah

taare da rokonshi zuri’a tagari,da kuma fatan ya

tsare mu daga sharrin shaidan dama duk abin ki.

Ta fita ta dauro alwala,shi kuma ya kuskure

baki.shine yaja su sallar,raka’a biu sannan sukayi

ta addu’a,shi ne ma yake addu’ar ita kuma tana

cewa amin. bayan sun idar da sallah idar da

sallar,ya yi mata tambayoyi game da addini ta

sanar da shi,yayi mata yan gyare-gyare sannan

suka kwanta. sam Abba be daga kafa ba,a ranar

ya angwance abin shi.don haka yayi kwanan farin

ciki. da asubahi ya dawo masallaci,har lokacin

amarya tana ta shirga bacci ya zauna bakin

gadon yana kallonta.yasa hannunshi a gefen

kumatunta. “sleeping beauty” tayi mika sannan ta

bude ido,ya ce”a tashi ayi sallah ko?gashi sai

kinyi wanka ko?” ta ce,”eh.” ya ce, “to tashi ki

gani gari ya soma haske.” zani taja ta daura

daura ta nufi waje. da kallo tabi tsakar

gidan,sannan ta dawo dakin Abba.bazan iya jan

ruwa daga cikin rijiya ba. ya fito da sauri yaja

mata sannan yakai mata bandakin,ya dawo yayi

taja yana cika robobin ruwanta.sai da ya cika

mata komai,sannan ya koma dakin. lokacin ta

idar da sallah.ya dauko Alqur’ani mai girma ya

zauna gabanta,ya ce “madam zamuyi karatu.” ta

dube shi tareda yatsina fuska,”wallahi bacci

nakeji.”ya ce,”daure muyi ko aya biyar ce,” ta ce

cikin shagwaba,”ni biyu.” ya ce,”to bismillah,mu

fara ta sama ko ta kasa?” ta ce,”ni kam ko ta

ina, don haka sai ya soma mata daga bakara

yana yi tana maimaitawa,aya biyu kusan minti

ashirin ta ce, “zan kwanta.” Ya aje kur’ani ya

kmama hannunta,zo muje kicin mu gani me zamu

nema.dan dole ta bishi zuwa kicin din.suka tsaya

suna kallm kayan, tukwane ne zuwa kuloli da

sauran tarkace,sai risho.ta dube shi cikin yanayin

tsausaya ma kanta. tace, sun qi sai min gas

cooker wai gidana ba flate ba ne bai dace da gas

cooker ba. ita ko anti aisha an sai mata, kayan

girkita ma duk yan chaina. tausayinta ya tsirga

ma abba, ya jawo ta jikinshi ya rungume, kada ki

damu bishira, duk abin da a ke sai ma yar gata

xan sai miki, matsawar Allah ya hore min. ya

janyo kwalin risho din ya ciro shi, ya hada yace

xan siyo lagwani da kalanxir kenan ko? tace eh.

ya miqe bari na dawo. tace to. ta nufi daki ta

fada kan gadanta taci gaba da baccinta, shi kam

gidansu ya nufa. tun daga nesa ya hango ahj

babba xai shiga dakin waje, in da aka sauki baqi

maxa, da alama ahjn ya hango shine shi yasa ya

tsaya a bakin qofar. abba yana cike da fara’a ya

rusuna xai gaida ahj shi kuma ya miqa masa

hannu, dan haka sai abban ya kama suka yi

musabaha. ahj yace Alhamdulillahi abbana, ka

xama mutun, sai ayi ta hakuri da rayuwa. abba

ya sunkuyar da kai yana tambayar kanshi ko

manya suna ganewa ne in kayi auratayya da

matanka? ahj ya katse shi da cewa, ya kwanan

iyalin taka? tare suka shiga gun baqin, yana

gaida su ya fito xuwa cikin gidan. yana leqawa

dakin umma bata ciki, sai baqi. wata uwani dake

matsayin abokiyan wasansu tace ango amarya ta

koro ka ne? yace, keni karki dame ni, ina umma

na? umma daga kicin tace, gani nan dana, xo

qyale su uwani. gurinta ya nufa yana cewa,kina

kicin ashe? tace, eh ina hada ma baqi abin kari

ne. yace kalli yanda duk suka yi mana kaca kaca

da gidan,wannan in sun tafi sai kin sha aikin

tsaftace gidan.tace to yana iya?dole in gyara in

sun tafi,ai arxiki ne ma xuwan nasu.abba yayi

dan murmushi,sannanya canxa maganan da

cewa,umma galan din kananxir muke so.tace,ga

ma kananxir din can da ahj ya siyo jarka babba

wai saboda biki.nace yaushe girkin biki xai yiwu

da kananxir?shine na aje shi.sai kadau galan ka

cika.yayi murmushi. Yace kai ahj akwai qoqari,

musamman lkcn bikin nan.umma tayi yar dariya

tare da cewa ko abinci fa baya iya tsayawa

yaci,in na masa magana sai yace bijin da guda

ina yaga ta cin abinci?abba ya girgixa kai,Allah

ya rama muku da mafificin alkairin da kuke

min,yasa ni ma in goya ku kamar yadda kuka

goya ni.tace amin abba ai muma kana yi mana

biyayya Allah yasa albarka a cikin auran, ya baka

yaya masu binka kaima.yace amin. ya isa gida da

kalanxir da lakwani ya samu ta koma bacci,dan

haka ya hada ya dora ruwan xafi ya juye cikin

plaks yaje ya ce ta shi mu karya. tayi juyi tare da

cewa sai an jima,dama tun jiya sun shigo da

biredi da kayan tea,shima sai ya sake

kwanciya.ya mannata jikinshi suka koma

bacci,goma da ishirin wayarsa ta tashe shi da

ruri. ya daga ahj ne ke san ganinsa qarfe sha

biyu.yace,ya sanme shi can kasuwa,ita ma ta

tashi.nan suka karya sannan yayo wanka ya tafi

kiran abba.kaya ne ya ba shi da kudin mota, yace

ya kawo ma baqi yan xamfara da xasu koma gida

yace ka tabbata ka dauki shatar mota har

Zamfara abba ya ce to.sai da ya samu motar

sannan yaje ya loda su suka daga,suna ta

godiya.yau satinsu daya cir umman shi ke kai

masu abinci,sannan ita kuma ya shigo da kayan

marmari,sai kaji ko tsire da balango.abba ya

shirya tsaf cikin qananan kaya xai tafi shago,yace

madam yau fa abinci xaki yi mana,kin san

abokaina su ahmad xasu xo muci abinci,in yaso

daga nan sai mu wuce gaisuwan surukai gidanku

a matsayin kina amarya wanda xaki soma girki

yau, me xaki dafa mana? ta tashi xaune duk abin

da ka ke so.dadi ya rufe shi,kowanne dai ki mana

fatana shine ki birge abokaina.tace an gama.

yace to bari inje xan turo yaran shago da abinci

da cefane tace to, har ya tafi kuma ya dawo

yace, xan biya in turo miki ummi,tace saidai in

fati.yace,ummi tafi fati hanxarin aiki fa.tace eh

nafi son fatin.kamar kullum sai da ya soma shiga

gun ummarshi suka gaisa ta tambaye bishira,

yace lafiyi lau.yaci gaba da cewa, yau nema xata

soma girki,nace na turo mata ummi tace wai

fati.umma tayi murmushi, sannantace kai ko

yaushe xata so a tura mata ummi umma tace ina

xata so a tura mata ummi? ita fa ba natsuwa

gareta ba.abba yace, duk da haka tafi fati

hanxarin aiki. umma tace,yanxu dai tura mata

fatin.ka ko sai kayan abinci?yace ina fa,yanxu dai

xan je bin wasu yan kudadena.tace ina xuwa

baqar leda ta ciro a cikin adakan suturunta,taxo

ta xauna sannan ta umurce shi da ya xauna.ta

miqa mashi ledan tace,kwance ka gani.abba ya

kwance ledan yana cewa menene a ciki ummana?

kudin da yayi arba da su su suka bashi amsa

yace,umma kudin nan fa?tace gudunmawa ce da

jama’a sukayi ta bani,ka gansu nan.yanxu ka je

ka siyi kayan abinci da su.abba yayi dariya,

sannan ya kullesu ya miqa mata tare da cewa.

