ZAMAN MAKOKI-Page1-
to-end OCTOBER 23, 2016 | RASHIDATKARDAM | 2 COMMENTS [4:53PM, 9/16/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *Na* *Ummieluff* *Rash Kardam* _Bissmillahi rahmanu rahim_ _Dukkan yabo ya tabbata ga ubangijin sama da k’asa, mai raya kuma mai kashewa_ *Tsokaci* _Wanna labari k’agagen labari ne munyi shi sabida abunda yake faruwa a wannan zamani namu a gidan rasuwa, in har yazo iri d’aya da labarin ki/ka to sai ku gyara ba wai dan tozarci mukayi ba sai dan samun gyara aciki al’umma. Ya Allah muna rok’anka ka bamu ikon farashi mu kuma gama lafiya Amin._ *Gamasu gyara k’ofa a bud’e take muna sauraronku don ko da yaushe mu masu kuskure ne sai fatan Allah ya yafe mana kuma muna maraba da masu na gyara.* *Jin-jina* “`Jin-jina da duk wata k’ungiyan“` *“`ONLINE HAUSA WRITERS“`* “`muna k’ara gode muku da jin-jina muku gurin k’ara d’aukaka rubutu da jajurcewa gurin kare marban rubutu da hausa Allah ya k’ara d’aukaka da basira Ameen.“` *“`NAGARTA WRITERS ASSO“`* *“`FIKRA WRITERS ASSO“`* *“`EXCELLENT WRITERS“`* *“`ONLINE HAUSA WRITERS “`* *“`WISDOM HAUSA WRITERS “`* *“`EXTREME HAUSA WRITERS“`* *“`WRITERS WORLD ASSO“`* “`Allah ya k’ara maku d’aukaka da Albarka Ameen.“` Page *1~5* Matashiyar narinya na hango bak’ace tana sanye da hijab mai ruwan madara kalo d’aya zaka masa ka gane ya d’an kwana biyu. Yarinya bak’ace tana da d’an tsayi ko damuka kalli fiskanta tana da madai-daicin fuska tana da dogon hanci tare da k’aramin baki sai fararen hakwaranta dake haskawa kalo d’aya zaka mata ka gane nutsuwar da ke tattare da ita tubarkalla mashaa Allah abunda mukace kawai. Cikin sauri naga tunifi gidansu Haneefa da ke Tudun wada hausawa road da sallamanta ta shiga nan ta tarar da Auta tana zaune a gefen Hajiya cikin girmamawa ta gaida Hajiya. Da sakin fuska Hajiya ta amsa ta zauna a gefe Candy ta ce”Auta wai ni sai yaushe zaki rage son jiki”. Auta ta murmusa ta ce“ sai randa zan girma kamar Aunty Haneefa”. Candy ta murmusa ta ce“ah! Lallefa da sauran aiki kenan”. Hira suke yi da Hajiya da Auta da Candy. Amrah da K’urratu~ayni suka shigo bayan sun gaida Hajiya suka zauna. Hajiya ta ce“ya na ganku duk kunyi jigum”. Kurratu~aini ta ce“hmm rasuwa akayi anan balayin bayan mu layin ‘yan kosai”. Hajiya ta ce“innalilahi wa inna ilaihi raji’un waye ya rasu haka?”. K’urratu~ayni ta ce“Malam Idris na gidan su Sa’idu”. Hajiya ta ce“ayya Allah ya jikansa da rahma”. Suka amsa da amin Candy na jin haka ta mik’e da sauri ta ce“Hajiya zan tafi sai anjimanku”. Cikin sauri ta fito ta nufi layin ‘yan kosai da ke bayansu cikin sauri ta nufi anguwan tun daga nesa ta hango mutane zaune ga kulolin abinci wanni sassayan ajiyar zuciya ta saki tana zuwa rumfa da ake karb’an gaisuwa ta k’ak’alo hawaye ta farayi ta rusuna ta gaidasu tukun ta mik’e ta shiga cikin gidan tun daga nesa ta hango drinks kala-kala a jere ga kulolin abinci wasu na ci wasu na shan juice yayin da wasu ke d’aki sai hira suke yi suna shewa tamkar ba a gidan rasuwa suke ba, a haka ta k’ara ta saki kuka a dai-dai k’ofar shiga d’akin tana zuwa ta fara kuka ta na gaida mutane nan suka amsa bayan ta musu ta’aziyya ta ja gefen wata mai cin abinci ga namomi akai tamkar a gidan biki take. Candy sai da ta hadi’yi miyau don yanda k’amshin ke bugan hancinta. Pherty ce ta fito ganin yanda Candy ke kallon mai cin abinci ta ce“bai war Allah zo ki karb’i sadakan abincin kema”. Cikin sauri Candy ta mik’e sukaje gaban kulolin abincin Pherty ta ce“mai kike so a saka mik?”. Candy sai raba ido take ga taliya, ga shefe(shinkafa), ga tuwon shinkafa miyar taushe. Candy ta ce“asa min shinkafanan”. Nan Pherty ta zuba mata tare da nama zuk’u- zuk’u Futha da Ummu Abrar suka iso gun d’auke da wani manyan plate kai ka d’auka su goma zasuci abincin. Jellop d’in shinkafa suka saka tare da nama kamar zai yi magana ga kifi tukun suka d’au juice zasu tashi Candy ta ce“ku d’an k’aramin naman nan da juice d’in ba musu suka k’ara mata tukun suka nufi wani rumfa suka zauna suna ci suna zuba hira tamkar ba gidan rasuwa ba. *_TAGWAYEN MARUBUTA_* Coming soon…. [4:53PM, 9/16/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* _Ummieeluff _ & _Rash Kardam_ Page~6/10 Bayan ta gama ciye’ciyenta ta zame ta kama hanyan gida tana mai ciki da farin ciki, dan ta koshi sosai ta jima bataci abu mai dad’i irin wannan ba. Tana tafia tana wake’wakenta harta iso anguwansu dake tudun wada hausawa road..jikin wani gida ta tsaya,wanda bangon gidan kadan ya rage ya fad’i karamin gidane maidaici..sallama tayi tun daga kofan gidan,sannan ta shiga, d’aki kwaya d’aya ne ah tsakar gidan sai wani ginin daya rushe daga gefe..da kuma d’an wani akurkin kajinsu,sai kuma wani kichen d’in langa’langa dake jikin akurkin d’akin. Hango mahaifiyarta tayi nata faman hura wuta yaki kamawa duk idanunta sunyi jajaye abun tausayi,duk iskancin khadija tana mugun son mamarta bata son taga tana shan wahala..dan ita kad’ai take da ita aduniya. Da sauri ta isu inda take “sannu mama kawo na hura miki” ta kar’bi hura wutan,dataga baida niyyan kamawa ta fita waje tsintan ledodi da ruba sabida ta samu saukin hura wutan. Tana shigowa ta had’a wutan ya kamaci kamar wanda aka xuba masa petrol, ” ummah me xa’a d’aura”? Nuna mata wani tsohon tukunyan tower tayi “d’auki ki dumama mana tuwun jiyane da bakiciba ya rage”..nan take khadija ta ‘bata rai dan ah duniyanta ta tsani d’umame ballema tuwun dawa..da miyan kuka shar daga gishiri saidan magi dabai wuce kwaya 2 ba. Ah xuciyanta tace “ohh Allah ya taimakeni danaje gidan “`MAKOKIN NAN“` naci abu mai dad’i son raina,da yanxu saidai na kwana da yunwa” . “Candy” maman ta kira sunan ta,d’agowa tayi tana kallonta,”toh ki daura abincin mana kikabar wuta naci bayan kinsa babu itacen”da sauri ta d’aura tuwun akan wuta tareda xama daga gefenta. ” waini ina kika shigane tun safe kina yawo ah anguwannan”? Mamah gidansu Haneefa naje ..shine su nana suke fad’a mana anyi rasuwa anan layin yan kosai,shine mukaje gaidasu”. “a’a kikaje dai dan bayanda xa’ayi rasuwa ah anguwannan ace ba’a sameki ah wajenba” wai me kike samu ah xuwa gidan makoki ne? Candy tayi shiru kamar ruwa ya cinyeta. “koh bada ke nake magana ba,ki fad’a min dalilinki na yawan zuwa gidan makoki da kikeyi? ” eyy amm muna zuwa gaishe da sune fa’ bayan kin gaishesu toh zaman me kikeyi? Ta zungoro baki “muna cin shinkafa..ga kuma drinks kala2″. Innalillahi wa’inna elaihi’raju’un” mamah ta fad’a tareda rike baki.” yanzu abunda kuke zuwa yi kenan ah gidan makokin? Kai duniya abin tsoro yanxu rasuwan ma baya bawa mutane tsoro saidai aje ayita hira anacin abinci kamar gidan biki” toh khadija Allah ya shiryeki..ki kumayi hankali da xuwa gidan makoki..dan talauci ba hauka bane.”toh toh mama basu bane suke bamu..”oho nidai na fad’amiki kiyi hankali da biyebiyen gidan makoki. “`Shin wacece khadija (Candy?)“` _khadija Abubakar Alkali_ shine cikakken sunanta..mahaifinta malam Abubakar Allah yamasa rasuwa tun tana qarama..bata wani saba dashiba..dama sana’ansa shine facin tayoyin mota da keke..bayan rasuwansa Maryama watoh mahaifiyar ta kenan taci gaba da d’aukan dawainiyar yarta tilo guda d’aya khadaji wacce akafi sani da candy..candy nason mamanta sosai sabida ta wahala akanta ainun..kullum magananta mamana,banida kowa aduniya sai mamana. Koh Aure batason amata maganan sa sabida bata son rabuwa da mamanta. Matsalanta d’aya masifan son xuwa *Gidan Makoki* da Allah ya d’aura mata,koh muce ta d’aurawa kanta.duk nisan inda taji rasuwa toh insha Allahu xakuga candy acan..burinta kawai abinci da drinks..kowanne cikin kawayenta taji anyi rasuwa toh xai sanar da dan uwansa..su d’ebi juna xuwa gaisuwa kodako basusan suba..su zarah B B ah gaba..na kalli rasheeda,itama ni take kallo atare muka had’a baki wurin fad’in,“`ikon Allah!“` *TA GWAYEN MARUBUTA* [4:53PM, 9/16/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *Na* *Rash Kardam* *Ummieluff* Page *11~15* Burinta kawai abinci da drinks..kowanne cikin kawayenta taji anyi rasuwa toh xai sanar da d’an uwansa.. Su d’ebi juna zuwa gaisuwa kodako basusan suba..su zarah B B da Aneesa da Munay a gaba.. Na kalli rasheeda,itama ni take kallo atare muka had’a baki wurin fad’in,“`ikon Allah!“` kuma duk in ka gansu a gidan rasuwa sun iya yanka manyan loma tamkar sunyi makarantar koyan manyan loma. Khadija tayi makarantar primary da ke Tudun wada gata da k’ok’ari sosai tun tasowarta mayyar Candy ce ita ko kud’i ka bata bata damu ba gwara ka saya mata Candy milk yafiye mata komai sai shinkafa(shefe) ko aika taje bata wuce tayin shefe. Ma haifiyar Candy tana k’ok’arinta gun yin aikatau na gida da ‘yan kule-kulen kayan miya don ta tsare mutuncinsu abu d’aya da ya musu sauki gidan kansu suke bana haya ba inda rayuwan tazo musu da sauki kenan. Candy tana da kyau nagaban kwatance don tun tana k’arama wasu ke zuwa kamun kafa akan in ta girma suna sonta amma sam Ummanta taki ta ce“sai in yarinya ta girma ta amince da kanta tukunna”. Da wannan kalaman take ja ma masu sonta burki Umma ta kan d’aura ma Candy tallan sabulu da omo lokacin tana primary haka Candy zataje ta ajiye tallan ta kama carafke ko tambo sai lokacin komawa gida yayi ta fara zare ido ga kaya ajibge, in ta koma gida Umma zatayi ta mata nasiha kuma da kud’in da tayi ciniki dashi suke sayan abunda zasu ci ga Candy bata iya hakura da carakfe. wataran kuma ta nimi tsokana azubar da sabulum ta dawo gida tana kuka. Randa ‘yan mutuncinta suke kusa tayi talla tasayar duka tukun ta dawo gida randa batayi niya ba kuma inta zaga tayi d’an ciniki sai ta je gidansu Auta ta kwanta ta shari baccinta tun Hajiya na koranta har ta gaji ta daina in ta gama baccin sai tasai sabulun naira d’ari tukun Candy ta nufi gida. *“`TAGWAYEN MARUBUTA“`* [7:16PM, 9/16/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *NA* _Ummieeluff_ & _Rash kardam_ Page 16~20 Tun hajiya na koranta harta gaji ta daina,data gama baccin sai tasai sabulun naira d’ari tukun candy ta nufi gida. Wata rana duk cinikin datayi tana kashewa wajen cin candy da awara,awajen kawayenta masu rashin ji kamar ita. Tana shiga ta tarda mamanta xaune tanacin gyad’a mai gishiri,da sauri tanufi inda take har tana tuntu’be “laah mamah aina kika siyo gyad’a”? Mamah ta ‘bata rai kamar bada ita takeba. “ni matsalana dake kwad’ayi khadiya baki isa kiga mutum nacin abuba,shikenan kin rinka tambayansa kenan aina yasamu? Toh satowa nayi” nan take candy ta ‘bata rai kamar ta had’iyi kota. “toh mamah danna tambayeki inda kika samu shine xaki rinka min fad’a” nina lura kwanan nan ma ba sona kikeba,kullum sai kinmin fad’a, nan take shagwa’ba ya motsa ta rinka matsan hawaye tana bubbuga kafa. Mamah tayi murmushi tana kallon candy dake ta faman shagwa’ba wani kaunarta na sake shiga zuciyanta..candy akwai rashin ji ammah kullum addu’anta shine Allah ya shirya mata yarinya. Janyo hannunta tayi” zonan yar mamanta,idan banso ki ba inso waye? Ke kad’ai Allah ya mallakamin danake gani inajin dad’i,fad’an nan danake miki bawai kiyayya bace kwad’ayinki yanada yawa,ke kenan daga kinga abu ahannun mutum saikin roka. Wannan hali naki Allah dai yasa kada ki girma dashi..Allah ya yaye miki irin wannan kwad’ayi”. Sannan ta d’auko gyad’ar kulli d’aya ta bata nan take ta hau murna tana cin gyadarta,tana d’an raira waka dad’in gyadar na ratsata. Shiru mamah tayi tana kallonta Allah sarki mutuwa mai raba tsakanin masoya,tasan da mahaifinta nada rai da khadija tagama jin dad’inta sabida shi mutum ne mai zafin nema. Gashi babu yan uwansu akusa balle su taimaka musu,basuda kowa su biyun nan suke rayuwansu. Cikeda son juna. Tana gama cin gyad’ar ta mike ta fice abinda zuwa gidan su Aneesah abokiyar fad’anta..tana shiga ta’tarda Anush nacin shinkafa da manja habawa da sauri ta nufi inda take ko sallamah babu tasaka hannu har Anush ta tsorata..haka sukayita wawa akan abincin har candy ta cinye tafara zare idanu “akwai wani ne”? Haushi yasa Anush wanka mata mari suka kwashi dambe suna zage’zage. *TAGWAYEN MARUBUTA* [9:00AM, 9/17/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *Na* *Rash Kardam* *Ummieluff* Page *21~25* Haushi ya yasa Anush ta wanka mata mari mai lafiya Candy ta ce “kutumelesi cabd’i yau ba zan yarda in kuma na yarda na dan k’are anan guri”. Kafin Aneesa tayi wani yunk’uri tuni Candy ta d’agata sama ta nuna kafin ta makata a k’asa ta d’ale ruwan cikinta Candy sai jibgar Aneesa ta ke kamar ta samu jaka. Ihun Aneesa ne yasaka Mamanta fotowa da sauri tana fad’in “lafiya Aneesa mai ya same….”