Idan nayi aure mijina ya tafi kallon kwallo zan rufe gida in kashe wayata—Fateema Zahra
Yau muna tafe da ra’ayin wata budurwa mai suna Fateema Zahra wacce ra’ayin nata ya tada kura tare da yamutsa hazo a shafukan sada zumunta na social media.
Inda wasu mazan ke goyon bayanta yayin da wasu ke zagibta tare da kunduma mata ashariya, ga abinda ta ce.
MATA GA SHAWARA: Idan mijin ki ya tafi kallon kwallo da daddare ki rufe kofa sannan ki kashe wayarki kibar dan iska ya kwana a waje.
Inbanda iskanci kana bukatar mijin ka yana wajen kallon su Messi da Ronaldo.
Ra’ayi Fatima Zarah
Agajahub publishers