Allah ya kyauta in amsan makh kudi, ki boye

abinki. tace bana son muyi ta jan magana

abba,kawai ka riqe kudin nan.muryan tsohuwa ne

ta katse su,inda take cewa yanxu ke suwaiba

hakan da ki ka yi adalci ne? yar gudunmuwar da

ki ka samu kiba mai sunan malam duka, ummin

fa? umma tace,to tsohuwa ummi me xatayi da

kudi yanxun?abba yace kai wannan matan sa

idan ki ya gota misali. Tace kai tafi can,ni rufemin

baki,ke kuma suwaiba da kike cewan haka ba kya

siyan mata yan tukwane da kwanonin nan na yayi

maigida cika duba ne ku ke ce musu ko ci bari

kallo? umma da abba suka sa dariya,tsohuwa ta

sake jin haushi ta ce eh dole ku min dariya tunda

kema kin xama shi,ai sai kiyi ta bashi naki ne ba

nawa ba.umma tace yi haquri tsohuwa, gani nayi

nan gaba muna sa ran abba shi ne xai ma ummi

kayan dakin ma gaba daya tace,me kika ce?tab

mai sunan mlm ne xai yi wa takwara wani abin

axo a gani?shi da ya tsaneta.abba yace,in lkcn

yaxo ke kya yi ma.ta tafa hannu cikin jin

matuqan takaici ta ce,a gayawa mai xuciya ba

mai dukiya ba,dan ko xan mata.ta nufi dakinta

tana fada.umma tace,tashi abba,dauki kudin nan

kaje. yace,wallah umma bari dai in dauka tunda

kin matsa,amma ba xan amsa duka ba.ya qirga

dubu uku,tace ka qara dan kusan dubu tara ne

kudin,yace haka ma ya isa ki adana sauran.tace

shi kenan. daga nan kasuwa ya wuce,ya sai

kayan abinci.bayan ya amso wadansu kudaden

shi ya hada ya kai mata. Sannan ya yi cefanen

kayan miyan rigijif da nama ya aika yaran

shago.dama kafin ya bar layin ya shiga gun

umman bashir ya gaisheta.da tana ta bace bacen

rai,sannan da yace umma ina fati? taje xata taya

bishira aiki ne.sai ta washe baki,tan bandaki.

yace to in ta fito ki tura mata ita.ya fice

abinshi.biyu saura ya iyo gidan,tun a tsakar gidan

yake jin qamshin shinkafa.ya isa kicin din tuni ta

sauke shinkafa sai miya.yace ki xubama yaran

shagona.ya dubi fati da ke yanka latas yace,in

kin gama jamin ruwan wanka a rijiya.tace to.yana

daki yana sa kaya yaji sallamar abokanshi.da

sauri ya fito, suna ta yi masa tsiya ango kasha

gyara, munxo dibar girki. abba ya bude musu

falo,falan yaji jeran samiru abin yayi na xamanin,

ga kujeru suka xauna suna yaba dukiyar da aka

xuba cikin falon.ya fito yace bishira ta saka hijabi

taje su gaisa.ya dauki abinci ya kai musu,sannan

yasa fati takai filet da ruwan sha,shi kuma ya

koma daki dan qarasa saka kaya.a xatam shi xai

samu sunyi nisa da cin abincin amma sai me?

dukkansu su shida kowanne filet din gabansa

shaqe da abinci da nama,ga cokali a

hannunsu,amma kowannansu juya abincin

yake,yace a,a kuci mana kai muke jira ka bude da

addua.tsaki yayi, yasan halin ahmad gun

xolaya,dan haka sai yace muktar kuci abincinku,in

kun bi ta ahmad xai ta bata mana lkc.cokali ya

dauka shima ya xauna kusa da sunusi ya ce mu

ci tare.take ya yatsina fuska tare da dawo da

abincin ya xube shi kan ledar yana tande

harshansa.dan danan gishirin da ya kama masa

harshe ya ragu,cike da kunya ya dubi abokanan

nasa suna ta dariyar da suke gimtse.da farko ya

dubi sunusi,wai gishiri ka qara ne?sunusi ya

ce,qila dai gishirin nan da bakin buhu ta

xufa.muktar yace dubi gaban rigata ni da shegen

kwandayi na tura nama a baki na tauna ya qwace

saboda tsananin qarfi ya dawo ya fado min

jiki.abba ya miqe cikin damuwa ya ce bari in

maku wata miyar. ahmad yace a,a duk yunwa

muka debo, inda yaji da mai a bamu muyi maneji.

abba ya fito xuwa kicin.fati ce xaune da nata

abincin tana ta juya cokalin. Abba yace ina

bishiran?taje daki.ya daga murya ya kirata,ta

amsa sannan taxo.ya dubeta fuska a daure ke

dama ba ki iya abinci ba shi ne ki ka toxarta ni

cikin abokaina?maimakon ki fada min? tace, to ai

fati ce nace tayi miyar, danni bansan yadda a ke

yi ba. haushi ya kama shi.ya dubi fati, ke dama

baki iya komai ba kema?shashasha, gara ki koyi

girki, dan duk macen da bata iya girki ba ba mace

ba ce.ya daka mata tsawa, tashi kije gidan

ummana ki ce ta baki abinci inji ni,ni da abokaina

ne.sallamar yaron shagon shi ne ta katse shi,ya

gaishe su sannan ya ce,naxo daukan abincin.ya

dubi bishira,kina da yaji?tace,eh gashi can cikin

kwalba da ummanka ta aiko min.ya ce,xuba ma

yaran nan yaji da mai.ta ce ai akwai miyar.yace

miyar ai ta xama guba.fati ta dauko abinci cikin

kula xata fita,yace wannan fa?ba aikenki nayi ba?

tace na ummanmu ne xan tafi mata da shi,ita ce

ta ce duk abin da a ka dafa inxo mata da shi, shi

ne yaya bishira ta xuba mata.abba baice qala ba,

sai al-ajabin halin uwarshi ya ke yi. Bishira ta ce,

kawo ita ma a kwashe miyar a xuba mata mai da

yaji. ya daka ma fati tsawa,kai mata haka ni ki

dauko min abinci gun ummana, minti uku na baki

in kin wuce biyar xa ki sani.da gudu ta fita tana

shiga gidansu ta aje bata tsaya yin surutu ba, ta

fita da gudu.dan wake umma tayi,Allah yasa tayi

da yawa,dan haka ta xuba musu ta dora ma fati

ba tare da ta tambeyeta dalilin aikowarshi ba. sai

dai a ranta tana ta saqe saqe tace,qila sun fasa

girkin ne,ko kuma bai kai kayan abincin ba.koda

fati ta kai musu dan waken nan suka baje suka

kwashi dan wake suna santi.bishira tana jiyo

shewarsu.abba na cewa ummana ta iya girki, bari

in xo in sa muku waigi.muktar yace, ka kai

amaryarka ta koyo girki.garzali yace,saboda irin

wannan matsalan kafin in auri yarinya sai na

tabbata ta iya girki.ahmad ya ce daya daga cikin

illar auran yaqan masu kudin nan kenan,

sangartattu ne basu iya komai ba tun da a

gidajensu ba sasu a ke yi ba.ado yace wasu ba

amma wasu suna saka yaransu.

vels / ZURFIN CIKI book 1 part 7

ZURFIN CIKI book 1 part 7

Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 21:59

Ado yace wasu ba, amma wasu suna saka

yaransu,dan wani abokin wasanmu a kaduna ya

auri yar wani attajiri, ba kaga girki ba kala

kala.abba dai yana ta binsu da ido,har aka yi

kiran sallar la’asar suka fita xuwa masallaci,daga

can xasu wuce gaida surukai.bishirata dinga jin

haushi,wai abokan abba sunxo har gidanta sunci

mata xarafi.ummi ta fito dan xuwa gidan su

amina,domin akwai wata xainab da wai ta musu

gulma xasuje su.kirata har gida su dake ta.suna

xuwa kuwa suka tsaya a waje suna tunanin

yadda xa suyi ta fito,amina ta ce muje mu ce

mun xo gunta ne, inta xo rakiyan mu mu duke ta

mu gudu.haka kuwa suka yi,har ummarta tana ba

su quli quli,ita ga me qawayen yan tana rako su

tun daga soron gidan suka soma dukanta.sai da

ummanta ta fito sannan suka gudu.ta ce yar tata

kin san gidansu?xainab tace,na sani.ummar tata

ta taso ta.su kuwa su ummi suna fitowa sai suka

canxa hanya.amina tace dan allah muje gidan

amaryan abbanku,naji ana ta labarin jeranta an

ce kaya ne na uban gari. . Ummi ta ce,”duk da

son kirgan samirana ban taba zuwa ba,saboda na

kula ita ma yar rainin wayau ce kamar mijinta.”