. Kasa karasawa tayi ganin Candy a kan Aneesa tana jibgarta da sauri Maman Aneesa ta nufo su Candy na nagin haka ta tashi da gudu tayi k’ofar gida ta rik’e k’uugu ta ce“Aneesa kalli nan wuuuu!”. Ta mata gwalo ta ce“ehe naci shinka fa na more haushi ya kasheki. Ran Maman Aneesa in yayi dubu ya b’aci ta kalli Candy ta ce“kanda kike ko wa naga fitsaranki ya soma yawa fa”. Candy ta kyalkyale da dariya ta marairaice murya ta koyi yanda Maman Aneesa tayi magana ta ce“lah kuji bata iya fad’a ba wai Kanda hahaha!!!”. Ta kece da dariya ran Maman Anee ya k’ara kufula ta juya zata duba bulala Candy ta lallab’o tazo ta zuba ma Aneesa dun- du tare da mari ta yanka aguje tayi k’ofar gida ta mata gwalo ta ce“na daki banza aha gobe ina zo cin shinkafa mutum ya hanani ya gani in masa wanda yafi na yau”. Ta sake gwalo ta fita da gudu Maman Aneesa bak’in ciki y isheta tamkar ta kurma ihu ta ce“Aneesa d’auko gyaleki yau gidansu Kanda zamuje Aneesa ta ce“to Mama amma sunan ba Kanda ake cewa ba Candy ne kinga har tana kwaikwayan maganarki”. Wani tsawa Maman ta daka mata ta ce“rufe min baki sai yanzu kika iya maganan nan ina ta dakaki in banda ihu ba abun da kike mana kin kasa ramawa mtsss!!”. Fuuuuu Maman ta fita Aneesa ta rufa mata baya zasu kai k’aran Candy. Candy tana fita bata zarce ko ina ba sai gun carafke da nan suka fara carafke yayi dad’i Candy ta nason cin gyad’a ta mik’e ta ce“tun d’azu sai cinyeki nake tunda ‘yar bashi muke yi dan haka a gyad’anki zan fanshe bashi na”. Kafin ya rinya ta mik’e Candy ta d’ibi gyad’a tasaka gudu tamkar k’afanta zai tab’a keyarta. Sai da tayi nis sosai ta zauna akan wani hakali ta fara cin gyad’anta tana ‘yar wak’a ta sai da ta cinye ta ce“yanzu ina zn a nufa? Gashi yau ba wani Gidan da ake “`ZAMAN MAKOKI“` bare naje”. Wata zuciya ta ce“ki koma gida kiga halin da Ummaki ke ciki sai ki d’an taya ta aiki ma”. Murmushi tayi ta ce“Allah sarki Umma na kina sona nima ina k’aunarki Allah ya bani kud’i in gina miki k’aton gida kaman Garin Bauchi. *“`TAGWAUEN MARUBUTA“`* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* “`NA“` “`Ummieeluff“` & “`Rash kardam“` Page 26~30 Murmushi tayi tace “Allah sarki ummana kina sona nima ina k’aunarki Allah yabani kud’i in gina miki k’aton gida kaman garin bauchi. Bata wani bata lokaci ba ta kama hanyan gida ahanyanta na tafia ne ta gamu simbiat “yauwa yau wana kama?” simbie ta kama zazzare idanu dan tasan halin mugunta irinna candy. ” ina tambayanki wana kama? Jiya ina rokanki alewan madara kika hanani kika gudu,toh yanzu kinga babu kowa dagani saike in lakad’i banza in more” simbie ta soma komawa da baya tana neman hanyan gudu. Candy na binta “aiyau sai kinci na jaki watarana idan na rokeki abu ki hanani” nan ta cabko wuyan riganta,tun kamin ta fara dukanta simbie ta suma kuka. “kai meya had’aku” sukaji anfad’a daga bayansu. Ammah candy koh ah jikinta taki sakin wuyan riganta. Mutumin ya tsinko bulala yana zuwa,dataga yayi kusa sai ta saki wuyan simbie tareda faska mata wani zaz’zafan mari dayasa simbie sakin ihu ta tsuguna. Taruga ah goge gobema kimin rowa ki gani. Tana shiga layin gidansu ta hango Anush ta mamanta sun nufo hanyan gidansu,da sauri ta buya jikin wani bishiya dan kada su ganta “kambu ammah idan Aneesa tasa ran mamah ya baci saina mata d’an karen duka” suna wucewa tabi bayansu,basu gantaba ahankali take binsu har suka kawo kofan gidan. Ko sallama babu suka shiga cikin gidan.Allah sarki baiwar Allah tanata tsince’tsincen kara da zata had’a wuta.kawai taga mutane ah kanta kerere. ” ah ah maman Aneesa ce sannu da zuwa ga wurin zama” tafad’a tana kokarin shin fid’a musu tabarma. “Kinga ba zama ya kawoni gidanki ba, nazone kijama yarki kunne kada ta sake dukan min d’iya” shiru tayi tana sauraron abinda take fad’a. Yama za’ayi yarinya da gidan ubanta ahanata sakewa, kinsan Aneesa bata iya fad’a ba tana zamanta tanacin abinci wannan kande d’in ta shigo ta cinye mata abinci hakan bai isheta ba ta kara mata da duka” ina mata magana zatamin rashin kunya ta gudu,ai talauci ba hauka bane”.idan ran mama yayi dubu to yabaci. “Yanzu khadijan ce taje tayi miki rashin kunya har gida”? to dan Allah kiyi hakuri idan tazo zanmata fad’a” matsowa tayi wajen Aneesa “kiyi hakuri kinji mamana insha Allah bazata sake dukankiba”. “Inama zata sake ganinta, ki sakawa yarki ah kwa’kwalwarta idan nasake ganin kafanta ko wucewa tayi ta kofana to sainasa an karya mata kafa” janyo Aneesa tayi kamar zata cire mata hannu suka fice daga gidan. Candy dake labe tayi saurin buya dan karsu ganta. Suna wucewa ta fad’o cikin gidan da sauri. Yanda taga fuskan mamah tasan ranta yayi mugun baci. Da sauri ta isa wajenta “mam”…kamin ta karasa mama ta wanka mata mari. Cikeda tsoro candy ke kallonta dan mama bata dukanta, ta manta yaushe rabonda aka zegeta balle harya kaiga mari. “khadija meyasa kike son sa kanki ah bakin mutanene?,bakisan harshe guba bane,kullum saikin nema min abun magana a anguwannan. Haba khadija saikin kasheni, da bakin ciki tukunna zakiji dad’i” da sauri ta dago kanta dan batason ana am’bata mata mutuwa musam’manma mamanta. haka mamata rinka mata fad’a shiru tayi ranta abace..ta kudurta aranta idonta idon Aneesa saita koya mata hankali tunda tasa mamanta bacin rai. *TAGWAYEN MARUBUTA* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *Na* *Rash Kardam* *Ummieluff* Page *31~35* Candy ganin ran Umma ya b’aci sosai gashi bata son abunda zai b’ata mata rai rusunawa tayi ta ce“Ummana dan Allah kiyi hak’uri bazan sake ba Ummana karkiyi fishi dani kinga bani da kowa sai Allah sai ke kinji Ummana”. Umma duk jikinta yayi sanyi Candy ta gama kashe mata jiki a hankali ta furta “zo nan Khadija kece ai amma in kikabar neman tsokana to zamu zauna lafiya da ke”. Candy ta ce“Umma zan bari in dai zakiyi farin ciki”. Umma ta ce“sosai ma zan so ganin hakan Allah ya miki Albarka”. Candy ta amsa da ”amin”. Bayan kwana biyu ana zaman lafiya da Candy talle in ta d’auka ma Umma take ta kan zaga da ikon Allah ya k’are ta dawo gida ko gidansu Autar Hajiya bata zuwa yanzu bata shiga harkan kowa. BAYAN KWANA BIYU… Candy kamar abun kirki har Umma tana murna d’iyarta ta nutsu komai cikin girma take yi da nutsuwa. Yau ta dawo daga talla ta hango Aneesa cikin sauri ta zaga ta bayanta ta ajiye tallan tukun ta shak’o ta, sai da talasa Aneesa tukun ta mak’ureta ta ce“in kika fad’a a gida ko wa Maman ki sai na fasa wannan bakin”. Sake ta tayi ta d’au tallanta tayi gaba. Tun daga nesa ta hango motan gawa an wuce da shi zuwa makabarta a gur-guje ta sayar da sabulun ta ce“Umma barin je gidan su Munay bata jin dad’i zan gai data”. Umma tace“to karki dad’e kice ina gai data Allah ya sauwaka”. Candy ta amsa da “Amin”. Tana fita tayi gidan su Munay da Sallama ta shiga ta gaida Maman Munay ta ce“Inna Munay na nan kuwa?”. Maman Munay ta ce“ki duba d’akinta tananan ta na baccin rashin zuciya”. Da sauri Candy ta shiga tana zuwa ta d’ana wa Munay duka ta ce“ke tashi yau mun samu gun zuwa zamuje cin shefe(shinkafa)”. Da sauri Munay ta tashi ta ce“da gaske ki keyi ne?”. Candy ta ce“eh wallahi dazu naga an wuce da motar gawa amma ban san wani gida bane kawai sai mu gan-gara kasan layi in munga gidan sai mu shiga”. *“`TAGWAYEN MARUBUTA“`* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *NA* *_Ummieluff _* & *_Rash Kardam _* Page *36~40* Candy tace “eh wallahi d’azu naga an wuce da motar gawa,amma bansan wani gida bane kawai sai mu gan-gara kasan layi in munga gidan sai mu shiga”. Munay tace “toh yanzu ta wani layi zamu fara neman gidan”? Gashi wlhy dama yunwa nakeji,kinga umma kubewa ta dafa koh alfarman wake babu,kwanciyan nan da kikaga inayi na bakin ciki ne” candy ta fashe da daria “kaji yar iska yanzu dabance miki anyi rasuwa ba, da ashe mutuwa zakiyi da yunwa,dan nikam na daure naci kwad’on garin kwaki”. “Toh yanzu dai tashi muje”. Munay ta janyo hannunta “ke tsaya kefa bakida wayo,yanzu idan umma ta tambayeki me zamuce”? Candy tayi shiru ta d’aga kai kamar me tunani.”ammah fa kawata kin kawo shawara,toh yanzu me zamu ce da ita”? “Yauwa zo muje nasan mezan ce da’ita”. Suka fito atare munay na kokarin saka hijabinta. “Ummah bari muje mu gaida Asea B Aliu kawarmu mamanta bataji dad’iba jiya aka sallamota daga asibiti”. “Eyyah toh idan kunje ku gaidata da jiki,Allah yakara mata sauki” atare suka had’a baki wajen fad’in”Ammen” sannan suka fice da gudu. “kai ammah kin taimakemu da yau umma bazata bari inje ko inaba” yanzu ta ina zamu fara kenan gashi bamusan gidan ba” kumafa, muje mud’an zagaya mugani”. Haka suka rinka yawo cikin anguwan shiga nan,fita can har suka gaji basuga inda ake zaman makokin ba. Zama sukayi kofan wani gida ishin ruwa ya ishesu..sun rasa ina zasu shiga su samu ruwan sha. Can saiga mai saida pure water.da sauri candy tace “me ruwa” da karfi cikin sauri ya iso wurin. Cikin kakkarfan murya candy tace “bamu na naira goma”,ta d’auki d’aya tana kallon Munay”ke kina kallona bazaki sha bane” munay ta kalleta dan tasan cikinsu babu mai sisi, ammah yaya ta iya ta d’auki guda d’aya tasha itama. Yauwa jiramu anan bari mu karbi canji a wancan shagon, ta nuna masa wani bangare,kamin yaron ya juyo taja hannun munay suka kwasa aguje yaron na binsu, suna gudu har suka bace mishi da gani,yaja musu Allah ya isa. Da kyar suka ‘buya wajen wani gida suna nishi..Munay tace “ammah ke yar iska cefa,kisa musha ruwa ammah bamuda ko sisi”Ke dalla ja dagacan idan kikace zakisha abu sai kinada kud’i toh ashe zaki mutu wata rana”. MunaY zatayi magana sukaji kukan wata mata daga gefensu ta wuce tana kuru’ruwa. Munay ta kalli candy suka had’a baki wajen fad’in laaa ga gidan da ake zaman makokin can. Suka kwasa aguje zuwa gidan, suna isowa kofan gidan sukaga gidane nagani nafad’a,anata shigar da drinks katin- katin..Candy ta rike baki jiki na rawa taja hannun Munay zuwa kofan gidan. *TAGWAYEN MARUBUTA* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *Na* *Rash Kardam* *Ummieluff* Page *41to50* Candy jikinta na rawa ta ja hannu Munay suka nufi k’ofar gidan rasuwan suna zuwa suka gaida mazan da ke *“`ZAMAN MAKOKI“`* a k’ofar gidan. Kayan drinks ake shiga da shi ga