Amina ta ce,”ke dai muje inga samirun da aka ce

jajaye wai masu shida-shida” ummi ta ce,”mu

fara bi ta shagonsa in yana nan to sai muje,in ko

bayanan ba zani ba ya dake ni a banza.” duk da

cewa shagon da gidan tsakaninsu da nisa sai da

sukaje suka duba sukaga yana nan,sannan suka

je. gidan shiru sunata sallama,ummi ta nufi wata

kofa ta tura,ta yafito Amina,”zoki gani nan ne

falon.”suka kirge samiru tsaf,sannan suka fito. ta

window ummi ta leka nan ta hango bishira kan

gado tana ta bacci,suka je kicin suka leka suka

tura dayan dakin da ba kowa. nan ma sukaga ba

komai ciki,an dai shimfida ledar kasa an sa

manyan robobin ruwa. suka fito,ummi ta

ce,”gaskiya matar nan banza ce,dubi yadda

mukaje tana ta bacci.” daga can suka sake zuwa

gidan wata amaryar don kirga samira,sai kusan

magariba sannan ta shiga.umma tana alwala ta

ce,”to tunkiya uwar tumbele,tun yaushe ki ka bar

gidannan sai yanzun kika waiwayo? sai kararki

da jama’a keta kawo min?to na gaji da

halinki,bari Alhaji ya dawo,wato tunda yanzu

babu Abba a gida shi yasa iskancinki ke son yafi

da.” tsohuwa ta fito,”suwaiba da a ce ba a

gabana kika haifi takwara ba,to da zance ba yarki

ba ce,ba dama yarinya ta fita wasa?” umma ta

ce,”ban hanata yin wasa ba,amma tayi shi a gida

yawo ne bashi da dadi.” tsohuwa ta ce,”a’a karki

wani fada ma Alhaji,ta daina ko takwara?” ummi

ta ce, eh.umma dan haushi ta shige daki ta barsu

anan. lokacin da su Abba suka je gidan

surukanshi an amshe su ba yabo ba fallasa,har

ma da zasu tafi aka basu (uniforms)din bishira na

boko wai ranar monday lallai ta tafi makaranta.

sun zaga gidajan danginta dake kusa,sannan

suka dawo gida.ya sameta tana fushi,shima

shareta yayi don yaji haushi barnar abincin da

tayi masa. dadin dadawa gidan nan yanda ya bar

shi haka ya tadda shi.ita kanta batayi wanka ba

ta kwanta tana ta uban bacci.fita yayi daga

gidan,sai goman dare sannan ya shigo ya rufe

gidan yaja ruwa yaje yayi wanka. sannan ya

shiga dakin,tsayawa yayi yana kallon gadon

mutsu-mutsu,sannan ga kaya nan duk a kai.ita

kuma tana kwance rike da wani littafi tana

karantawa. . Ya ce,”bishira wai me yasa bakya

son kakkabe gadonki? ta dube shi nifa duk na

gajine.tsaki yaja tare da cewa me kikayi da har

kika gaji? bani guri ni in gyara shimfidar zan

kwanta. shine ya kakkabe shimfidar sannan ya

kwanta.duk da ya cike da bukata amma haushi

ya hanashi kulata,sai ma baya da ya juya mata.

Abba yanada tsafta sosai,haka nan ma’abocin

son kamshi ne,duk da gyara gami da tsafta irin

na ummanshi wata ran har cin gyaranta yake

yi.sam baya so yaga ko ina rakwacan,yafi son

komai ya ganshi a muhallinsa. dole kullum shi ke

share gidan ya wanke ban daki,sannan da rana in

ya dawo ya dora abinci. litinin duk makaranta

suka koma daga dogon hutun kirismeti da suka

samu.Abba ya koma kan aikinsa na bautar

kasa.dan haka kusan tare suka fita da bishira ta

wuce makaranta shima ya wuce wurin koyar war

shi. . Ya rigata dawowa gidan,dan haka gajeren

wando ya samu ya shiga tsabtace gidan.sannan

ya dora dafa dukan taliya. uku da minti sha biyar

ta shigo ya dubeta ina kika tsaya? ta ce,ba ko

ina mufa makarantar mu biyu da rabi ake tashin

mu.dan ma na samu direban gidanmu da yazo

daukan kannena shine ya kawo ni. Abba y sake

had’e rai,motar gidanku? Bn baki kud’in mota

ba?Ta ce ka bani, ya ce to bn amnce ki sake

shiga motar gidanku ba. Ta ce,”kan me ? ya

harare ta ba tare d ya bata amsa ba,y nufi kicin

tabi bayanshi d harara,sannan ta shige d’aki. A

ganin Abba sam babu wani sauki da ya samu a

auranshi,nashi ganin wahala ya d’ebo ma

kanshi,kwanciyada ita ne kurum zai ce ya k’aru d

shi acikin auren. Ya shiga gidansu d

sallama,Umma ta amsa tana zaune kan sallaya

bayan ta idar d sallar Isha’i. Ta ce,Abba ba a je

an kwanta ba?ya zauna tare d d’an jan tsaki ta

ce,A’a ha,jikin ko garin? Ya ce,Umma gaskiya ni

abubuwa sun cud’e min,yarinyar nan tunda a

kawo ta sam ban huta ba. Umma ta saki dariya

“ka ji Abba d wani zance,dama ce maka a ka yi

ana bauta d hutu? Aure shi bautane. Ya ce,Tsaya

kiji fa ummata,kinga tun Asubahi in nayo Sallah

zan hau sharar gidan,in shirya in je gurin d nike

koyarwa. In dawo in dafa abnci,sannan in tafi

shago kuma don takaici in na zo kwanciya ni zan

kakka6e shimfid’a,ita bata iya komai ba ashe

daga gidan nasu.Ni fa har ta soma sure min……

“Kai Abba! Umma ta katse shi d sauri, kada in

kuma jin wannan furucin, kana hauka ne?yanzu d

fada min menene matsalarka?in dai abnci ne ka

bari zan diga aiko muku da shi. Ya ce umma ya

ya ma za a yi haka?Tab ai ba zai yi wu ba,Ta dai

zo ta koya sati d lahadi. Umma ta ce,To shi

kenan,tazo din.kayi ta hkr Abba,nasan ka kai ma

d zuciya,don Allah kada ka sake in ji wata

fitina,ka lalla6a matarka kuyi zamnku lfy. Abba

ya ce, To ko da ya sanar d Bishira cewa yana son

taje gurin ummansa ta koyo girki,sai ko ta tuma

ta ce ita ba zata je ba,dama dai gurin umman

Bashir ce, Ya ce,shi kuma gurin ummansa ya

turata,koda Asabar din tazo kin zuwa tayi,shi

kuma sai ya shareta ta ya daina girkinki. Sai dai

yaje gidn ummanshi yaci,hatta ranar litinin d suke

d makaranta bai dafa abncin ba da ya dawo a

galabaice da yunwa ta iso. Bashir ya ce, Ni har

fata nake wata rana ‘yar sa’ in’sa ta hadu ku

umma,wlh in mata shegen duka. Bishira ta ce,Ni

dai bata isa ba, in ma ita ce ta turo shi dn in

dinga zuwa gidnta to ba zanje ba. Haka suka yi

ta zagin umma,daga bisani Bishira ta mike ta tafi

dn kada ya dawo bata nan. Rashin iya girki ya

kawowa masoyan 2 rashin jutuwa,wanda ko

magana Abba bai cika yi mata ba. In ta zauna

tayi ta kuka tana mmk,me ta mishi ya juya mata

baya dan da nan? Yau kam abn ya yi kamar

kaurace mata ya yi daga dakin baccinta, ya dauki

filo ya tafi falo ya kwanta. Tayi ta kuka. Kasa

jurewa tayi ta mike ta bishi,kwankwasakofar tayi

kusan sau 3 ya ce “Waye?” cikin muryar kuka ta

ce, Ni ce, Abba don Allah ka bude. Ya kunna

wutar falon,sannan ya bude ta shigo ta zauna

kusa d shi, ta ce, Abba wai mi na maka ne ka

tsane ni? ka duba fa ko wata daya ban rufa

ba,kasan dai yadda a ka yi auranmu yanzun in

Mahaifana suka ji dariya za su Min. Amma ba

komai sai biredi ta samu ta k’asuma,d ya tafi

shago sai ta yafa mayafinta ta nufin gidn umman

bashir. koda tai sallama umman tana kan turmi

zaune suna ta ganzar rake ita d su bishir. umman

Abba ce ta aiko musu da shi don rashin Adalci

suna sha suna yi da ita. Suka shiga lale d zuwan

Bishira, ta kalli bashir ‘Ina fushi da kai, shine

wato har yanzun ba ka zo ba ko? ya ce, Tab, sau

2 ina zuwa zan shiga gidan sai yaya Abba ya fito

ya ce min kina bacci, na gane nufinshi baya son

ina shiga masa gida,shi yasa na share.Bishira ta

ce Um, wannan Yayan naka halinshi sai shi,

yanzun ma fa fushi yake dani. Umma ta ce,” A

kan Me kuma? wai shi dole sai nazo gurin

ummarshi na koyi girki, ai ko nace wlh ba ni

zuwa. Umman bishir ta rafka salati. sannan tace

‘Naga ta kaina ni Sahura,kai Allah ya isa

tsakanina d Suwaiba. yanzun kuma ta gama d ni

ke ta sako a gaba, so take ta shiga tsakaninku?’

Abba ya kura mata ido, yasan abn d ta fada

gaskiya ne ya ce “Me na miki to?” ta kalle shi,”Ba

ka ma san abn d kayi min ba?Ta ga daya yanzun

fa kaurace min kayi. Ya ce ba kya gyara

gadonki,ni kuma na gaji d gyarawa. Ta saka tafin

hannunta cikin nashi zo muje in gyara.

Tausayinta ya ji,ya tashi ya bita yana kallonta

duk kakarin d ta yi dn t gyara ta kasa. Sai dai shi

ne ya gyara, Sannan ya janyo ta suka

kwanta.Sam bata d gardama ko nuna gajiyawa a

gurin ba shi hakkinshi na kwanciya. In zai zo sau

nawa ba ya damunta,gurin da ta ke birge shi

kenan. Amma ba wannan ba ne kadai namiji ke

bukata,Musammanirin Abba dan kwalisa. Wata

ranar Jumma’a bayan sun tashi daga mkrntr da

ya ke koyarwa,ya ce da Ummi ta jira shi zaya

aike ta gida. Kudin cefane ya bata ya ce taje ta

sai kayan miya d nama ta kai gidanshi, Sannan

ta tsaya tayi masa miyar tare d yi masa sakwara.

. Shi kuma zai je ya fada ma umma, dn yana son

d dunkunan wata amarya d yake son karasawa

ummi ta zun6uri baki bayan ta amshi kudin ta

wuce tana yankun-kunai, ya ce “Ke!” ta waigo “Zo

nan . ta dawo, Ya kama mata kunne, Kin san

kwana 2 bn ta6a lafiyarki ba ko?to kiyi abn d yau

zaki gwammace ba ki zo duniya ba. ya

rankwashe mata kai, Sannan ta wuce tayi ce

fanan ta nufi gidn Matar gidn tana zaune d kayan

mkrnt a jikinta,,Ummi ta mata Sannu harara ta

zuba ma Ummi, Ummi ko ta rama,sannan ta ce

“Mijinki ya ce in zo in yi mashi sakwara d miya.

“Bishira ta ce, To sai ki koma gidn ubnki ki dauko

tukunya d murhu b dai nawa ba, Ummi ta ce, To

ni dai gaskiya d ubana ba. Bishira ta taso tana

cewa Sai na wa? Ummi ta ce, Oho,amma ba

nawa ba. Za ta kai mata duka ta goce ta ajiye

mata kayan miyan ta ce ” Gashi sai kiyi, kila ma

baki iya girki ba ne. Taje ta fadawa umma, Umma

ta ce “Ke ummi karya ki ke daga zuwa zata hauki

d zagi sai ka ce Mahaukacciya? To kije ki fada

wa Abban in ya so sai kuje tare ya fada mata

amma fa kada ki ce masa ta zage ki, ki ce masa

dai yazo ya fada mata zaki tayata. Ummi ko kyn

mkrnt ba ta cire ba ta nufi gurinshi,yana tsaka

dinki taje,Ummi sai ce masa tayi ta ce ba zam

mata girki d tukunya ba. Ya ce Muje gidn ganin

nan. “a kofar gida ta zauna tana jiranshi, sai d y

shiga sannan ta bishi. Tana tsaye tsakar gida

tana jin rigimar d suke yi.Bishira ta dage ita fa

babu mai yi mata girki d kayan aiki, shi kuma ya

ce tunda ba a koya miki girki ba a gidnku dole ne

in sa kanwata ta mini. Ta ce ya turo Fati

mana,wannan maran kunyar yarinyar mata

tarbiyya ba za ta zo mata gida ta zage ta ba.

Ran Abba ya 6aci, ya ce Ga ki nan mara

tarbiya,ina fada kina fada ina matsayin

mijinki.,Ummi tafi ki tarbiyya domin uwar d ta

bata tarbiyya ita ta bani har ki ka amince ki ka

aure Ni. Ta ce, Ta baka tarbiyya ko ta asirceka?

Ta mallake ka har baka ganin Mahaifiyarka d

gashi sai ita. Zancen ya soki Abba sosai Har ya

daga hannu zai mareta sai kuma ya fasa,ya juya

ya fita. Fatanshi Allah ya sa ummi bata ji ba,dn

yasan tsaf sai ta fada ma Umma. Tana zaune

gefen rijiya ya nufo ta,Ummi ina kayan Miyan?