manyan jeep suke tsayawa suna ta’aziya suna shiga zauren suka mammatsa idonsu suka fara hawaye kafin suka shiga da kuka. Ga wasu suna zaune sai brush suke da naman saniya manyan tsoka ga wata rantsatsen abinci kai ka d’auka gidan biki ne. Wata Hajiya ce ta shigo ta sha less ta sha gayu kai ka d’auka zab’en kyawawa zata sai wani takun k’asaita take in ka ganta bazaka dauka a gidan mutuwa ta ke ba. Ga wanni lafiyayyen kamshin da ke tashi tamkar tayi b’arin turare. A hankali ta taka zuwa d’akin da ake karb’an tana gai dasu tukun ta dan zauna. Candy da ta sake baki sai kallon matar take yi don ta gama burgeta, Munay ce ta zun gure “ke zo muje muyi abunda ya kawo mu tukun”. Gurin da suka ga ana d’iban abinci nan suka nufa ba kunya su Candy suka saka hannu suka d’au plate suka zuba abinci naman kai d’in kuwa kamar da gayya suka saka tsaban had’ama goran Fanta bibbiyu suka dauka. Gefe suka koma suka fara jan abinci wata Mata ne ta shigo ita ma cikin shiga ta alfarma sai da ta shigo ta hangi wannan Hajiyar nan fa suka fara aika ma junansu da kallon-kallo. Kowacce a tuanninta ta gama kure adaka amma kashh!! Sai gashi sun ga juna kuma duka cikin shigan ba rai ni dalilin da yasaka suka fara kalon-kalo ma junansu. Munay ta kalli Candy ta ce”kiga wa’yannan matan kallon da suke majuna kamar ba gidan rasuwa ba kuma inaga hakan baya rasa nasaba da sun dauwanka mai kyau shiyasa suke kallon-kallo ma junansu”. “Mtss abun da bai dameka ba dad’in ji gareka ina ruwan mu. Kowa yayi abunda ya ficce sa mu ba gashi cin shefe(shinkafa) shi ya kawo mu, kawai muyi mu tafi”. Mai sayar da pure wata ya bi su Candy bai gansu ba nan ya tafi yana kuka don ya san sai an dakesa a gida amma duk randa yaga Candy sai ya tara mata jama’a ta bashi kud’insa. Sai da suka kai gejin k’oshi kafin suka sud’ad’e suka bar gidan . Candy na dawowa gida ta canza fiska da sallama ta shiga sai da ta gai da Umma kafin ta ce”kai Umma gsky Munay tana jin jiki amma da sauki har an mata allura ma”. Umma ta ce”ayya Allah ya bata lfy gobe zanje na dubata in Allah ya kai mu”. Idon Candy yayi tsuru-tsuru jin gobe Umma zataje duba Munay take wata dabara ta fad’o mata cikin sauri ta ce”la! Umma ai basai kinje ba ma naji kamar Mamanta ta ce gobe da safe zasu je Gashuwa”. Umma ta ce”ayya! Allah ya sauwake ya kai su lafiya”. Bayan kwana biyo komai na tafiya wa Candy lafiya suna zaune a k’ofar gidan su Autan Hajiya nan suka ga wasu Christian sun wuce da motar gawa acikin akwati da alama daga asibiti suka d’auko za’aje bikin birne shi. Da sauri da lakato Munay ta ce”kaa kalli mu hanzarta mubi bayansu don kar su mana nisa da alama ba daga unguwan nan suke ba”. Munay ta mike da sauri ta ce”aikam don yunwa nake ji sosai”. Candy ta jata suka fara sauri suna bin motar kasancewar bata gudu sosi motar a slow take tafiya. Candy ta kalli Munay ta ce”nifa kinsan duk randa banci shinkafan gidan Mutuwa ba bana jin dad’i ji nake kamar ba abinci naci ba shiyasa nake ala-ala ayi mutuwa. Ganin motar ta fara gudu yasa suma suka saka gudu. Motar gawan ta nufi Abuja Road Magajin garin dai-dai Wushishi road ta tsaya, nan suka ga ta faka a k’ofar wani gida aka fito da gwan aka shiga gida basu dad’e ba sai ga motoci aka tafi gun da za’ayi biki. Mutane sun fito sai ihu suke yi suna kira jejous name Candy ta ce”kai nifa yau naka sa kuka fa”. Munay ta ce”ni ma idona kyamas yau”. Candy kamar wacce ta tuna wani abu ta waro hannu zaninta sai ga *ROB* ta ce” mud’an shafa wannan abakin idon mu zai yi hawaye na Umma nane da ta aiken”. Nan fa suka goga kan kace me sai ga hawaye suka fara ihu suna aka shiga mota gun da suka je an sake speakers sai tashi da kida yake yi ga kayan abinci ga su minti da Coc ga Fanta da Mirinda nan jikinsu ya d’aurawa sai bari yake yi sun ga abun nema. Suma ayarin suka bi suka fara rawa aka gama suka ci abinci sannan suka d’ebo goran Fanta kowa bibbiyi a hannusu suka nufo gida. Umma da ke jiran *ROB* harta cire rai can sai ga Candy ido yayi jajazur alamar taci kuka. Da sauri Umma ta taso ta ce”lafiya Candy”. Candy ta mutsuka ido ta ce”naje shagon Kabiru mai provision *ROB* dinsa ya kare ganin kinaso shiyasa nace barin je kasuwan bacci na sayo miki, to a hanya ta tadawowa wani mai mashin ya bugeni ganin banji ciwo yabani hakuri ya sai min Fant”. Ajiyan zuciya Umma ta sauke tace”ai barka tunda bakiji ciqo ba kuma da bai wahalar da kansa ba yasai abu”. Candy ta ce”ai shi yayi niyya ya ban”. Umma ta ce “to angode Allah ya kare na gaba”. BAYAN SHEKARA BIYU…. Yau su Candy ke bikin kammala makarantar primary sun yi shiga ta alfarma Candy ta samu kyaututu ka kasancewarta hazika mai kokari acikin dalubai gifts ta samesu da haka suka gama ta dawo gida Umma sai da tayi hawayen murna. Bayan kwana biyiu sakamako ya fito Candy taci kamarantar gwamnati na jeka ka dawo da ke Kabala Costain ranar murna a gunta ba’a magana wai ita ce zata bababn makaranta ta gama primary da hakan ta nufo gida cike da murna. *“`TAGWAYEN MARUBUTA“`* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* Page 51~60 Tun daga k’ofan gida take ihun kiran sunan Umma!! ta shigo aguje sukaci karo da Umma tana nufo inda take.” kai Khadija harkin tsorata ni wlhy,wane irin kirane wannan sai kace makauniya, ke kullum ba kya sanin kin girma kenan” dariya Candy ta fashe dashi “kai haba Umma daga kiran sunanki saiki tsorata haka,toh yau kiran naki ba fad’a na janyo aka biyo niba”. Hmm” Umma tayi ajiyan zuciya,”toh Allah dai yasa hakan ne”. Tsalle tayi ta d’ane cinyanta yau u Ummah na gama primary d’ina kuma naci makaranta ta jeka ka dawo dake kabala costain,kinga kenan mafarkina zai zamo gaskia,dama kullum burina kenan,Banason naje makarantan kwana sabida bazan iya rabuwa dakeba Ummana”. “Uhumm Khadija yaranta ke damunki,kina yawan mantawa da akwai aure da mutu….” Da sauri ta rufe mata baki “ballema bazaki mutuba muna tare har karshen rayuwanmu”. Tana kai wa nan ta nufi d’aki aguje dan cire uniform d’inta. BAYAN SHEKARA UKKU!! Su Candy an zamo manyan mata komai na budurci yasoma bayyana ajikinta. Cikin sauri tafito sanye da uniform d’inta tayi kyau sosai abinta.”umma nizan wuce dan na kusa yin latti,”toh yar umma da fatan kin cinye d’umamen dana baki, Candy tad’an bata fuska “eyy na cinye umma”,Sannan tafara tafiya umma tace “zo Khadija gad’an guntun naira ashirin ko zaki sai wani abu amakaranta”. Ta karba tareda godiya “toh Allah kiyaye hanya” Tace “amin”. sannan ta kama hanyan tafiya abinta. Taku take cikeda nutsuwa ahankali kamar bata son taka kasa. Rasheeda ta kalleni, ” Ummielurv ammah kina kallon abunda nake kallo kuwa”? Juyawa nayi na kalleta “wlhy kuwa kinga yanda Candy take tafiya a nitse kamar da gaske”. “Nidai ban yarda Candy zata iya canza halinta ba” inji Rash. Da haka dai harta shiga makaranta ta nufi ajinsu wato JS3A tana zuwa aka fara mata ihu. Tana d’aga musu hannu harta zo wajen zamanta. Ta kalli Rabi’at SK “ke matsamin awajen zamana, ai kinsan nice da lungu amma kullum saiki zauna min awaje”. Yanda kuka san bada mutum take magana ba haka Rabee’at ta manna mata.haushi yasa ta kai mata mari tasss!!, kake ji karan marin, sai da wutan idanun Rabee suka d’auke na wucin gadi. Nan take kokawa ta kaure, babu wanda yayi kokarin rabasu dan kowa na tsoron kada fad’an yadawo kansa. D’ane ruwan cikin Rabee’at tayi ta rinka kai mata naushi aciki kamar tasamu jaka. Tun tana kokarin kare kanta harta kasa karfinta yakare. Cikin sauri malamin ya shigo ajin ya daka musu tsaya. Kowa yasamu nutsuwa nan take Candy ta nutsu dan babu wanda take tsoro aduniya irin Malam Muh’d tsawa yadaka mata “u again Khadija, come here ma frnd”. Da sauri ta matso kusa dashi jikinta na rawa kamar mazari dan tasan yau ubanta zata ci. Yasa aka d’aga Rabee tare da zaunar da ita akan kujeranta. Tana mai da nunfashi. Malam Muh’d yasa Candy up n down tun tanayi tana dariya harta fara kuka da majina. Malam Muh’d najin kukan har tsakar kanshi ammah babu yanda zaiyi, yana son ya hukunta’ta tukun tayi hankali. Tun tana kukan ahankali harta wage baki,ta soma ihu. Tsawa yadaka mata “will u keep quit?”. Kai ranan Candy taci kuka ta gode Allah. Sanda yagama darasin sa na lissafi sannan yace taje ta zauna. Da kyar take tafiya zuwa wajen zamanta. Tsayawa yayi yana kallonta cikeda tausayawa. azuciyansa yasan hukuncin da yayi mata yayi tsauri da yawa. Ba yanda ya iya ne Candy bata ji sosai. Da aka tashi kawayenta irinsu Mamu da Kausar suka fara bata hakuri. Kausar tace “kai ammah Malamin nan dan rai nin wayone,in ba dan iska ba me yasa zai baki irin wannan punishment d’in”. Mamu tace “rashin imani mana”.wlhy idan ba kici uban Rabee ba baki burgeniba, Shigiyar yarinya anan da kike kukan fa dariya take miki”. Kausar tayi karaf tace “wlhy malam Muh’d sai mun”…” Candy ta daka mata tsawa “dan Allah ya isa tun d’azu Malam Muh’d ina ruwanku, ni daya wahalar banji haushi ba balle ku, Kowa taji buzzir dake d’uwawunta,munafukan banza, ina kuma dad’i kukaji dayake punishing d’ina” “mustew!!”. ta karya kwana zuwa bin layin gidansu tana di gisa kafa. *TAGWAYEN MARUBUTA* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *NA* *Rash kardam* *Ummieluff* Page *61to70* Jan k’afarta take yi har ta iso k’ofan gida. Sai da ta tsaya k’ofar tana tunani shiga don yanda take jan k’afar. Ta kai minti goma a gun kafin ta shiga cikin gidan da sallamanta. Umma da ke fama da itace a murhu sai hayaki yake yi idonta duk ya kaɗa yayi ja- jazur. Ta joyo tana fifita wuta ta amsa sallaman Candy ganin k’afarta na ɗin gishi, da sauri Umma ta yarda abun fifita, ta nufo gunta ta na ce wa”lafiya Candy mai ya faru dake naga k’afarki na ɗingishi?”. Idon Candy ya ciko da kwalla Umma ta ce”ki faɗa min mana Candy duk hankalina ya tashi”. Hawayen da Candy ke mak’alewa ya zubo, cikin muryan kuka ta ce”Umma ba Malam Muh’d bane don yaga muna faɗa da Rabeer’at ya dake ni, kuma ita ce da niman tsokana”. Umma ta ce”kai amma Allah yayi ma Muh’d ɗinnan albarka da ko zan ganshi da na gode masa”. Candy ta zunɓuro baki ta nufi ɗaki. Umma ruwan zafi ta juye ma Candy ta kai mata bayi. Ta je ɗakin ta ce”ki je ki watsa ruwan zafi zaki ji daɗin jikinki”. Candy ta mike da kyar ta nufi bayi ruwan da zafi haka ta ringa watsawa tana faɗin “washh!!. Sai ta yarfe hannuta sabida zafi. Tana gama wankan ta ɗauro zani ta fito sai taji daɗin jikinta, man zafin da ummah ta ajiye matane,ta shafe dukkan jikinta dashi,sannan ta ɗan samu sa’ida, tayi sallah taci abinci ta sha maganin ciwon jiki,ta kwanta barci mai nauyi ne ya ɗauketa. Candy bata farka ba sai bayan sallah la’asar, ta tashi tayi sallah ta ɗanji daɗin jikinta. Yau zama tayi ko k’ofa bata fita ba dan k’afarta yana ɗan taɓata har yanzu. Zama tayi ta zabga ta gumi tana tunanin kalan dukan da zatayi ma Rabee’at in ta kamata. Washe gari bata je makaranta ba sabida yanda k’afarta ke taɓata amma da sauki. Malam Muh’d yana zaune a gindin bishiyar da yasa ba zama yana kallon wucewarta. Duk ya damu yanda yaga ‘yan latti nata wucewa babu alamanta wani karin abun haushi kusan k’arfe tara ba labarinta. Duk sai yaji zaman Makaranta ya ishesa. A can k’asar zuciyansa kuma cewa ya ke”gaskiya nima ban kyauta ba hukuncin dana bama Candy yayi tsauri inaga hala k’afarta ne ya da meta”. Ajiyar zuciya ya sauke lokacin da yaɗaga kai ya ga har an rufe gate ɗin makaranta. Jiki ba kwari ya mike ya nufi office, yana mai jin haushin kansa sosai akan hukuncin da ya mata. A cikin aji Mamu da Kausar Lurv suna zaune jigum Mamu ta ce”Kausar ki ga har 9:00 yayi Candy bata zo ba ko lafiya”. “Hmm”. Mamu ta sauke ajiyar zuciya ta ce”nima Kausar tun ɗazu nake tunani anya ba k’afarta bane ya dame ta?”