tana nuna masa su tare d cewa ‘Gasu ya

ce,Dauki ki kai ma ummana. Har ta kai bakin kofa

ya sake cewa “Ummi!”ta tsaya ya zo ya kalleta

Ummi kin ji me Bishira ta ce? Ummi ta dube shi

cikin ido,,sannan ta kalli hanyar fita. Naji duk

abnda ku ka ce,Ya lumshe ido “Ummi dn Allah ka

da ki fad ma Umma. Ta tsura mashi ido,bata

ta6a jin Abba ya yi mata magana cikin tattausar

murya ba sai yau tunda ta taso. Ta ce, “To.” Ta

juya, yasa ke cewa Ummi. a waiwayo Don Allah

kin ji? kai kurum ta daga sannan ta fita Tafe take

tana Mmkn me yasa Abba baya son Umma taji

zagin da Matarshi tayi Mata? Hakika d taso

Sanar da Umma amma yanda ya yi ‘yar Murya

yana rokonta sai t jure,koda taje gida bata sanar

d Umma ba. Cewa tayi kawai ya ce a ma barshi

sai dai cikin ranta ta tsani Matar Yaya Abba fiye

d tsanar d ta yi wa Abba. Shi kuwa Abba duk

wata hulda tsakaninnshi d matarshi ya dakatar d

ita,saboda yana son nuna mata matsayin umma a

gurinshi. In ya fita tn Asubahi bacce ke kawo shi

gidan,wanka ma cn gdn Umma yake yi sai ya ce

mata Bishira tana mkrnt. A cikin rana t 3 hnklnta

y gama tashi,taje t fadawa umman Bashir,ta aiko

yaje tayi ta fadan gami d zazzagnshi,ya bata hkr

y fita. Amma sam Bishira, bai canza mata ba. Sai

ma sabon salon d ya dauko na yn kaura daga

falon zuwa dayan dakin d babu kowa,dk kayn

sawanshi y tattara y koma can. Abba yana d zcy

g taurin kai,Umman Bashir ta ce,”Yanzun in kin

samu saukinshi to uwar goyonshi ki ka fada

mawa, km gwada ki gani za ki gane ta fini a

gurinsa. Sannan ki g aikin asiri. . Shi kuma zai je

ya fada ma umma, dn yana son d dunkunan wata

amarya d yake son karasawa ummi ta zun6uri

baki bayan ta amshi kudin ta wuce tana yankun-

kunai, ya ce “Ke!” ta waigo “Zo nan . ta dawo, Ya

kama mata kunne, Kin san kwana 2 bn ta6a

lafiyarki ba ko?to kiyi abn d yau zaki gwammace

ba ki zo duniya ba. ya rankwashe mata kai,

Sannan ta wuce tayi ce fanan ta nufi gidn Matar

gidn tana zaune d kayan mkrnt a jikinta,,Ummi ta

mata Sannu harara ta zuba ma Ummi, Ummi ko

ta rama,sannan ta ce “Mijinki ya ce in zo in yi

mashi sakwara d miya. “Bishira ta ce, To sai ki

koma gidn ubnki ki dauko tukunya d murhu b dai

nawa ba, Ummi ta ce, To ni dai gaskiya d ubana

ba. Bishira ta taso tana cewa Sai na wa? Ummi

ta ce, Oho,amma ba nawa ba. Za ta kai mata

duka ta goce ta ajiye mata kayan miyan ta ce “

Gashi sai kiyi, kila ma baki iya girki ba ne. Taje

ta fadawa umma, Umma ta ce “Ke ummi karya ki

ke daga zuwa zata hauki d zagi sai ka ce

Mahaukacciya? To kije ki fada wa Abban in ya so

sai kuje tare ya fada mata amma fa kada ki ce

masa ta zage ki, ki ce masa dai yazo ya fada

mata zaki tayata. Ummi ko kyn mkrnt ba ta cire

ba ta nufi gurinshi,yana tsaka dinki taje,Ummi sai

ce masa tayi ta ce ba zam mata girki d tukunya

ba. Ya ce Muje gidn ganin nan. “a kofar gida ta

zauna tana jiranshi, sai d y shiga sannan ta bishi.

Tana tsaye tsakar gida tana jin rigimar d suke

yi.Bishira ta dage ita fa babu mai yi mata girki d

kayan aiki, shi kuma ya ce tunda ba a koya miki

girki ba a gidnku dole ne in sa kanwata ta mini.

Ta ce ya turo Fati mana,wannan maran kunyar

yarinyar mata tarbiyya ba za ta zo mata gida ta

zage ta ba. Ran Abba ya 6aci, ya ce Ga ki nan

mara tarbiya,ina fada kina fada ina matsayin

mijinki.,Ummi tafi ki tarbiyya domin uwar d ta

bata tarbiyya ita ta bani har ki ka amince ki ka

aure Ni. Ta ce, Ta baka tarbiyya ko ta asirceka?

Ta mallake ka har baka ganin Mahaifiyarka d

gashi sai ita. Zancen ya soki Abba sosai Har ya

daga hannu zai mareta sai kuma ya fasa,ya juya

ya fita. Fatanshi Allah ya sa ummi bata ji ba,dn

yasan tsaf sai ta fada ma Umma. Tana zaune

gefen rijiya ya nufo ta,Ummi ina kayan Miyan?

tana nuna masa su tare d cewa ‘Gasu ya

ce,Dauki ki kai ma ummana. Har ta kai bakin kofa

ya sake cewa “Ummi!”ta tsaya ya zo ya kalleta

Ummi kin ji me Bishira ta ce? Ummi ta dube shi

cikin ido,,sannan ta kalli hanyar fita. Naji duk

abnda ku ka ce,Ya lumshe ido “Ummi dn Allah ka

da ki fad ma Umma. Ta tsura mashi ido,bata

ta6a jin Abba ya yi mata magana cikin tattausar

murya ba sai yau tunda ta taso. Ta ce, “To.” Ta

juya, yasa ke cewa Ummi. a waiwayo Don Allah

kin ji? kai kurum ta daga sannan ta fita Tafe take

tana Mmkn me yasa Abba baya son Umma taji

zagin da Matarshi tayi Mata? Hakika d taso

Sanar da Umma amma yanda ya yi ‘yar Murya

yana rokonta sai t jure,koda taje gida bata sanar

d Umma ba. Cewa tayi kawai ya ce a ma barshi

sai dai cikin ranta ta tsani Matar Yaya Abba fiye

d tsanar d ta yi wa Abba. Shi kuwa Abba duk

wata hulda tsakaninnshi d matarshi ya dakatar d

ita,saboda yana son nuna mata matsayin umma a

gurinshi. In ya fita tn Asubahi bacce ke kawo shi

gidan,wanka ma cn gdn Umma yake yi sai ya ce

mata Bishira tana mkrnt. A cikin rana t 3 hnklnta

y gama tashi,taje t fadawa umman Bashir,ta aiko

yaje tayi ta fadan gami d zazzagnshi,ya bata hkr

y fita. Amma sam Bishira, bai canza mata ba. Sai

ma sabon salon d ya dauko na yn kaura daga

falon zuwa dayan dakin d babu kowa,dk kayn

sawanshi y tattara y koma can. Abba yana d zcy

g taurin kai,Umman Bashir ta ce,”Yanzun in kin

samu saukinshi to uwar goyonshi ki ka fada

mawa, km gwada ki gani za ki gane ta fini a

gurinsa. Sannan ki g aikin asiri. . Bishira t nufi

gurin umma t same t zaune tana yankan ku6ewar

miya. tun d a ka kawo ta yau ne rana ta farko d

ta zo. Umma ta ce, “A’a Maraba d Bshra. shigo

koda yake je ki gaida tsohuwa. Taje suks

gaisa,Tsohuwa ta ce Ke dai wannan yarinyar

kirkinki d sauki,a ce tunda ki ka zo unguwar nan

baki ta6a zuwa kin gaida iyayensa ba? Umma t

jiyo 6aram6aramar d Tsohuwa ke yi,d sauri tazo

ta ce Tsohuwa b laifinta ba ne, laifin Abba ne. Ba

sai ya kawo ta ba za tazo? Jin haka Bishira ta

samu bakin magana,wlh Tsohuwa laifinsa ne nayi

in zo ya ki,yanzun hk kararsa na kawo. in y fita

tn Asubahi sai dare bana sanin shigowarshi.

Yanzun ni tn jiya ma bn sa shi a idona ba,Umma

ta ce Shi Abban ne ke hk? Ta ce IIlahi kuwa, ni

bana son in je gidanmu in kai karanshi ne amma

shi baya gani,yanzun fa ya tattare y koma dakin

nan d ba kowa. Ran Umma ya 6aci, a irin

tarbiyyar da ta yi wa Abba bata zaci zai

wulaqanta mace ba, . Ummi tana shigowa daga

Islamiyya ta ce,maza d sauri shagon yayanki kira

mn shi. kan keke ta same shi yana t dinki, t shiga

d sallama,sauran yaran shagon ma suna t

dinki,ta ce yaya Abba Umma ta ce kazo yanzu.

Ya dube ta me ya faru?Ta girgiza kai,bn sani ba,

ta dai ce kazo. Take ya mike,ita km t fice d gudu.

A ranshi ya ce ko yaushi Ummi zata yi hnkl t

dinga tafiya irin t mata? Yana shiga gidn umma t

rufe shi d fada,ba tare d tambaye shi dalilin shi

na yi wa matarshi abn d yake mata ba. Ta

ce,”Maza gata nan dakin Tsohuwa kaje ku koma

gida ka bata hkr. kanshi na kasa bai ce kala ba

ya nufi dakin Tsohuwa. Ya dube ta Tashi muje.

Har daki suka shiga ya dube ta kiyi hkr. Ta ce, To

nima kayi hkr. Ya ce kin ga matar d ki ke zagi ta

baki gaskiya alhalin danta nake fushi. Ya ce ki

kula kici albarkacinta karki sake ki km fadin wata

mummunar magana a kanta,km hucewar da nayi

da hkrn d na baki kada ki zata dn kin isa

ne,umurninta na cika,ta ce to na daina. . Da dare

gidn Umma ya je ya bata hkrn dn yaga ta dau

zafi, ya ce, “Umma yarinyar nan bata kyautawa,

abn d take min ni d har zan kai wa yarta kara na

gaji. Umma ta ce, kada ka soma,kayi t hkr in

girkin ne matsalarku tunda bata son tazo ta koya

kai ai ka iya,sai ka ware lkc ka zauna ka dinga

koya mata kasa tayi kana kallo har ta iya. Ya ce

To, amma kin huce kin daina haushina,? Umma

ta ce , sam ban jin haushinka Abba raina yana

6aci ne in ji an ce ga laifinka, ya ce to na gode

ummata. Shawarar Ummanshi ya dauka,ranar

farko ya ce ta dora farar shinka fa sai da ya koya

mata yadda zata dafata kashi-kashi,harkala 4.

Sannan ya ce,tayi jajjage tayi tana wai-wai ita

duk ta gaji. Yana gefe zaune d wayarshi yana ta

Game sai d yasa ta tayi miyar komai yana nuna

mata yadda zata yi. Sai gashi kafin wani lkc

Bishira ta iya girki, gurin tuwo ne a ka danfi

samun matsala,sukai kwana 4 suna yi yana

gudaji. . Yanzu sun samu jituwa dk d dai abncin

ma ba ya samunshi kn lkc sai dai kuma fannin

tsafta.Duk da yakan zage ya gyara gidn d shara

kullum in ya dawo Masallaci ya wanke bayi

fes,cikin dakunan a nan matsalar take, sannan

jikinta ma bata son gyara shi. Cikin haka ta kamu

d laulayin ciki sun je asibti sun samu magunguna

dk d hk amai ko ruwa tasha sai y dawo, dk hnkln

Abba ya tashi y kira wayar Anti ya sanar d ita.

Da dare tazo dubata ita d mijinta suka zo,sun

same su Abba yana bata tea,ganin Anty,Bishira ta

soma kuka wai ita zata bi Anty. Anty ta ce A”a ki

zauna ga mijinki na kula d ke, ni dai bana zama

in kin je gidana ba zai miki dadi ba. Sunyi Murna

d Abba ya fada musu ciki ne, take Anty ta kira

Mahaifiyarsu ta fada mata. “Tabdi!” in ji hjy. tun

yanzun? To Allah ya raba lfy. Anty ta ce to sai

anjima,dn jin yadda hjyr bata yi murna d cikin ba,

km bata so Abba ya gane. Ta dubi Bishira, Momy

ta ce a gaisheki d jiki, Bishira ta ce ba za ta zo

ba?Rannan d muka yi waya d Anty Aisha ta ce

min ita ko Momy taje / ZURFIN CIKI book 1 part 8

ZURFIN CIKI book 1 part 8

Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 – 22:01

Ni kuma sai naga ta min qanqanta. Ummi ta ce,

ahj kaima ka sai mota ne mu dinga shiga? ya ce,

to xan siya mamana, ki dunga min addu’a kinji?

umma ta ce, nayi murna abbana, ya yi abin

hawa. bari in je masa albishir. tsohuwa ta taba

baki, sannan ta ce, kullum burinku da tattalinku

na ne sunan mlm ne, ita takwara kun maida ta

baya. umma ta ce, sai na dawo. ta fice, dan

tasan tsohuwa da mita. abba yayi murna samun

abin hawa, domin da dan nisa in da ya ke xuwa,

waton makarantarsu ummi, in ya shirya ya kanxo

gidansu ummanshi ya dauki ummi su tafi. jwanci

tashi su ummi an shiga aji uku, lkcn abba ya

gama service din shi, ya amshi certificate. bayan

sun je sun yi faretinsu. dakin umma ya dire, ummi

tunda ya shigo take kallonshi da kayan yan

bautar qasa. ita kam kayan suna birgeta, ya dube

ta kallan fa? ta dauke kanta, sannan ta murguda

baki, umma ta nufi kicin tana dariyar halin ummi

da abba. dama ummin tana kwance kan kujera ne

tana wasa da wayar umma, yace ta ga me kyau

tana ta kallona, ba xa dai ki samu miji mai kyau

kamar ni ba. . Ba ta san lkcn da ta ce, tir, da me

kama da kai gara in mutu banyi aure ba. ya

dubeta da sauri sannan ya dauki hijab din umma

ya jefeta, tare da cewa, mummuna, qaxama gaki

mahaukaciya. wama xai aure ki? sai kn

mahaukaci dan umanki. ta hade rai tana

kallanshi, ya ce daina kallona me kama da

goggon biri, in kuma kika min wata magana in

xane ki. fuu ta tashi ta shige uwar daki. tana jiyo

hiransu da umma, in da yake cewa, naso a ce

ummi tana aji uku ne lkcn da xan bar

makarantantan mu bari tare, saboda sam bata ji.

gashi akwai mlmn da aka samu a makarantan ma

su bata yara, sannan tana da wata qawa da aka

kama da wani malami a bayin makaranta. sai da

taci duka sannan ta rabu da yarinyar. umma ta

daff qirji tare da cewa, na siige su ni suwaiba, to

ko amina ce qawan tata? abba ya ce, ba ita ba

ce. umma ta ce, hu-um, to makarantar boko dai

ba tilas, da yaro ya fada cikin irin wannan

rayuwar gara a bar bokm. abba ya ce, ina ganin

xan nemi koyarwa a makarantan, in naci sa’a an

daukeni to sai ta qarasa har lkcn. . Abba ya ce

Ina ganin zan nemi koyarwa a mkrntr in na ci sa’

an daukeni to sai ta ci gaba hr zuwa lkcn d zata

gama,sai in bar koyarwar. Umma ta ce,To hkn za

a yi. Ummi km daga cikn dk take mgn ita 1,ta ce

Da na shiga 3,ka ci gaba d koyarwa a mkrntrm ko

dai ka ci gaba d hn ni sakewa? In yana aji

numfashi mai karfi ma bana iya yin shi,Allah yasa

kada a dauke ka. Murna kmr me gurin Ummi d

taga an yi bakwai 2 Abba bai zo ba,hk na nufin

ba a dauke shi a mkrntr ba. . Don hk ta ci gaba d

tsula tsiyarta. Kwatam! a sati na 3 sai gashi ya

zo daukarta suje mkrnt,hr kuka sai d ummi tayi

don takaici. Daga dawowarshi km y dora mata

daga in d ya tsaya,d rashin mutunci,hr t soma yi

mishi fatan mutuwa,dn tana ganin matsawar

Abba yana raye baza ta ta6a jin dadin rayuwar

dny ba. Tunda cikin bishira ya samu t daina zuwa

mkrnt, Abba bai matsa mata ba,amma d yaga t

soma dan jin dadi,sai ya ce ta fara zuwa. . Haka

ta ke zuwan yau taje gobe ta ki zuwa ta ce ba a

komai hr lkcn biyn kudi yayi. Duk d tsadar mkrntr

hk Abba ya fige ya biya,daga bisani ma sai ta

daina zuwa, Abba ya kira Anty a waya ya fada

mata Bishira ta ki zuwa mkrnt. Yaya-yayi ta

ki,shi km gsky ta zo tayi mata fada,dn ba ya so

su momy suga laifinshi., Don ko d suka je

gaisuwar surukai sai d ta ce “Kada a katsewa

‘yarta krt”Anti ta ce za ta zo. . Ai kuwa ranar d

Anty tazo taga ta kaici gidn Bishira,ko ina

datti,Falon d ta leka dk kura d yanar gizo-gzo.

Cikin dakin baccinsu kuwa ko ina yamutse d

kaya,bngo dk t tofe shi d miyau,sannan g wani

gwangwani madara gefenta ta kusan cika shi d

miyau. Gashin kanta rabi an tsefe shi rabi ba a

tsefe ba.jikinta fari sol tamkar bai ta6a ganin

ruwa ba. Anty t doka salati tare d cewa Bishira

me zan gani hk?Dan ubnki hk ki k dawo? Dubi

gdnk?dubu kanki? A kanki a ka soma ciki?nan t

zauna ta zageta tas, sannan ta taya t suka gyara

gidn suna yi tana fada. Ta ce Hk ki ka ga ina yi a

gidana?Ko sauran jama’a hk suke yi? Za ki sa a

zagi uwarmu a ce an sangarta ki alhalin aikin

gida dk a na sa ku.Sannan kin ki mkrnt,to ki sani

kanki zaki cuta dn kuwa dk ranar d mijinki y

zama wani abu ‘yar boko zaya nema ya tafi d ita

cikin lamuranshi. . Zan km hada ki d momy.byn

sun gyara gidn t sata tayi wanka t dauki kaya

masu kyau t saka. Gwangwanin miyau tasa t tayi

jifa dashi,ta ce ki dinga saka sweet ko goro a

bakinki zanje nan d sati 1 zan dauko momy muzo

tare. kin san dai me zai biyo baya. Abba da ya

shigo gdn byn Isha’i dk d cewa dare ne sai d y

gane an tsaftace gdn,Domin kamshi tare d iskar

da ke kadawa a gdn sun bayyana hk. Dakin ta da

ya yi wa kaura yau kam hr bakin gado,ganin t

cikin kwalliya yasa shi cikin wani yanayi wanda

ya kwana 2 bai shiga ba. Ko abncin bai nema

ba,ya shiga caftar Syy,wnd ita ma dk d tana

laulayi tana ra’ayin hkn,don hk sai suka rankaya.