. Kausar ta ce”in kuma ta wahala Mamu sai mun daka Rabee’at don ita ce silla, sabida kinga asali gurin zaman Candy ne ta zauna, shi kuma wannan mugun Malami ya dake ta”. Mamu ta ce”nifa yanzu haushi yake ban ya wani saka mana ido baran Candy ma kusan kulum sai ya bata punishment”. Kausar ta ce”ke dai bari kawai in an tashi zamu bi gidansu mu gani”. Malam Muh’d ya tsinci kansa cikin nadaman abunda ya mata da wannan tunanin har aka tashi daga makaranta. Jiki ba kwari ya nufi gida abunsa. Mamu da Kausar suka bi gidan su Candy nan suka samu k’afar yayi sauki, ta kuma shaida musu gobe tana zuwa makaranta. Sallama suka mata suka tafi gida. Washe gari Candy ta tafi makaranta cikin shirin kota kwana don sai ta rama abunda aka mata akan Rabeen Gwaggo….lol.. Malam Muh’d ganin Candy yau yaji sanyi a ransa. Bakar gilashinsa ya mannata wanda ke kara masa kyau, hakan kuma yake basa daman kare ma Candy kallo. Yarinyan tana burgesa gata da k’ok’ari sai dai bataji abunda ke haɗa su da ita kenan kuma baya sake mata. Aji suka shiga akayi ka nan suka zauna ana musu karatu sam Candy bata nuna ma Rabee’atu Gwaggo komai ba. Hakan yasa su Rabee da kwayenta sai dariya da zunɗe suke ma Candy. Ana tashi Candy ta ja su Mamu suka laɓe a wani gida suna kallon su Rabee sun ɗau hanyan gida suna dariyan mugunta akan dukan da akayi ma Candy suna dariya suna faɗa. Sai da suka shiga lungu Candy ta fito da sauri su Mamu ma suka biyo bayanta tana zuwa ta sha gabansu take ido ya raina fata. Rabee tana shirin artawa da gudu Candy ta cafko ta ta haɗa ta da bango nan ta fara jibgarta kamar ta samu jaka. Sai da ta lallasata su Mamu kuma sukaji da yan koren Rabee. Su Rabee sai hawaye, Candy ta ce”saura naji kun sanar da wani ko ya je kunnen Malam Muh’d hahaha!!”. Tasaki dariyan mugunta kai ta gir-giza musu alamar kun san sauran. _*“`TAGWAYEN MARUBUTA“`*_ [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* “`Umieelurv & Rash kardam“` Page 91-100. Duk masifa da tsiwan da ta ɗago domin ta masa tana ɗaga kanta sukayi ido huɗu nan take ta nemi masifan ta rasa. Rass!!! Taji kirjinta ya buga arba da tayi da kyakkyawn saurayi, ajin farko wan da duk wata mace ke fatan samunsa. Wani sanyi ya sauka azuciyanta. OMG tafaɗa azuciyanta nan take ta sakar masa ta wani tattausan murmushi daya daɗa fito da kyawunta azahiri. Kafa mata kyakkyawan fararen idanunsa yayi sai murmushi fararen hakoransa suka baiyana. Candy wani daɗi ya mamaye mata zuciya dan bata taɓa tsammanin babban yaro kaman wan’nan zai kulataba,ga kyau ga kuɗi aina gama caɓawa arayuwa in siyama na sabon gida mai kyau nasan Ummana zataji daɗi. *** **** “ah’aaam” yayi gyaran murya wanda sai yanzu Canday ta dawo daga duniyan tunani data shiga. “Tunanin me kikene Beauty?.” Wani daɗi taji da taji ya ambaci kalman beauty taji kamar ta saka ihu. Ina bakin Candy yaki rufuwa sai murmushi take, da kyar ta tattaro nutsuwanta “ah! ah!! Babu komai sauri nake shiyasa Ummana tana jirana.” “Alright dear nima banso tsayar dake akan titi hakaba, sabida ba mutunci,ammah ganinki yasa nakasa juran tafiya ba tare dana miki magana ba” shiru Candyƴ tayi tana sauraron daɗin muryansa. “Toh yanzu dai ba wannan ba gidanku zaki nuna min sai anjima na dawo muyi magana na fahimta ko?”. Cikin sauri Candy tace “eee’ee hakane” cikin sauri ta kwatanta mishi gidansu ko irin jan class ɗinnan babu taga mai kuɗi. “To sai anjima beauty inasha Allahu zanzo anjima inganki,ammah in bazaki damu ba muje mana in ajiyeki.” Candy ta ɗanyi jim kaɗan sannan ta ɗago kai tana kallonsa “please beauty don’t say no” ya faɗa cikin karamin murya. ahankali yafito daga motan yanzune taga zahirin kyawunsa tafiya yake cike da kasaita harya iso ɗaya bangaren tareda buɗe mata kofa ” bismilla muje”. Cikin sauri taje ta shiga motan wani kamshi ya bugi hancinta nan take ta lumshe idanunta… Sanyi takeji yana shiga jikinta gashi ta rasa ta inane wannan sanyi ke ratsata haka dube-dube tasama dan ganin inda sanyin ke fitowa. Tana kak’kare jikinta da hijabin dake jikinta,Tama manta tana tareda wani. ahankali ya furta “o’oo am so sorry beb bari na rage Sanyin AC da alama yana damunki” {haha su candy ba’a taɓa shiga mota me Ac ba lol!} Dai-dai kofan gidansu ya ajiyeta sukayi sallama ta fita daga motan tana tafiya ahankali su Candyƴ harda canza salon tafiya kallonta yake tareda dukan siterin motan da karfi yace “shez so beautiful, i think i’ve found my missin wyf” ahankali yake drivin harya bar layin. “Assalamu Alaikum” Ta shiga gida da sallamanta Umma tagani tana soya kaji masu yawan gaske. Ihu ta shiga gidan dashi “eeee Ummana waya bamu kyautan kaji”? “Ah! Ah!! Khadija aikatau aka bani gobe akwai biki da za’ayi abayan layinmu, yaya kin dawo daga makarantan yaya karatu”?. “Lafiya kalau Ummu, amma yanzu dai yunwa nakeji wlhy ina abincina”? Da hannu Umma ta mata nuni da inda abincin yake. Candy na cin abincin tana kallon kaji da Umma keta faman soyawa. Can taga bazata iya jurewa ba tace “Umma kazan bazamu ɗan-ɗana bane”? “Kinga bana son sakarci kajin mutane ne zamu ɗan-ɗana toni badani ba wannan sakarcin”. Candy taji kamar ta fashe da kuka dan bakin ciki har idanunta suntara hawaye,(kunsan idan mutum ya kwaɗaito da son abu ba’a bashiba yanda yakeji)Tana nan zaune kamar mage. Ummah najin an’kiran sallan la’asar ta mike dan zagayawa bayi. Candy na ganin haka ta isa bakin murhun taɗau cinya babba guda ɗaya. “keee Khadija me kikeyi abakin murhun”? Da sauri ta juyo “babu fa Umma kawai nazo gyara miki icen ne.” “Muga hannunki!” Candy taki ta fara kowama baya ahankali “nace muga hannunki ko bakya jine”? Da sauri candyƴ ta arce ta gefenta aguje.” Zaki dawo ki sameni”. *** *** *** Misalin “`7:30pm“` wani ɗan almajiri yashigo gidan “Assalamu Aleikum wai ana sallama da bauti” Umma dake alwalan sallah isha’i tace ” ayyah yaro ba gidan bane babu bauti agidan nan” mikewa yayi zai fita Candy tayi carap tace “aihoo Ummah nasan gidan su nan suke kwanan’nan suka kauro anguwan nan” bata jira ansan Umma ba taja hannun almajirin suka fice “zo in’nuna maka gidan” suna fita tana hango motan bata bita kan almajirin ba tayi wajen da sauri. Da sallamanta ta’isa wajen kamar abun kirki,ya ansa fuskansa ɗauke da murmushi. azuciyanta tace “wai wannan baya gajiya da murmushi ne? “Barka da zuwa Sarauniyar kyawa’wa” Tayi ɗan murmushi “barka dai ina wuni” Ta gaidasa, “Shigo mana daga ciki” har tayi kamar zata shiga sai ta tuna da sanyin da ke shiga jikinta ɗazo sanda taji ɗan mura-mura. “a’a nan ma yayi wlhy” fitowa yayi daga motan cikin wani lal’lausan farin shadda wanda yaji zubi kamar bada kuɗi aka yisu ba. tsayawa yayi daga gabanta yana murmushi “as u wish ma beauty” “Kamar dai yanda nafaɗa miki ɗazu ina ganinki naji kinyi min,da farko dai ni sunana Abdoul-wahab ina zuwa garinnan tym to tym dan duba yan uwana, Ah Abuja nake aiki ni Manager bank ne FCMB wato first city monument bank, ina shigowa garin nan dake nasoma arba sai naji ajikina lalle na samu matar aure. Idan bazaki damuba zansu sanin wacece ke”?. Cikin muryanta mai matukar sanyaya ran mai karatu tace “sunana Khadija,ammah amfi sanina da Candy”. “Woaw!!!” Ya faɗa yana mai tafa hannu tattare da murmushi “what a nice name Khadija”. Yanda ya furta sunan yasake sa Candyƴcikin wani shauki. Nan dai taɗan labarta masa labarinta. “Toh Khadija bana son rikeki da surutu da yawa dan naga 8:00 yawuce yanzu kozan iya samun number ki”? Cikin sauri ta ansa “banida waya fa”. “toh babu damuwa beauty insha Allahu zan samo miki waya wanda ya dace dake”. Cikin motan yakoma miko mata kuɗi yayi wanda tunda take bata taɓa ganinsuba balle harta rike irunsu, nan take hannunta yaɗau rawa kamar mazari. “karbii mana beauty” Sa hannu tayi carap har tana yakushinsa da kyar ta tat’taro yawun bakinta da nutsuwar ta kamin ta iya furta “nagode”. Tana shiga cikin gidan ta ɓoye kuɗin cikin zaninta. “Aww harkin dawo hala gidan da nisa” “Eee” kawai ta ceda Ummah. Sannan tabi lafiyan gado lumshe idanu tayi tana kallon kayatac’cen murmushinsa wani ihu ta saki tareda rungume pillow a’hankali ta furta wannan shine “`Mr Smiles•“` Kuci gaba da kasancewa tareda mu *TAGWAYEN MARUBUTA* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *Rash Kardam* *Ummieluff* Page 81-90 Ahankali kaunan Candy ya soma mamaye zuciyan Muh’d tun yana iya ɓoyewa har ya kasa controlling feelings ɗinsa gashi baya son raini koh kaɗan. Ko yaya soyayyan zai kasance oho. Gashi in ya zauna bai da tunani sai na Candy in kuma bai sata a ido ba ranan bai da zaman lafiya. Ya ringa sintiri tsakanin aji su Candy da office ɗinsa. Har sai ya ganta kafin ya samu sauki a cikin zuciyar shi don wannan al’amari ya dawo mishi kamar jaraba sai ya ganta ko ya ji muryanta. * * * * Wasu daga cikin ɗaluɓai sun soma zargin wani abu, don yanda Malam Muh’d yasa ma Candy da ‘yan group dinta ido. Abu kaɗan zata yi zai hau faɗa ko punishment, ga wani mayen kallo da yake aika mata ta cikin glashin sa. Candy ko tamkar bata san Allah yayi halitta a gun ba damuwar gabanta take yi. Don ita hasalima haushi Malam Muh’d ke bata. Wani zubin in suna zaune da su Kausar takan ce mata “Candy nifa ina ga Malam Muh’d sonki yake yi, Kiga irin kallon da yake miki ga kuma irin yanda ya samu gaba ina ganin salon nashi soyayyan kenan”. Mamu ta nisa “kin san Allah Kausar nima na jima ina wannan tunanin ga dukkan alamu ya faɗa tarko sonki Candy”. Wanni uwar hararan da Candy ta aika ma su Kausar yasa su jan bakinsu suyi shiru. Cike da masifa ta mik’e ta rik’e kuugu ta wani gir- giza jikinta kalo ɗaya zaka yi ma fiskanta kasan ta kai iya bangon kuluwa don har bakinta yana wani ɓari, idonta ya juya kalar ruwan madaran kwando bala’i ne kaɗai a cikinsa. Kallon da ta musu sai da hantan cikin Kausar ya juya Mamu kam kame-kame ta fara tana bama Candy hakuri don ta san karon su baya kyau. “Kausar ki kama gutun mutunciki ki ja zummar bakinki ki min shiru kin san Allah duk lokacin da kika kara min zance wannan mutumin sai na lahira ya fiki jin daɗi”. Kausar wani miyau ta haɗiye don gaba ɗaya kayan cikinta juyawa suke yi. “To wai ke a likitan luv ko to inaga likitanci ki bai tafi dai-dai akai na ba don banjin son Malam a rai na ina ma zan kai mungu da shi to bari kiji ki kuma buɗe kunnuwanki da kyau……..”. Maganan ne ya makale mata a fatar baki, sakamakon jin kiran da Malam Muh’d ya kwala musu, don ya hango su, kira ya kwala musu don yaga alaman Candy warning take musu. Jin kiran Malam Muh’d ya sa Candy ta soma matsse kafa don wani irin fitsarin da taji yazo mata. Tabbas ta san gwamuwarsu bazata yi kyau ba. Ganin yada take masu Kausar zai ɗauka dukansu zata yi. Ko da suka je sai ya kasa sa su aiki ko tambayansu. Hannu yasa a aljihu ya ciro gudan ɗari ɓiyar sabuwa ya ce”kuje school shop ku sayo min lai dan pure water mai sanyi”. Ya na juyawa Candy ta zauke wani sassayan ajiyar zuciya wanda yaso bama Kausar dariya amma ta make a cikinta sanin halin kawarta Candy. Bayan sun sayo ruwan suka kai masa ya amsa ya nufi office ɗinsu da shi, su Candy kuma suka koma aji a haka har aka tashi kowa ta nufi gida. * * * * Wata mota kirar Frado na hango fara tass tare da bak’ak’eɓ glass a jiki ta fe ya ke mai motar a hankali yana jin wakarsa kalo ɗaya nayi ma fiskansa na gane tsantsan farin ciki gami da jin daɗi dake shimfiɗe a fiskansa. A hankali yake bin wakar tare da gir-giza kansa alamar wakar tana sanya sa nishaɗi da sanyaya masa zuciya. Gayen matashi ne baki mai dogon hanci yana da faɗin kirji ga manyan ido masu fiskan mace, yana da sajen da ya kara kawata fiskansa. Wanda duk inda ake son namiji ya kai. Abdoul-wahab namiji ne mai ji da kwalisa gami da ji da kansa kalo ɗaya zaka masa kasan yana cikin hutu da naira sun zauna masa. Tun daga nesa ya hango cikin tafiyar ta mai ɗaukan hankali a nitse ta ke tafiyar tamkar hawainiya in ka kura ma tafiyarta ido ka ɗauka tausayin kasan take ji ko mu nan sai da ta tafi da tunanin mu. Kalo ɗaya yayi ma bayanta yaji wani abu ya tsarga masa a zuciyarsa tunda ga kwanyar kansa har yatsan kafarsa. Take yaji wani irin abu yana fisgansa gudun mota ya kara yazo dai-dai gabanta ya tsaya. A hankali ya buɗe motar ya fito ya tsaya a gabanta tare da harɗe hannusa a kirji ya zuba mata ido tamkar wani waye don yarinyan ta gama tafiya da shi. Kanta a sunkuye tana tafiya jin mota ya tsaya a gabanta dummm!!! Taji kirjinta ya buga wani irin ruwan kwandon bala’in masifa ya zo mata cike da mafisa da wani tsiwa ta ɗago wanda har kwayan idonta na wani kala-kala. Tana ɗagowa karaf suka haɗa ido take taji wani sanyi ya sauko mata tunga kanta har tafin kafarta. Duk masifa da tsiwanda ta ɗago ido dasu take ta nimesu ta rasa sun gudu. Tirkashi lallefa masu karatu zamuso jin wacce yarinya ce wanna. *“`TAGWAYEN MARUBUTA“`* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* *“`Rash Kardam“`* *“`Ummieluff“`* Page 101-110. Tana shiga cikin gidan ta ɓoye kuɗin cikin zaninta. “Aww harkin dawo hala gidan da nisa” “Eee” kawai ta ceda Ummah. Sannan tabi lafiyan gado lumshe idanu tayi tana kallon kayatac’cen murmushinsa wani ihu ta saki tareda rungume pillow a’hankali ta furta wannan shine “`Mr Smiles•“` Sai da ta gama tunane tunane “`Mr Smiles“` ta tashi ta cire kayan jinkinta, wani dogon riga ta dauko na bacci ta sanya tukun ta hau gado tayi addu’a ta kwanta cike da tunanin saurayinta. Washe gari ya kamata talata ranan Candy da wuri ta shiya zuwa makaranta a cikin kudin da “`Abdoul Wahab“` ya bata ta dauko dubu ɗaya da biyar ta ɓoye a cikin littafinta. Umma ta kalli Candy ta ce”yau bazaki karya bane?”. Take Candy ‘yan hanjinta suka motsa. Cikin yanayin rashin kuzari ta kalli Umma ta ce”zanci amma yau cikina ke ɗan juya min kamar ya ɓaci”. Cikin alhini Umma ta ce”ashsha! Ashsha!! Sannu to ki rage ciye-ciye gudun karya kara ɓata miki ciki. Gashi ba wani kuɗi a hannuna da kin je chemist ki sayo magani. Yanzu ki ɗan shafa toka a saman cikinki zakiji dama- dama”. Duk Umma ta damu akan Candy. Candy ta ɗauko kwanon abinci taci kaɗan ta mike ta ce”Umma na tafi sai na dawo” Ta sa kai ta fita. Tana fita ta nufi wani shagon da ke kan hanya ta sai cake da nutric milk gora uku ta bashi kuɗin ta nufi makaranta. Tana zuwa ta samu ba a wani zo ba, hakan yasa ta ciro cake ɗin taci sannan ta ajiye wa su Mamu nasu. Ba da daɗewa ba su Mamu suka zo nan fa ta mika musu tare da basu labarin komai. Su Kausar sun matukar tayata farinciki da addu’a alkairi, a haka suka ɗau darasin ranan har aka tashi a makaranta. A hanya taga wani karamin restaurant nan ta tsaya tai musu take away biyu na jelop rice da yaji naman saniya akai da maltina gwan- gwani hudu. Ta saka a leda ta nufo hanyan gida. Tana zuwa k’ofar ta ja ta tsaya nan tunaninta ya dawo cikin zuciyarta ta ce”yanzu in an tambaye ince a ina na samu”. Kai ta ɗaga tana nazarin abun can ta saki wani lallausar murmushi ta nufi cikin gidan da karfin gwuiwa tana zuwa kwaɗa sallamanta da karfi “Assalamu’alaikum” Umma ta amsa mata da “Wa’alaikumusalamu”. Ta na shiga kallo daya tayi ma Ummanta ta gane ba abbinci. A hankali ta zauna a tabarma tare da faɗin “washh!! Yau na gaji”. Umma ta kalleta cike da kulawa ta ce”sannu ya makarantan?”. “Alhamdulilah!!”. Candy ta faɗa tare da miko ma Umma laida. Umma ta kalleta ta ce”miye aciki kike miko min?”. Cikin muryan shagwaɓa Candy ta ce”Umma ki buɗe ki gani tukun”. Umma tana buɗewa taga take away cikin kallon tuhuma ta ce”ina kika samo wanan?”. Candy tayi murmushi ta ce”Ummana munje debate ne yau aka rarraba mana nikuma na ɗau har biyu nasan muna da bukata”. Umma ta ce”kinsan ba kyau haka kowa ɗaɗɗaya aka bashi ke ki ɗau ɓiyu”. “Umma ai na faɗa ma Aunty mu ni bazanci a gun ba zanzo dashi gida shiya ma na ɗau biyu kuma ta sani tace ba matsala”. Umma na jin haka ta sauke ajiyar zuciya nan suka ci abimci harda barin saura suka kora da drinks abunsu. Haka Candy tayi ta gudanar da rayuwa cikin kwana uku sai tai dabara sun ci abinci mai kyau. Ba tare da Umma ta gane ta ba. Yau ta kama jumma’a da yamma Candy taci kwaras ɗinta da atamfar sallanta ba laifi tayi kyau sosai. Littafin turanci ne a hannunta tana dubawa wani yaro yazo da sallama. Candy ta ams yaron ya ce”wai ana sallama da Candy a waje”. Umma ta ce”inji waye haka?”. Yaron bai daɗe ba ya dawo ya ce”wai inji “`Abdoul wahab ne”.“` Candy ta ɗan kalli Umma ta ce”kaje kace ina zuwa”. Yarin yana fita, Umma ta ce”Khadija yaushe kika fara hira ban sani ba?”. Candy ta maraice fiska ta ce”Ummi na kiyi hakuri wallahi yana da hankali sosai”. Nan taba ma Umma labarinsa, Umma ganin yarta Candy tana son *ABDOUL WAHAB* yasa ta aminta ta bata izinin fita tare da fatan alkairi. Candy tana zuwa k’ofar gida ta canza salon tafiyarta tamkar wata hawainiya cikin nutsuwa da takama ta ke tafiya. *Abdoul wahab* zuba mata mayatattun idon sa yayi ya kasa ɗauke kansa daga kallonta. Cikin zuciyarsa ko cewa yake”gsky duk cikin matan zamannin banga kamar Candy ba komai nata dabanne ga aji tabbas nasan nan gaba gogewa kaɗan zatayi ta zama mace mai class, mace wuce raini, mace nuna ma sa’a”. Wani lallausan murmushi ya sakar mata dai- dai lokacin da ta karaso gurin. Cikin yanga ta kara make murya ta ce” *Mr Smiles* ka yini lafiya? Ya jumma’a?. Abdoul wahab mutuwar tsaye yayi sabida yanda Candy ke sarrafa bakinta da sunan da ta kirashi da shi. “tabbas baki yi karya ba sunan ya dace dani kuma ya min daɗi gaskiya ni mutum ne mai yawan murmushi.” Candy tayi wani fari da ido kai ka ɗauka wata babbar macece yanda take iyaye, duk ta rikita Abdoul wahab. Cikin kan-kani lokaci suka kara sabawa hira suka yi sosai. Sai dab Magriba Abdoul Wahab ya mata sallama tare da mika mata wasu manyan laidoji guda biyu. Candy ta ki karɓa sai da taga ya bata rai kafin ta amsa ta masa godiya ta shiga gida. Ko da ta shiga Umma faɗa tayi mata na karɓan kaya, nan ma tayi bayani ma Umma akan taki shi ya dage daga karshe Umma ta sanya ma abun albarka kafin suka buɗe kayan da ke ciki kamar haka; riga da skirt guda biyu dogon riga biyu sai atamfa wanda aka dinka biyu da takalma uku da poss uku sai kayan shafe-shafe. Abun dai son barka don kowani kaya Candy tasaka zai haska ta bana wasa ba. Umma taji dadi ta kara godiya da sanya masa albarka. Candy kuma rawan kai zai karu kenan tunda ansoma yin kaya masu kyau…lol.. Bayan kwana biyu Abdoul Wahab yayi mata sayya na kayan makulashe sosai. Ya sai mata waya Samsung Galaxy. Tun daga wanna rana suna makale da juna a waya har ya koma gun aiki. Munay ce ta shigo cikin hanzari ta gaida Umma nan ta tambayi Candy Umma ta ce”tana daki”. Ba tare da bata lokaci ba Munay ta shiga ta samu tana gyara daki tana ganinta suka rungume juna dan murna. Munay ta ce”Candy kin kusa gama aikin ne?”. Candy ta ce”eh shara kawai zanyi shikenan”. “Ok to kiyi muje wani gida ne a kayi rayuwa can unguwan Mu’azu”. Cikin zakwadi Candy ta ce”da gaske?”. Munay ta ce” eh kai har an kai gawar ma yau kwana daya”. Candy ta ce”kai wolla har ina jin yawuna ya tsinke na kwana biyu banci abincin *Gidan rasuwa* ba”. Munay ta ce”ni ma haka”. Ba tare da bata cokaci ba ta gama aiki suka zuga ma Umma karya suka fita. Suna zuwa gidan rasuwa kamar abun arziki sukai ta kuka har sai da aka kawo musu abinci sukaci sannan suka mike suka bar gidan. Zuciyansu dauke da farin ciki kal!! Kamar an musu albishir da gidan aljannah. “Oh!! Muko mukace Hali a jikin rai, mai hali baya fasa halinsa a ko ina yake”. *“`TAGWAYEN MARUBUTA“`* [6:01AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* “`Ummieelurv & Rash kardam“` Page 111-120 Misalin 8:00am Candy na bakin gate na makarantan su tun daga nesa tasan yau zataci duka sabida tayi latti. Malam Muh’d ta gani da wani zabge’gen dorina yana dukan ɗalibai, tun daga nesa ta soma tafia a karkace tana matse cinyoyinta da alama fitsari takeji sosai. Abun har daria ya bamu. _Kneelin down_ aka saka su ammah na Candy dan rashin kunya samun qaramin dutse tayi ta zauna akai babu wanda yake kallonta. Layi’layi ake dukansu har akazo kan candy nan take jikinta ya ɗauki’rawa idanunta suka canza launi nan take hawaye yasoma zubowa. ” kee ni kikeson inzo inda kike da kaina ne”? Cikin saurin Candy ta mike sai ganin dutse yayi a bayanta “owk wato gaki mai wayo kenan kowa nakan kneel ke kina zaune to punshment ɗinki will be double.” Iho ta saka “Malam dan Allah kayi hakuri wlhy na rantse ban zaunaba harna rantse Malam.” Yanda Candy ke rantse-rantse taso bawa Malam Muh’d dariya amma sai ya gintse. Aga bulalan yayi ya zabga mata sau ɗaya ta mike tsaye tana rokonsa da kyar ya bula’leta sau ukku. “Mugu kawai haka zaka kare”, Sannan ta wuce aji tana harare-harare kowa a ajin sanda ya nutsu. “`BAYAN SATI BIYU“` Da dare Candy na kwance tun safe yau basuyi waya da Mr smiles ɗinta ba duk sai taji babu daɗi. Da misalin takwas da rabi taji rurin wayanta kamar bazata ɗauka ba ammah sai tayi tunanin shine. Tana ɗagawa kuwa sai sunansa ta gani bayyane jikin screen ɗin rangaɗa’ɗau. Wani lallausa murmushi ya baiyana akyak’kyawan fuskanta. “Hi handsome! Av’been waitin for ur call since morning,hope all is well with u”? Shiru taji bai ansa taba sai can taji yace “kiyi hakuri dan Allah yau ina cikin tashin hankali mara misaltuwa” mikewa tayi daga kan gadon “OMG meke faruwa haka?wani abune yasameka?” Ta jero masa waɗannan tambayoyi. “mum ɗina ce ta rasu ɗazu da asuba.” “Innalillahi-wa’inna-ilaihi raju’un” candy ta furta tareda dafe kirji. (0o ikon Allah yau Candy ce da jajanta mutuwa) “meya sameta ko dama batada lafia ne”? “lafianta lau wlhy,ɗazu da safe taketa complaining ciwon kai,sai tasha magani daga can shikenan bata tashi ba.” Candy ta zaro ido hankali tashe dan mutuwan ya tsorata’ta. Ahankali ta furta “Allah ya rahamsheta yasa ta huta” muka haɗa baki wajen faɗin {“first in history.”