Kwana 2 ya dan samu sauki kazantar dn tana

tsoron momynsu tazo ta gani,sannan tana zuwa

mkrnt. Amma d momyn tazo tayi mata fada t

tafi,shi kenan sai ta koma gdn jiya,dama

Hausawa sun ce mai hali ba ya fasa Halinsa.

Haka dai hr cikin ya tsufa Umma tasa shi ya sayi

dk wani abu da mai jego da jaririnta za su

bukata. . Ita km ta daka yajin mai jego ta tanadi

sabulun salo zuwa Kwallin da za a sa ma jariri.

Wani dare Abba y kira Umma,Alhj ne y daga nan

y sanr d su bishira bata d lfy,yana ganin haiuwa

ce. Alhj d kns y raka umma hr gidn suka buga

Abba ya bude,suka shiga.Ranar Alhj y yi burin

mota,dmn d yana d mota yanzun sai su tafi

assibiti. Bishira bata d juriya,dn hk sai raki take

yi,tana fadin a kaita assibiti. A daddafe suka kai 4

dare Ahlj ya je ya taso abokinshi suka kaita

assibiti tare d su umma,karfe 8 na safe ta haifi

danta namiji. . Umman Bashir d taji sai ta hau

fadan me ya sa ba a sanr d ita ba?Alhj karami ya

rufeta d fadan cewa,ita wace irin mutum ce? Sam

ita bata son Alkairi ba,sannan ya fita ya yi wa

Alhj babba barka,dg assibti gdnsu iyayenta suka

wuce d ita ba tare d sun nemi shawarar mijinta

ba ko ta iyayenshi. Hjy ce ta bada wannan

umurnin,rai 6ace Abba ya zo gurin umma dn ita

ta baro gurin ne d iyayenta suka iso. Ya

ce,”dama umma umma haka akeyi sai a daukar

wa mu2m mata a tafi da ita ba tare da neman

izini ba?to gaskiya bazan yarda ba.” umma ta

ce,”ka kyalesu, Allah ya raya.shi kenan, tafiya da

ita ba laifi bane tunda ita kadai ce a gidan ba mai

kula da ita matsalar dai da basu nemi izininka

ba.” ya ce,”sai ka ce ba zamana take ba?

wankan gidan addini ne?dama fa niyyata in kawo

ta nan gidan ki lura da ita.” umma ta ce,”to

yanxu dai hakuri kawai zan baka,ka bar

maganar.” tayi ta lallashinsa har dai ya

hakura,amma shifa ya dau alwashin sai ya nuna

musu nasa ikon. umma ta hada abubuwan data

tanada suka tafi da makota.bayan sun shiga

gidan aka kai su gefen da maijego take. sun sami

dakin tamkam da jama’a nan dai suka zauna aka

gaisa,sa wani gani-gani ake musu ga talakawa.

umma ta ce,bishira ina ummar taku mu gaisa?sai

da ta yatsin fuska sannan ta kalli

kanwarta”sumayy a kije ki cewa momy ga

baki,koda yake kice mata yan gidan su Abba ne.”

Hajiya zainu tana zaune da kawayenta da suka zo

barka, tana labarta musu rashin mutuncin dangin

mijin bishira dashi kanshi mijin. ta ce,”yau

kwananta uku tunda tazo gidan nan bashi ba

danginshi,kuma yanda bishiran take fada mana

laifin masu rikonshi wato wan ubansa da

matarsa. sun mallake yaron sai abinda suka

ce,hajiya nafi ta ce,”ku nuna musu kuskurensu ne

yanzu haka tunda kika ga sun mallake shi kila

shine mai dan samun gunshi suke ci.” Hajiya

sabuwa ta ce”shi yasa auran talaka ko tsiya,yar

wajena Amina da tazo min da wani wai sun hadu

a ummara,koda na bincika sai na tarar likita

ne.karamin likita ubanshi dashi ya dogara na ce

ba dani ba.” Hajiya zainu ta ce”ai gara shi

wannan fa tela ne.” “TELA?” kawayen suka hada

baki, ta ce”au dama ku duk fadan da nayi lokacin

biki baku ji ba? tabi ta nace sai shi gashi nan

yanzun ya wulakanta mu.” Ta dube su d

wulanqacin da ya fi Ki haihu kwana 3 tun dg

asibiti miji bai kuma bi ta kanki ba? Hjy Nafi ta

ce in bai zo don kowa ba ma yazo dn dansa.

Zainu ta ce Ina nan ina jira ko shi ko danginshi

domin…….. Sumayya ce ta katse su da sallama.

Sannan tace momy wai kizo ga yan gidan su

Abba sun zo. su duka suka mike ita d kawaynta

suka nufi gurin su Umma. Hjy Zainu ta kalli gurin

d su umma suke,sannan ta kalli Bishira,

wadannan sune ‘yan gdn Su Abban? Bishira ta ce

Eh ummar tasa ce gata nan. ta nuna umma Hjy

zainu suka kalli juna d kawayenta sannan suka yi

‘yar dry wanda hkn ya kashe jikin umman. Tasan

cewa akwai wani tanadi d a ka yi mata. Hjy

Zainu ta ce d kawayenta ku mu zauna,aikin

zaune yafi na tsaye. Suka zauna. Ta kalli umma

Dama ko ina son ganinki,ke ce uwar goyon tasa

ko? ta ci gaba To gsky ba ki yi wa dnki tarbiyya

ba,sbd rashin mutunci a yi maka haihuwa amma

kwana 3 ba zuwa ba aike? Kuma sai yau za ku

kwaso kafa kuzo in ‘yarki ce zaki so hk?umma

tayi shirun tana tunani, ta kuma rasa me zata ce

dn tund take ba a ta6a ci mata mutunci ba irin

wannan ba. Amma ita bata iya fada ba,dn hk sai

ta ce, To Hjy a yi hkr, bn san cewa Abba bai zo

ba,Amma zan tsawata mishi,dn kuwa bai kyauta

ba. Sai dai km shi ma bai so yadda a ka dauko

masa mata ba izininshi ba,dn ya same ni d

fushinsa ya ce min shi ba ya son wankan gidan

nan,sannan ba a yi shawara da shi ba a ka taho

d ita nan. kin ga km hkn bai dace ba……….

“Dakata min Hjy zainu ta katse ta Shi ne ya

haifar min ‘yar d hr zan tsaya neman izininsa?

shi kuma a wa? Ramatu mokociyarsu ta ce “Miji

km hjy ai ba abn wasa ba ne. hjy nafi ta ce ko?to

ke kinji hjy Zainu tabdi!Tun farko kuskuran naki

ne da ki ka bar ‘yarki tayi irin wannan auran na

rainin d tsiya. Umma ta ce d abokan tafiyarta

wadanda ko dan (ba) ba su ce ba, ta ce kuzo

muje”Ta dubi hjyr “Allah ya baku hkr.Hjy zainu ta

ce Ai ban ga gama maganata ba. umma ta ce,To

fadi ina jinki. Hjy zainu ta ce Sako ne zuwa ga

danki ki fada masa ba komai muke nema dg gare

shi ba,abn d ya siya ma na yaron dk mun canza

wasu sdb dk ‘yan gida ne. Bukatarmu ya zo ya yi

wa yaronsa huduba,in km ya kai gobe za mu yi

masa d kanmu. umma ta ce Abba ya yi wa dansa

huduba,tn lkcn d a ka haife shi. Hjy Zainu ta

ce,To ai bai yi shawara d uwar yaron ba,ko d ya

ke ga ki dawa zaiyi shawara? Uwar d ta haife shi

ma bata zama komai ba, a dai ji tsoron Allah.

umma jiki ba karfi ta fito. Su Ramatu suka biyo

ta hr kuka sai d umma tayi dn takaici. koda taje

gida sam bata fada ma kowa komai ba,illa dai dk

wanda ke gidn yasan yau umma tana cikin 6acin

rai. Hatta ummi da bata d kn gado sai d tayi ta

tambayrta,umma baki d lfy ne?ta ce Eh,kaine ke

ciwo. Da ta zauna sai ta shiga tunani so take

lallai sai ta gane aibnta,ko kasawarta akn Abba.