} “ki sanar da mama dan Allah jibi sadakan ukku zanzo sai muje ki gaishesu,” “to shikenan zan sanar da ita Allah kara hakuri.” “Ameen” yace tareda katse wayan. “`WASHE GARI“` Candy na kwance aɗaki tana game da wayanta sun gama waya kenan da Abdoul. Taji an faɗo ɗakin pamm kamar an wurgota har Candy ta tsorata ta yasar da wayan tana neman hanyan ɓuya. “mustew ammah miemie-bee ni bansan ke wace irin sokuwa bace wallahi,bakisan irin haka zai iya saka mutun cikin wani hali bako,yanzu da hawan jini gareni da na mutu.” bee batayi magana ba ta sanu waje daga gefen Candy ta zauna tareda dafata “kawata yau ko zagina kikayi bazai dameni ba,dan nazo miki da daɗa’ɗan labari” candy ta tashi zaune tace ” ke dan Allah”? “Eƴƴ mana ba har zagina kike ba, wani yasuwa akayi anguwan mu, Kinga kuɗi kawata wallahi masu kuɗine na hakika kinga ruwan juice da kaji da ake goge hakora da wanke makoshi. “mustew shine kike son kasheni sabida ɗan wannan”? Toh bazani ba dallah ki kyaleni ina cikin jimamin mamar mijinda zan aura ta rasu.” wangale baki miemie-bee tayi cikeda mamaki Candy gidan *Zaman makoki* nefa” “ke ba gidan zaman makokiba ko inane bani zuwa ayau” da kyar dai bee ta zuga Candy zuwa gidan makokin da aƙe. wannan shine karo na farko da Candy taji bataso zuwa gidan zaman makoki ba. Gidan su Munay suka je tare da sanar mata komai cike da murna ta zaro hijab suka fita. Suka kama hanya sai kofan gidan suka bi mutanen da ke ta shiga gidan suna shiga cikin gidan Candy tayi mutuwar tsaye dan yanda taga gidan tsaruwa iya tsaruwa ya tsaru wanda yasata sakin baki tana kallon gidan. Cikin gidan suka nufa nan ne suka sake ganin haɗuwan gidan ammah kowa kuka gani cikin gidan yana cikin bakin cikin rabuwa da mamacin. Abinci aka kawo ga paper soup, gasasshen nama,da kuma drinks ammah babu wanda yayi masa kallo biyu. Su candy sai zazzare idanu akeyi matan tace “bismillah mana” tana nufin su sami wajen zama dan gaida yan uwan mamaci. Ammah ina su a’tsammaninsu ancene suci abincin, habawa suka rufu akan abincin kamar ba gobe basu lura da irin kallonda ake musuba. Wata yar budurwace ta shigo ganin su Candy kasa magana tayi ta tsaya tana ganin ikon Allah. Candy ci take ba sassauci ganin cikinta yasoma dauka sai ta zaro wasu laidan Walima kwaya biyu ta soma juye abincin aciki dai-dai nan wata mata suka shigo da gani kamanin su dayane ko muce ma yarsa ce, tare da *Abdul-wahab* suka shigo dakin cikin razana Candy ta dago ga laida ta shake shi da shinkafa da nama. Turus *Abdul-wahab* suka tsaya. “Yasalam” Candy ta ce take yayan hancin cikinta suka soma juyasa shikenan yau mai aukuwa ra auku. Abin kunya agidan *SURAKAI.* *TAGWAYEN MARUBUTA* [6:02AM, 9/21/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* “`Ummieelurv “` & “`Rashida A Kardam“` Page 121-130 Kasa magana Abdoul yayi dan besan me zai ce ba shi da kansa kunyan yan uwansa ya kamashi he’iz speechless ammah kina ganin idanunsa kinsan akwai matsala dan ransa yayi mutukar ɓaci da abunda Candy tayi masa. Shin wannnan wace irin macece? Shin mema yakaishi neman yarinya irin Candy? Shin meyasa bai yi bincike ba kawai ya afka soyayyah da ita? Shin me yan uwansa zasu ɗauke sa? Mutuminda bai san abunda yake yi ba mana. Wani zuciya ya sanar dashi. Kallon Candy yake da disappointment a kwayan idanunsa. Baiwar Allah kuma jikinta yayi sanyi sosai wanda bata taɓa tsammanin akwai rana irinta yau da abu irin haka zai sameta ba. Wayyo Allah nashiga ukku. Yanzu yaya soyayyanmu zai kasance? Anya kuwa Abdoul wahab zai yarda da aurena ayanzu? Anyan yan uwansa zasu sake yarda dani kuwa? Innalillahi-inna’ilaihi Raju’un ya Allah ina neman mafita agarwka. Da kyar Abdoul wahab ya buɗi baki yace “Yanzu Khadija abunda kika yimin kin kyauta kenan? Yaya za’ayi kizo gidanmu ki zubda min mutunci ki kuma zubdawa kanki mutunci,wane irin rayuwane kika sawa kanki? Kina ganin abin burgewa ne kizu gidan makoki kike cin abinci kina nishaɗi,bakya tunanin kema wata rana naki zai iya rasuwa azo gidanku amiki irin abinda kika min yaya zakiji kenan?”. Ee’e nasan bai kamata azo gidan makoki ayita ihu da koke’koke marasa amfaniba,hasalima anfison ku zauna daga gefen wacce akayiwa rasuwan kuke ɗan hira dan yaɗan rage mata kunci da takeji agame da rashin da akayi mata. Ammah kirasa abunda zai saki nishaɗi sai zuwa gidan makoki bama dan jajanta musuba a’a ke kawai dan kice abu mai daɗi. Baki damu dame yan uwan mamacin zasu jiba ganim suna bakin ciki,keko kina farin ciki. Kiduba wannan mahaifiyata ce tarasu duk da naji zafin rasuwan’ta ammah abinda kika min yafi yimin zafi dan kin nuna baki damu da damuwana ba, ya nuna bakya *tare’da ni* kenan,mahaifiya tace ba taki ba, haka Khadija abunda zaki saka min dashi kena? Duk irin tsananin so da kauna dana nuna miki,na kudiri niyar mayar dake u’war ya’yana,ashe Allah yataimake ni daban aureki ba kika haifamin yara masu irin halayenki, Kaichona.” banda kuka babu abinda Candy take Arayuwa bata taɓa soyayya ba sai akan Abdoul,bayan Ummanta babu wanda take jinshi har’a zuciyanta irinshi. Abdoul shi kaɗai nakeso banajin zan’iya kaunan wani kamarshi gashi yanzu abinda yasameni kenan. Kai Allah na tuba. Mikewa tayi jiki asanya’ye ta isa garesa “Abdoul nasan nimai laifice agareka ammah ina rokonka dan Allah kayi hakuri,nayi maka alkawarin daga rana irinta yau na daina abinda nakeyi matukar ka yafe min kuma ka yarda zaka aureni wallahi harna rantse maka bansan nan gidanku bane,Abdoul ni yarinyace bansan komaiba banda sonka,dakai nasan me ake nufi da kalman so, *So ɗaya tak* nake maka dan Allah kayi hakuri.” tana kaiwa nan ta fashe da kuka abun gwanin tausayi miemie-bee banda zare idanu babu abinda takeyi awajen duk abinnan dayake faruwa tana rike da ledanta data ɗura zalalan tsokan naman kaza aciki. Kuka Candy take har tsungunawa agaban Abdoul tana rokonsa daya yafe mata. Ɗagota yayi cike da so yana share mata hakaye “ki daina kuka beauty na,yaranta ke damunki na yaff-” bai karasa ba wacce muke tsammanin yayar sace tayi karap ta buge hannun Abdoul tareda fashewa da kuka “Ashe bakada hankali Abdoul,ashe zaka iya zaban soyayyah over mahaifiyarmu wacce ta kawomu duniya.” kuka take harda majina ita adole batason Candy “idan har kana sonta to saida kazaɓa ko mu ko ita-” “a’a haba ya’ya ki daina wannan zancen dan Allah yaya ma zaki soma faɗin irin waɗan’nan muna’nan kalaman.” wani kallo yawatsawa Candy “tashi kije nagode kema wata rana zakiji irin yanda naji nima” kuka take tana rokonsa ammah yaki sauraronta badan ranshi nasoba yakori Candy koran kare daga gidansu idanunsa sun rine jajaye. “a’a dawo mana ki ɗauki ledanki wazaki barmawa”? Candy ko kallon inda Yake batayi ba wannan shine karo na farko da Candy ke ganin kaza da idanunta ammah ta barshi bataci kota sace ba. “kee zoki ɗauka mata” sukace da mie-mie ko kunya babu ta juya zata koma wani irin shaka Candy tayi mata ta rinka janta kamar tinkiya har suka fice zuwa bakin gate. Suna fita tayi wulli da ita tareda watsa mata kyawawan mari guda 2″ Ammah dai miemie-bee Allah ya isa tsakanina dake,har duniya ta naɗe bazan yafe mikiba,sanda nace miki bazan zoba kika nace sanda nazo yanzu me kika janyo min kenan”? Miemie dake kuka tace “wallahi candy kiyi haKuri bansan haka abun zai kasanceba.” ‘dan uwarki da kika sanin ma kin mutunta nine inace komawa kikayi niyyanyi dan ɗauko min leda,wallahi kika sake magana zan ɓabɓallaki munafuka kawai.” miemie zatayi magana candy ta ɗaga hannu kamar zata mareta ta gudu. Kuka take ta shiga gida yanda umma taga idanunta da yanda take kuka yasata rikicewa “ƙhadija meya sameki kike irin wannan kuka haka”? candy babu ansa sai kuka tanason ta faɗa mata tana tsoro “ummah mamar kawata ce ta rasu shiyasa nake kuka” “aiya addu’a yakamata kiyi ba kuka ba kirinks mata addu’a, dafatan dai bakiyi halinkin a gidan zaman makokin ba”?zaro idanu tayi cike da tsoro kamar umma ta ganota. Da haka dai tarinka lallashinta ranan ai candy batayi bacciba,tana rufe idanunta photon abinda yafaru take gani adanunta. Tashi tayi ta zauna tana jimamin rabuwa da mr smiles ɗinta. **** Tun daga wannan ranan Abdoul bai sake bi ta kanta ba. Don yan uwansa sun rabasa da ita. A haka har akayi bakwai ya koma bakin aikinsa. **** Candy duk ta rame ga yawan tunani Umma tayi faɗan har ta gaji sai addu’a take mata. Candy kulum cikin zuba ido take ko Abdoul zai dawo shiru.in takira wayansa baya ɗauka, daga karshe ma yayi blocking ɗinta. Wani sa’in taci kuka a ɗaki ita kaɗai duk damuwan duniya ya isheta. Saukin da ta sami yanzu sam Malam Muh’d baya shiga sabgarta. Ya rage tsangwanta.. **** *BAYAN WATA BIYAR…* Haka rayuwan Candy ya ci gaba da tafiya ga Ummanta yanzu bata da ishashen lafiya yanzu wataran ita ke wankin kuɗin, don ta sama musu abunda zasu ci dana maganin Ummanta. Kullum cikin kuka take da rokon Allah ƴya tashi kafaɗun Ummata ya bata lafiya. *TAGWAYEN MARUBUTA* [8:50PM, 9/22/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* _Rash Kardam_ _Ummieluff_ “`Page 131-140“` Jikin Umma kara tsanani yake yi, Candy duk ta rame kullum cikin kuka ta ke gashi ba yan kuɗi a hannunta. Ga shi yanzu Abdoul ya fita harkanta duk da yanzu bata kansa take ba, ta jinyan Umminta take. Wani sa’in da kyar ta ke samun aikatau tayi kafin ta samu kuɗin magani, rayuwansu ta dawo abar tausayi ga al’umma. Boko ta bar zuwa sai su Mamu da Kausar da ke ɗan leko ta. In sunzo suna bata ɗan kuɗaɗen da suka tara wani sa’in har kukan murna take yi don tabbas su Kausar kawaye ne nagari masu halin kirki. **** Malam Muh’d duniya ta masa kunci tun randa ya samu labarin Candy tayi saurayi ranan har kuka sai da yayi *MAFARKINSA* tana soyayya da wani tasan mai ya kawo sa teaching makarantansu? Anya tasan ko shi waye? Idan kuɗi ta ke so yana da miloyin da zai sayi soyayyarta harma yayi yawa. “Candy sabi da na kasance *TARE DA KE* na bar gata na da yan uwana nazo gare ki. Bana iya bacci sai da photon ki a idona, zuciyata na cike da kaunarki,kaunarki tamkar makullin rayuwata ce”. Ya share wasu zafafan hawaye tare da furzar da iska mai zafi. “Ina sonki Candy naga kina tsananin son Abdoul-wahab bazan rabaki da abunda kike soba, ya zama dole na yi nesa da ke naje naga iyaye na ko zan sami sassaucin suyan da zuciyata ke min”. Mi kewa yayi ya fara har-haɗa kayansa ya bar wanda zai saka kaɗai a waje. Wanka ya shiga bai daɗe ba ya fito sauri-sauri ya gyara jikinsa ya sanya kaya tare da fesa turaruka masu sanyin kamshi. Cikin gidan ya shiga ya musu sallama, ɗakinsa ya dawo ya ɗauki jakarsa ya rataya ɗaya a kafaɗa, ɗaya hannun kuma wani katon photon Candy ne wanda aka zana masa ya zuge trolley ɗinsa ya saka a ciki. A hankali ya janyo trolley ɗin tare da manna bakar glass a fuskansa. Yana fita bai zarce ko ina ba sai gidansu Candy ya ɗan ɓuya a lungu har yazo yaga wucewarta. A hankali ya rinka binta ba tare da ta sani ba yana ɗaukarta photo. Wayar sa ce ta soma ruri cikin hanzari ya ɗaga bayan sun gaisa daga ɗaya bangaren aka sanar masa saura minti talatin jirginsu ya tashi. Cikin sauri ya katse wayar yana wai- wayen Candy har ya tsari ɗan acaɓa sai Airport yana zuwa bai daɗe ba aka masa abunda ya dace jirginsu ya ɗaga zuwa Saudia. Ganin jirgin ya tashi na juyo da sauri na kalli Ummieluff. “Wai nikam waye ne wannan Malam Muh’d ɗin? Iyayensan suna inane da zama? Naji yace zai sai soyayarta da miliyoyin kuɗaɗe?. Kai na ya kulle ina da tambayoyin da nake niman amsa”. Ummieluff ta sauke ajiyar zuciya tare da wani gwauron numfashi. “Yanzu kawai jirgin online network zamu hau mu bisa inaga hakan zai fi mana zaurin cimmasa don mu samu labarin da muke son ji”. Murmushi nayi mata wanda sai da kumatu na ya lotsa. “Yauwa kawalli haka za’ayi”. Na faɗa mata. Tsalle mai kyau mukayi sai cikin jirgi Online Network take ya lula da mu cikin gajimare gudu yake yi salansar jirgin tana bulbula hayaki…lol. tamkar murhum da aka garkama motar icce bata ci. Ba tare da ɓata lokaci ba muka hango jirginsu M Muh’d. Munyi tafiya mai nisa kafin muka iso jiddah nan jirgin mu ya sauka. Muh’d na sauka mota ya shiga zuwa cikin garin Makka nan mahaifinsa ke da zama. Tafiya mai nisa sosai sukayi wanda sai da suka kwana a hanya. Notice kunsan jirgi bata sauka a Makka sai Jiddah. Kar wasu suga munsa hakan wa’yanda basu san da hakan ba. Yana sauka ya sake hawa taxe zuwa wani katafaren unguwa. Dai-dai wani kofar gida mai kyau na gani na fada suka tsaya. Ya ciro kudi ya basa bai tsaya jiran sauran ba ya nufi gate ɗin ya kwan-kwasa mai gadi ya leko ganin Adnan ne ya washe bakin da sauri ya buɗe masa ya shigo. “Ranka shi daɗe kai ne haka ko labarin zuwanka banji ba a gun Hajiya”. Murmushi Muh’d yayi mai bayyana kyansa. “Eh nine suma basu san da zuwana ba sai yanzu inna shiga ciki”. Mai gadi ya masa sannu da zuwa. Muh’d ya nufi cikin gida. Hajiya Fatima da suke falo da Abban Muh’d da sauri suka mike cikin farin ciki suke tambayar lafiyansa. “Abbah da Ummie lafiyata lau haka mutanen 9ja ma duk kalau suke sunce a gaida ku”. Cewar Muh’d. “Mashaa Allah”. Su Abba suka faɗa a tare. Bayan ya huta ya ci abinci nan sukayi hiran yaushe gamo har kusan shaɗayan dare kafin yaje ɗakinsa ya kwanta. Da safe Ummie da kanta ta haɗa masa breakfast mai lafiya bayan sun karya suka taɓa hira nan take tambayarsa Candy da ke yawan bata labarinta. Cikin dabara ya kawar da zancen suka ci gaba da wani hiran. *WAYE MUH’D ADNAN(ADEEL)* Muh’d Adnan haifafen Saudia ne amma Mahaifiyarsa yar Gombe ce sai Mahaifinsa Alhaji Aliyu yahya haihaffen ɗan Mai dugurine karatu ne ya kawosa kasa mai tsarki. Wanda a zuwan Fatima(Ummieluff) Ummurah suka haɗu har suka fara soyayya cikin ikon Allah akayi aure. Daga nan ta dawo Madina da zama. Sun daɗe da Aure kafin Allah ya azurtasu da ɗa guda ɗaya tilo wato Muh’d Adnan suna kiransa da *Adeel.* Adeel ya taso cikin gata har Allah yayi mahaifinsa ya kammala Masters ɗinsa ya fara ɗan aiki a Madina. Bayan wasu shekaru kasancewar ya rike gaskiya da Amana. Nan Allah ya haɗashi da wani balarabe mai suna Alhashim. Alhashim ya kasance mai kuɗi ne sosai yana da rijiyan man fetur. Ganin gaskiyan Alh Aliyu yahya yasa ya ɗaukosa ya ɗaurasa a harkan ba da daɗewa ba shima ya bun kasa ya haɓaka. Ganin hakan yazo gida 9ja ya buɗe gidan mai da campany yin shinkafa da sugar. Bayan wasu shekaru lokacin Adeel ya girma suka zo 9ja ganin yan uwa. Nanne suka ga campany ba wani ci gaba hakan yasa Adeel yace zai zauna tunda ya kammala karatunsa. Wannan shine dalilin zuwansa 9ja da zama. Bayan wasu watanni ya ga komai na campany ya zama dai-dai hakan yaji yana da sha’awar koyarwa hakan yasa yayi interview na teaching yaci bayan nan ya fara koyarwa yana kula da Campany su. Ananne ya ga Candy har ya fara sonta. Kuma wannan shine dalilin da yasa bai koma Saudi da wuri ba sai da Candy ta fara soyayya da Mr Smile. Dalilin da yasa yaji kasan Nigeria ta gun duresa ya shirya barin garin ba shiri. Har ya taho kasar da iyayensa suke wannan shine tarihinsa. ******* Jikin Ummin Candy kara tsanani yake yi wanda hakan yasaka suka je Asibiti. Gado a ka basu likitoti sunyi caa akan Ummi amma abu ya faskara nan suka sa mata drip ganin Candy tana cikin wani hali yasa basu sanar mata komai ba. Da kyar suka barta ta shiga gun Umminta. Ummi ta kama Hannun Candy ta rike cikin nishi da muryan marasa lafiya wanda jiki yayi tsanani ta soma cewa. “Khadijatu ki buɗe kunnuwar ki kiji mai zance miki”. Tari ta ɗanyi kafin ta dafe gefen kirjinta ta lumshe ido ta buɗe. “Khadija ina son ki kasance mai hakuri da juriya a rayuwanki. Kar kiyi wasa da ibada duk rintsi-duk-wuya ki rike amana gaskiya da zumunci. Karki manta da tarbiyan da muka baki koda bayan raina ki kasance mai yi min addu’a da mahaifinki da sauran musulmai. Ki kasance mai taimako a duk inda kika ga mai neman hakan matsawan bai saɓa wa addini ba. Dan Allah kar ki kina niman faɗa ki rinka hakuri duk inda kika samu kanki. Aaah! aaah!! Tayi tari ta cije leɓenta sabida zafin da take akirjinta. Candy ko in banda kuka ba abinda take yi cikin zuciyarta ko sai furta “ina! Umma zaki tashi bazaki mutu ba”. “Khadija ni kam ba tashi zanyi ba tawa ta kare ki kara hakuri a duk inda kika sami kanki. Kasancewar ba wanda zaki zauna a gunsa in kin samu miji kiyi aure. Ko zaki yi karatu sai bayan kinyi aure don gidan mijikin shine mutunciki. Martaban mace shine gidan mijinta..dan Allah khadija ki daina zuwa gidan *ZAMAN MAKOKI*Wanda nasan ya riga yazame miki jika ayanzu”. Cikin sauri candy ta suma girgiza mata kai” wallahi ummuh nadaina daga yau” murmusawa ummah tayi sannan ahankali ta furta “Allah miki albarka” Nasiha sosai tayi ma Candy. Candy in banda kuka ba abinda take yi. Ummi ta fara wani irin tari tana kakari tana salati idon ta suka soma kafewa a sama. Candy ganin haka ta kurma kara tana kiran “Ummi! Ummina!! dan Allah kar ki tafi ki barni in kin tafi wa zan zauna dashi. Ko kin manta ke ce gatana,da ke kaɗai nake gani nayi murmushi banda kowa sai Allah sai ke. Ummi karki tafi ki barni ina zan saka kaina? Ina zan zauna? Abba ya tafi kema so kike ki bisa? Zaki bar Candyn ki mai kaunarki. Ummi in nice na dai na rashin ji zan zauna da kowa lafiya zan na duk abunda kike so”. Wani irin kuka Candy take yi mai tsuma zuciya tana jijjiga Umma. Likitoci ne suka shigo suka rike ta tana fisgewa tana kiran Ummanta. Duk fuskata ya jike da hawayen tausayi na ɗago karaf naga Ummieluff itama kukan take yi abun gwanin ban tausayi. Rayuwa kenan. *“`TAGWAYEN MARUBUTA“`* [5:34PM, 9/24/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* _Rash Kardam_ _Ummieluff_ *_page 141-150._ Wani irin kuka Candy take yi mai tsuma zuciya tana jijjiga Umma. Likitoci ne suka shigo suka rike ta tana fisgewa tana kiran Ummanta. Suka fita da ita waje tana wani irin kuka mai tsuma zuciya ɗauke da tausayi a ciki. Dai-dai lokacin sai ga Baban Munay yazo duba su da Mamanta sun iso suka taras da rasuwan Ummin Candy jikinsu yayi sanyi. Maman Munay har ta fara kuka ita ta rike Candy Baban Munay yasa su a keke Napep suka dawo gida. Shikuma ya samo mota da wasu bayin Allah suka dawo da gawanta gida. Rayuwa kenan dukkan wani rai sai ya ɗan- ɗani mutuwa. A haka aka shirya Umma nan a kazo za’afita dan mata Sallah akaita gidanta na gasky. Candy na ganin haka ta kurma kara tana bori tana ture masu riketa da gudu taje ta rike makaranta tana kuka “Umma pls ki tashi kice wasa kike min kin ga zasu tafi da ke. Banda kowa sai Allah sai ke in kin tafi ya zanyi. Wayyo Umma na mai kaunata ki tashi daga yau zan ji duk abunda zaki ce min. Ko gidan makoki ma na bar zuwa ki yarda dani Umma sauko mu tafi ɗaki”. Duk wanda ke gun sai da ya zubar da hawaye don Candy abun a tausaya mata ne bata da kowa yanzu sai Allah. Baban Munay yayi karfin halin janyeta daga makaran tana turjewa aka shiga da ita ɗakin su. Maman Munay ta ce“Khadija kiyi hakuri kin san abunda kike haramun ne ba kyau. Yin kuka kana kururuwa ga mamaci kina da sanin ki mai yasa kike haka? Ayanzu Umma addu’a ki tafi bukata ba kuka ba. Ki sani duk kaunan da kike mata Allah da ya karɓeta yafi ki sonta ki yi hakuri addu’a zaki mata”. Nasiha sosai ta mata mai ratsa zuciya. A hankali Candy ta bar kukan sai sauke zuciya take tana hawayen. Bayan an kai Umma makwancinta na gsky. Gida ya cika fam da yan gaisuwa. Da yamma aka kawo abbincin sadaka kala- kala Candy bata taɓa jin ta tsani cin abincin gidan mutuwa ba sai yau. Tana zaune ta hango fiskokin da bazata manta da su ba. Wato *Ummu Abrar da Futha da Pherty* suka shigo bayan sunyi gaisuwa suka nimi tabarma suka zauna. Basu daɗe da zuwa ba Candy na halkance da su taga sunyi gun kuloli nan suka buɗe suka fara duba abinci har suka zo kan wanda ya musu suka cika plate. Take zuciyar Candy ya soma suya a rasuwan Mahaifiyarta wasu suka zo cin shinkafan gidam rasuwa. Asai daman haka ake jin idan aka maka rasuwa kaga wasu ba dan Allah suka zo ba? Bata idar da tunani ba taji shewar su da sauri ta ɗago kai wasu ta gani suna tsaye da su *Pherty,* *Futha* da *Ummu Abrar* sunci kwaliya kamar masu zuwa paty, sun daɗe suna hira kafin wayanda suka shigo kafin suma suka je suka ɗau plate suka ɗibi abincin suka nimi gu suka zauna. Candy ɗaki ta koma ta barke da sabon kuka lalle yau taji ɗacin da ake ji in an maka wannan abun tabbas sai yau take dana sanin zuwanta *GIDAN MAKOKI* da take yi yau taga ilar abun da ciwonsa. Washe gari bayan sun karya ta na zaune Maman Munay ta liko ta ce“Candy wasu na waje zasu miki ta’aziyya ki same su a zaure”. Jiki ba kwari Candy ta mike ta fito daga gefe ta ga wani ya haɗa kunu da kosai ga ɗan wake a plate duk shi ɗaya ta wuce shi ta fita. Wasu Malamansu na boko ne suka mata gaisuwa tare da nasiha sosai. Kafin suka mata sallama suka tafi ta mike zata shiga gida kenan taji wannan bawan Allah wanda ya ɗibo kunun nan ya ce“Alhamdulilah kai tun da nake zuwa *ZAMAN MAKOKI* Ban taɓa koshi irin na yau ba, aoohh!”. Yayi gyatsa yana murmushi. Sam bai ma lura da Candy ba. Laida sa ya zaro daga aljuhu yafara juye kosan yana cewa “kai amma Allah yasa wata ta kara mutuwa a wannan gidan wani sati don na sake dawowa na sha koko da kosai da kayan tea, da ɗan wake haka nake so gsky *ZAMAN MAKOKI* irin na wannan gidan a kwai daɗi……”. Kasa karasa magar yayi sakamakon ganin Candy tana hawaye a gabansa. Cikin ɓacin rai ta fisge ledar zuciyarta na mata wani irin suya. Cikin kunar rai ta ce” amma tirrr! Da halinka wannan halin ba mai kyau bane anya kana tuna zaka mutu anya kana tsoron Allah kuwa? Baka tunani kai ma akwai randa zaka mutu a maka haka? Shin iyalanka zasu ji daɗin in sunga hakan?”. Hawaye ta share “kaicona ni Candy kasani da bani da abunyi da ya wuce bin gidan mutuwa don nayi *ZAMAN MAKOKI* don kawai naci abincin mutuwa na koshi. Ni har gidan Christer ina zuwa. Ban taɓa tunani ya zasuji zafin abun, kunci ko ɗacin abun, sai jiya da aka fara min na gani tabbas nayi nadama da dana sani. Sai gashi kai har kana kara min addu’a a gidan asake mutuwa”. Wasu zafafan hawaye ta sake sharewa ta ci gaba da cewa. “Yau nayi nadama gami da danasani kuma nayi alkawarin canza ɗabi’una. Bawan Allah kaji tsoron Allah ka tuba ka dai na don in baka gyara ba wataran zakayi danasani kamar yanda nake yi yanzu”. Bata jira amsan sa ba ta sa kai ta shiga gida. Bawan Allah nan jikinsa duk yayi sanyi yana mai-maita kalaman ta ya fita a zauren. Tare da yin alkawarin daga yau ya bar wannan halin. A haka har akayi sadakan bakwai aka watse Candy duk ta dawo shiru-shiru da ita bata son yawan hayaniya sosai ko cikin sa’aninta in ta zauna ita kaɗai sai dai kaji tana azukar ko ta ɗauko al-qur’ani tana karatu. Rayuwa kenan Candy ta dawo kamar ba ita ba ta bar zuwa ko ina. Duk ta rame kulum tana cikin tunani, in ta tuna abunda tayi a gidansu Mr Smile sai ta zubar da hawaye gashi itama an mata. Ta naso ta kirasa ta basa hakuri tarasa yanda zata yi. *BAYAN KWANA BIYU….