Ta kasa fahimtar mallakr d a ke fadin tayi wa

Abba. Tana ganin nuna tsanarta ga Abba shi ne

mafitarta. Abba ne ya katse mata tunani d cewa

Ummana ina t zuwa ba kya nan. Ta dube shi g

mmknta ba ta iya bayya tsanarta g Abban,

maimakon hk ma sai ta samu kanta da cewa

Naje ganin jariri ne. Ya shiga ya zauna kusa d ita

t dube shi Yanzu Abba dm bn isa in fada maka

mgn ka ji ba?Dama kin zuwa kayi ka duba

matarka da danka? Ya shafa kai,Umma anjima d

dare zamu da su Ahmad ni haushi sukai bani. Ta

ce to ka tabbata yau din kaje,Sannan ko sun

nuna ma fushinsu naka kawai ka ba su hkr,Ya ce

to umma ta ce Na sanka d zcy ne. Ya ce to zan

kiyaye Umma. Ya kuma dabn ta ummata yau na

ganki a yanayi mara dadin gani. ta dube shi kaina

ke ciwo Abba na kuma sha magani. Da gaske

ciwo kanta ya dinga yi dn damuwa. Yace Allah y

kara sauki. Ya fita. Da Ahmad d Muktar suka

je,sun ci sa’a Alhjn yana gari. suka shiga suka

gaishe shi suka kuma yi wa juna barka. Sam ba

ruwanshi da matsala,Suka shiga ciki tare d

Sumyya,sn samu Aisha ta zo ita d mijinta.

Bishira km hade rai tayi lkcn d taga su Abba? Su

Muktar suka dauki jariri,sannan suka gaida mai

jego. ta amsa tana musu wani kallon daga ina?

Aisha ce taje ta sanar d uwar tasu. Nan ko ta

shigo ta samu su Abba d abokanshi. Ta shiga

zazzaga mishi masi fa,wai sai yau yaga damar

zuwa?Ai ta samu lbrn yadda yake wulaqanta

mata yarinya. ta ce km a bakin mahaifiyarka naji

kaji tsoron Allah ka talike a gurin uwar goyonka

sai yadda ta ce. to ‘yata tafi karfinta. Abba sam

ba zai juri ji ba,dn hk ya mike ya fita. tana ta

cewa saurare ni ko waiwayowa bai yi ba. Su

Muktar dai suna ciki suna bata hkr ya kira wayar

Ahamad ya ce zan tafi in ba za ku fito ba. Ya

kashe ba tare d jiran asmar Ahmad din ba, hk

suka fito. Muktar ya ce Tabdi! lallai matar

gidannan bata d mutunci.Ahamd ya ce ka fada

ma mai gidan Mana. Abba ya ce Ni sai ma in

sakar Musu ‘yarsu “Kul in ji Muktar, Kada kayi hk

Ahmad ya ce, Ashe hr umma suka yi wa rashin

mutunci dazu? Abba ya ce Ummata?Muktar ya ce

Eh, bayn fitarka take fada,Abba ya yi shiru dn

takaici. Gidanshi ya wuce,gado ya hau ya

kwanta. . Tabbas sun ci zarafin ummarshi,dn ya

ganta cikin yanayin da bai ta6a ganinta aciki ba.

Ko me dame suka fada mata?Umma bata

cancanci cin zarafi ba.Ranshi ya kai makura

gurin 6aci,ya rufe gidn ya nufi gdn su Umma.

Lkcn d ya shiga umma ta nufi dakin

Alhj,Sallamarshi ce ta tsaida ita,ya shiga dakinta

ta dawo ta shiga. Tana cewa Abba hr ka dawo

daga gurin ma su jegon?bai amsa ba,kanshi na

kasa,dmn sai ya samu kansa da jin kunyarta

sakamakon abn d aka mata sbd shi. Ta ce lfy

Abbana?Ya dube ta,maimakon amsa sai ya ce

umma me suka ce miki dazun d ki ka je gidn?

Tayi dn yaki ita a dole Murmushi , Na me Abba?

ya ce mamn bishira ta ce taci miki mutunci ko?

Umma tayi ‘yar dry,sannan ta ce ko daya ta dai

fada maka hk ne dn kaji haushi. Ta ciga ba d

cewa,Abba dn Allah ka bi sannu hr t dawo…… Ya

ce umma na san sunci miki zarafi sosai “ZURFIN

CIKI’ ne da ke umma shi yasa ki ka shanye,

amma yanayinki dazn y nuna.Umma b zan zauna

d matar d baya san darajarki, dk kuwa yadda na

kai sonta,ina ga zamanmu ba zai yiwa d bishira

ba. Umma ta ce “Kai! Kai!! kul na sake ji zanyi

fushi d kai me tsanani Abba,dk hakkinsu d ke

kanka matarka d danka ta ka sauke su,kuma

koyaushe kaje ka gansu, ba km na son su Alhj

suji wannan zancan. Ya ce yanzun hk zan zauna

umma cikin 6acin rai? Tunda na auri matar nan

bn huta ba,kema baki daina shan zagi ba? umma

ta matso kusa da shi ta dafa kafadarshi. Abbana

ka sani cewa ba a toru ka dny dn k huta ba,nawa

ganin duk wanda a ka haifa daga ran d ya diro

dny y gama hutu komai jin dadinsa,komai

kudinsa,ko mulki. Hutu daya ne in ka mutu ka

sadu d rahamar Allah,ita kuwa Rahama bata

samuwa g wanda bai bi Allah d manzo ba. Bn

Allah kuwa shine kada ka bata masa,kabi dukkan

abn d Manzonsa ya yi umurni,Sannan ka hanu

daga abn d ya yi hani. Aure bautar Allah ne Kum

sai kayi hkr sannan za ka yi bauta d kyau. hk dai

umma tayi ta wa Abba nasiha hr zcyrsa t sauka,

sannan sukayi Sallama. Washe gari misalin karfe

2,Abba ya dawo gida dg mkrnt d yake koyarwa,

dn suna ta shirye-shiryn jarabawa (J.S.C.E.) Su

ummi ne za su zana,wnk y fito sai ga wayr Alhj

ta shigo.Y daga cikin girmamawa. Bayn sun gaisa

Alhj ya ce Abbana kana ina ne? Ya ce ina nan

gida.Alhj ya ce kaje gidanmu ka amshi mukallin

dakina ka shiga kasa mukallika bude dirowar nan

tawa,zaka g wadansu ta kardu irin littafin nan na

rubutu. kabi a hnkl za ka g wani a samnshi an

rubuta Alhj Sale Jigawa,d ajami ne rubutun,maza

ka kawo min. Abba ya ce to.,Yana cikin duba

littattafan sai ya ga wani an rubuta wasiyya,dk

littattafan d ajami Alhj yake rubutu, Abba ya dauki

littafi ya bude shafin farko an rubuta…….. Babi

Na Daya “Ni Alhj Sulaiman, nayi kudirin ko bayan

raina ‘yata Habiba (ummi) zan aurar d ita ga dan

Idrisu(Abba). Da sauri Abba ya rufe littafin

gabnshi yana wata muguwar faduwa,ya sake

budewa ya kalli kwanan wata. Alhj yayi rubutun

ne ranar d a ka haifi ummi,Ya yi sauri ya maida

komai ya dauki wnd aka aiko shu yana zufa ya

kalle dakin ya maida wa umma makullin ya fita

da sauri Ya buga mashin can ya hango ummi

suna dambe da wani yaro an raba su ta tirje

kafafunta ba ko takalmi, mayafinta taci damara

da shi. Ya ce “Ke! tn dg nesa ta jiyo muryar

Abba,ya yi mata dakuwa ta kwashi takalmanta a

hannu ta yanka d gudu. Yabi ta da kallo hr ta

shige gida ya lumshe ido tare d fadin “Innalillahi

wa’inna ilaihin raji’un.”Me ma ya kai shi bude

littafin wasiyyar Alhj Babba, Duk garin kano akwai

mutumin d ya tsana irin Ummi?? To fa! ku

biyomu a littafi na biyu 

Agajahub publishers

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top