* Candy sai da ta nimi gidansu *Ummu Abrar da Futha da Pherty* taje ta musu nasiha kan zuwa *ZAMAN MAKOKI* wanda sai da suka zubar da hawaye. Suka mata alkawarin sun dai na zuwa. Tun ga ranar suka fara mutunci suna kawo mata ziyara. Haka rayuwan Candy ya kasance ita kaɗai a gida. Maman Munay tayi-tayi ta koma gidansu taki kasancewar makwabta suke hakan yasa kulum suna tare da Munay. ****** Adeel duk yana cikin damuwa yana zaune a Madina ne amma hankalinsa na 9ja gun Candy Kulum bai da hiran da ya wuce na Candy duk wanda yasan shi to zai san labarin Candy. Hakan yasa Umman sa tana murna tilon ɗanta ɗaya ya samu macen aure hakan yasa tun bata bata ga Candy ba taji tana sonta. *BAYAN WATA BIYAR…* Muh’d(Adeel) ne kwance akan gadonsa. Idonsa na kallon P.O.P dakin yana sana’arsa na tunanin Candy. Sam ya kasa tsinana komai bai da aiki sai tunanin Candy, wayar sa ne yayi kara har ya tsinke bai ɗauka ba. “mtssw ni fa bana son hayaniya shiyasa na ma cire layin da aka sanni na saka sabo”. Wayar ne ta sake kara kamar ba zai ɗauka ba sai ya ɗaga number 9ja ya gani da sunan Ahmad akan wayar. A hankali ya ɗaga wayar. “Assalamu’alaikum”. “Wa’alaikumusalam Adeel ina ka shiga ne kwana biyu ina ne man wayarka?”. “Hmmm!!”. Ya sauke gwaron numfashi. “Ahmad ban son hayaniya ne tun da na bar 9ja na rasa Candy na rasa farin ciki na shiya banson hayaniya”. Muh’d (Adeel) ya faɗa. “Muh’d(Adeel) haba ya kake abu kaman bana miji ba? Ko da yaushe ka kasance mai amsan kaddara da hakuri. Kuma in har *Rabo ya rantse* to ba makawa sai ka auri Candy. Ko kamanta *Matar Mutum Kabarinsa* wani baya taɓa auren matar wani. Na kai ina ta niman number ka don in sanar maka da Candy ta rabu da Abdoul wahab”. Cikin razana mai ɗauke da farin ciki Adeel ya ce. “what?!! Mai kake son faɗa min ne? Kana nufin cewar yanzu Candy basa tare da Abdoul?”. Ahmad ya ci gaba da cewa “eh sun daɗe da rabuwa ga mahaifiyarta Allah ya mata rasuwa”. “Innalilahi wa inna ilaihi raji’un”. Abunda Adeel yake nana tawa kenan. “Adeel a yanzu Candy bata da kowa sai Allah kuma yanzu ne ya kamata ka zo ka bayyana kanka in da halima ayi muku aure da ita. Don tana bukatar tai mako gaggawa”. Ahmad ya faɗa. “Allah ya jikanta ya mata rahma. Ahmad satin nan zamu zo ni da Ummie na da Abbah na ayi mai yiwuwa”. “good haka za’ayi sai najika”. Cewan Ahmad. “ok to nagode bye”. Adeel da sauri ya tashi ya nufi falo nan ya samu Ummie da Abbansa ba tare da ɓata lokaci ba yasanarsu komai. Abba ya nisa ya ce. “dole mu fara shiri satin nan zamu 9ja in Allah ya yarda ai *YAYA DA DUKOYA BA’A KETARSU* koda ba sonta kake ba abun a tai maka mata ne. Zamu iya kokarin mu ganin an samo fangin iyayenta”. Da farin ciki Adeel ya bar falon ya fara shiri zuwa 9ja gun abar kaunarsa. A satin su Abba suka gama shirya komai don yau Alhamis jirginsu ya daga zuwa 9ja. Ko da suka sauka a mai duguri garin su Abban Adeel. Nan aka zo aka ɗaukesu bayan sun huta suka ci abinci. Nan Abban Adeel ya sanar ma danginsa akan gobe zasu Kaduna aha ka kowa ya watse. Washe gari suka bi jirgi sai garin Kaduna. Ko da suka isa gidansu kanin baban Adeel suka sauka. Abban Adeel ya sanar musu komai basu dau lokaci ba suka je gun Baban munay. Abban Adeel suka sanar masa da komai. Yayi farin ciki ya ce. “Yanzu ni ba zance komai ba in har yarinya ta amince ba matsala ni zan tsaya mata har ayi aure amatsayin mahaifinta”. Godiya sukayi nan Abban Munay ya shiga gida ya kira Candy. Ko da ta zo nasiha ya mata sannan ya ce. “Khadija wani bawan Allah ne yazo yana sonki sunansa Adeel suna da zama a Madina. Adeel ya dade yana sonki amma ya kasa gaya miki. Har lokacin da yaji kinyi saurayi ya bar kasan sabida ke. Sai daga baya yasamu labarin komai har da rasuwan Ummanki dalilin da yasa yazo kenan”. Ya karashe maganan ya na kallon fiskan Candy. “Khadija ina shawarta ki da kiyi amfani da damanki don wannan masoyi ne na gaskiya kuma kiyi kokari ki bi umar nin Ummanki tace tanaso kiyi aure”. Candy tana kuka tace“Abba na amince tunda na san bazaka taɓa zaba min abunda zai cutar dani ba”. “Allah ya miki albarka”. Ya mike ya sanar musu da ta amince ba matsala. Na suka tsayar da maganan aure nan da sati biyu. Kuma sun dau nayin komai zasuyi sannan suna son ta dawo gidansu Munay gaba daya da zama. Don za’a gyara gidan tunda mallakinta ne. Godiya Abban munay yayi sukayi sallama suka tafi. Adeel bai taba zuwa gun Candy ba itama bata damu da tasan kowa ye mijinta ba. Bayan kwana biyu za’a fara aikin gidan hakan saya tasoma tattaro kayanta zata dawo gidansu Munay. Wata akwati ta dauko a kasan gadonsu duk tayi kura da tsatsa. Da har ta barta, kawai sai taji tana son ta ga miye a cikin a kwatin tayi ta balla kwadon ta kasa. Sai da ta samo tabarya ta rinka dukan akwatin ya balle. Da sauri ta buge wani takarda ta gani da rubutu duk jirwayen ruwa ya bata. Tana kara dago wasu photo ta gani na Ummanta da wanda take tsammanin shine mahai finta. Takardan tasoma warewa ta fara karanta shi kamar haka. *TAGWAYEN MARUBUTA* [10:23PM, 9/24/2016] Rash Kardam: *ZAMAN MAKOKI* _Rash Kardam_ _Ummieluff_ *_Last page_* Ni Ahmad Alkali hai fafen ɗan garin Sokoto ne zamane ya kawo ni nan Kaduna. Amina (sunan Ummin Candy) duk randa ki ka ga wannan sakon ku tafi garin Sakoto unguwan G.R.A gidan Malam Alkali. Sananne mutum ne in kinje ki gabatar da kanki da abunda ke cikinki ki gwada masa wannan photo zai gane ku. Ni kam tawa ta kare ki rike min amanar abunda ke cikinki ki kula da ita ki bata tarbiya tamkar ina raye daga mijinki Ahmad Alkali. Sai mun hadu a darusalam. Hawaye da ya wanke wa Candy fuska na farin cikin sanin danginta bata san lokacin da ta ruga da gudu ta shiga gidan su Munay tana kiran. “Abba! Abba!! Abba!!!”. Tana haki ta iso gabansa ta mika masa ta kardan yana gama karanta wa ya saki murmushi tare da fadin “Allahu Akbar! Allah kenan mai yanda yaso wato bai so Amina taga dangin mijinta ba sai yarta kuma bayan ranta. Tabbas ba sanya yanzu zan sanar da iyayen Adeel a sati nanna zamu tafi”. Waya ya kira ya sanar musu da komai. Cikin murna suka ce a jibi zasu wuce in Allah ya yarda. Bayan kwana biyu Abban Adeel da kansa ya sama musu motoci biyu daya shiga Ummie da sirkanta tana rike da hannuta dayan kuma Baban Munay da Mamanta da Munay. Ko da suka isa Sokoto basu sha walaha ba suka samu gidan tabbas babban gida ne suna zuwa suka bukaci ganin Alhaji Alkali suka sanar masa da komai. Yan uwa suka hadu masu kuka nayi masu murna nayi Alhaji Alkali yana rike da hannu jikarsa. Ya kuma yi na’am da auren yace a garin Sokoto za’a daura nan yace a ci gaba da shirin biki. *WAYE ALHAJI ALKALI* A Alkali haifafen dan garin Sokoto ne babban alkali ne. Yana da yara biyar Fatima ita ce babban yarsa tana Auren Soja wanda suke kiranta da *(Mrs Umar Soja)* Sai kuma Saeed da ke aiki a Bebeji suna kiransa da *(Ya Saeed Bebeji).* sai Abdol-raheem da ke aiki a jega suna kiransa da *(Ya raheem jega)*. Tukunna *Ahmad* (Baban Candy). Sai auntansu Lubabatu tana aure a kano. Sun kasance su kaunar junansu. Rana daya aka nimi Ahmad aka rasa ya fita fatauci sun shiga kunci da damuwa tun suna zuba ido har suka hakura. Wannan shine takaitacen tarihinsu. Duk wani shiri ya kan kama saura kwana biyu biki. Adeel sun kawo lefe na gani na fada kowa ya gani sai ya yaba. Alhaji Alkali walima kawai ya yarda ayi shi. Ranar jumma’a bayan sallah jumma’a dubban mutane suka shaida aure Muh’d (Adeel) Aliyu Yahaya da Khadija(Candy) Ahmad Alkali. Akan sadaki dubu dari haka taro ya watse. Da yamma Candy tayi walima wanda ya hallaci mutane da dama kuma akayi nasiha mai tsuma zuciya. Bayan gama walima iyayenta suka mata nasiha suka bi jirgi zuwa Kaduna don a gun Adeel ya gina gidan da zasu zauna. Gida ne mai kyau sosai gwanin burgewa. Su Candy da Auta suka zauna sai da amgwaye suka zo. Nasiha sosai suka musu kafin suka tafi. Adeel ya taso a hankali yazo kusa da Candy cikin salon kauna ya ce “Amarya ba kya laifi”. Har kwanyanta taji muryan kuma akwai ida tasan muryan amma ta rasa ganewa ga nauyin da take ji bare ta dago ta gansa. A hankali ya yaye gyalen tare da tallabo habarta ya ce “Khadija dago kiga mijinki”. Cikin sauri ta dago wata zata gani Malam Muh’d ido ta murtsuke ko idonta ke mata gizo. Ja da baya ta fara tana hawaye. Adeel ya sauka kasa ya saka gwuiwarsa a kasa ya fara bata hakuri yana fada mata irin kaunar da ke mata tun haduwarsu. Sam yaki kulasa jiki ba kwari ya koma dakinsa. Sannu a hankali Adeel ya soma koya ma Candy soshi har suka shaku sosai. Wanda har sukan iya zama gu daya suka kwana a gado daya. Zaune suke kamar yanda zuka saba cikin dabara da salo Adeel ya soma shafata yana sarrafata ganin kujera ya kasa musu ya daga ta sai gado a hankali ya soma zame mata kayan jikinta. Ganin haka muka bar dakin da sauri. Amatsayin mu na surkai….lol.. Washe gari Adeel shi ya gyara ko ina ya hada musu abun karyawa kar kuso kuga ta rairaya da kauna a gun Adeel da Candy. ****** *BAYAN SHEKARA HUDU* Adeel na hango da Candy tana rike da hannu wata yarinya wanda kamanta sak na Adeel, yarinya mai kyau da ita. Sun sauka a kofar wani gidan da akayi rasuwa Candy ta shiga ciki bayan tayi ta’aziya nan ta hango masu halin irin nata a da, gunsu ta nufa ta soma musu nasiha sosai ta ciro kudi mai yawa ta basu ta fito ta tafi gidan su Munay suka je suka gaida Maman Munay da Babanta nan ma Alheri sosai suka musu daga nan suka shiga gidan Hajiya ta gaida ta ta mata alheri suka tafi. A mota Adeel ya ce“My Candy wai yaushe za’ayi ma Khairat kanwa ne ko Kani?”. Ido Candy ta juya ta ce“oh Abban khairat da wuri haka yaushe aka yaye ta”. Murmushi yayi “gaskiya ina ga zan kara kai mi don ina son ganin yara na da yawa dan haka yau ki shiya duk dare sau shida zanna duty”. Ido ta zaro ta marairaice fiska “wayyo Abban khairat ina zan iya shida fa”. Dariya yayi sosai yace“kaga raguwa kawai”. Itama dariyan tayi. *ALHAMDULILAHI* Nan muka kawo karshen wannan littafi mai suna *ZAMAN MAKOKI* kuskuren da ke ciki Allah ka yafe mana amin. *TSOKACI* Wannan labarin ba wai mun yi shi da ni shadantarwa bane ka dai a’a akwai sakon da mukae son mu isar. Kusani yan uwa yanzu mafi yawanci badan Allah ake zuwa *ZAMAN MAKOKI* ba, sai dan su je cin abinci ko su saka zani mai tsada suna gasa ko gasan kawo abinci mai yawa da kyau. Wanda hakan haramun ne ko mai mutum zai yi yayi domin Allah. Dan Allah masu wannan halin kuji tsoron Allah ku dai na kunga yanda ya faru da Candy a wannan labari ya Allah ka bamu ikon gyarawa amin. *SADAUKARWA* Wannan littafin sadaukarwa ne gareka ɗan mu abin kaunar mu ɗa ɗaya tilo ga *Ummieluff* wato mai suna *MUH’D* *_ (Adeel)_* Allah ya raya mana kai bisa sunnan Annabi mu. Ya Allah ka albarkace shi da sauran ya ramu amin. *TUKWUICI* Wannan Littafin tukwuici ne gare ku: Sanah I .S Matazu Maryam Alkali(Mamu) Khadija Ahmad Alkali(Candy Uwa ta gari) Kausar Luv Ummu Abdoul Autar Hajiya Munay Futha Aneesa Abubakar Rimi Aisha Mazoji Saeed Bebeji Abdoul-wahab(Mr Smile) Abdoul Raheem Jega Aneesa (Anush) Ummu Abrar Aisha Muh’d(Maman Abdoul shakur) Mrs Umar Soja Haneefa Usman Manshat Afreen Zee Maman Khady Khdeey Maryam garba Simbielurv Bintu zaif Serdieylurv Nuceeluff Memie bee Queen Memie Zahrah BB Mesha Luv Ummi Aisha Lubee Mai tafsir Miss Hafsy Mrs Saif Rabee’at Sk mash Fancy (mrs sadiq) *GAISUWA TA MUSAMMAN* Ga dukkan online hausa writers. *GODIYA GA GROUPS* MAMAN ADNAN HAUSA NOVELS RASH KARDAM HAUSA NOVELS 1,2,3 DAN DALIN LUBIEE MAI TAFSIR FENNAT NOVEL MAMU NOVELS DUNIYAR LITTAFI HAUSA NOVELS DUNIYAR MAKARANTA KHALEESAT HAIYDAR NOVELS F/B ANEE NOVELS DAN DALIN AUTAR HAJIYA RAI DANGIN GORO MRS SHAMSUR NOVELS DA SAURAN WAYANDA BAMU AMBATO BA AMANA AFUWA. KUNA RAMMU KUMA MUNA KAUNAR KU. WRITERS WORLD ASS SIMBIELURV NOVELS *UMMIELUFF* *RASH KARDAM* Ku ka sance dani a sabon littafina mai suna *TAR KON KAUNA* yana nan tafe ba da jimawa ba.
Agajahub publishers