Kalaman soyayya masu ratsa Zuciya
SONKI TAMKAR WANI FURE NE DA IDANUWA KE KAWATUWA DA KALLONSA HANCI YAJI KAMSHI RUHI KUMA YA SAMU NUTSUWA
Rayuwatah zayyi dadine idan da ke acikinta daga sanda kika barni Shikenan nazama misaki Mai Rabin jiki Ina kaunarki❤️
Yanda zaka tsara mace a haduwar farko.
Idan kaga baby kaji tashiga ta ratsa zuciyarka kuma kanason yi mata magana kasan me Zakai?
To karanta
Dafarko dai kasami natsuwa sannan ka tabbata kaima kahadu ma’ana kadau wanka mai kyau saboda wanka yana daya daga cikin abunda ke sato maka zuciyara mace saboda sunasan namiji Mai Tsafta
Sannan karka yi mata magana sai ka tabbata gurin da babu mutane sosai don wata tana da alkunya Kuma ba girman mace mace bane Tsayawa a ko’ina.
Daka karasa gurinta dakaje sai kafara yi mata sallama Assalamu Alaiki baiwar Allah kamar yanda addininmu yatanadar nasan indai ta cika musulma zata amsamaka kaga kasamo hankalinta kenan sannan.
Sai kace baiwar Allah kiyi hakuri fah nasan ba mutuncin kyakkyawar mace wadda Batada makusa bane mai haiba da asali tatsaya ta kula namiji a yayin datake tafiya izuwa wani guri,amma kiyi hakuri nima bayin kaina bane wani sashen bangaren jikinane ya uzuramin dole sai nayi hakan tun yayin da idanuwana sukai arba da wannan kyakkyawar surar taki zuciyata tabani umarnin nazo na sameki nagaya maki wani sako.
You may also like this
Ina dauke da sako Mai muhimmanci wanda nakesan Sanar dake Karna cikaki da surutu nasan kina sauri ne saboda haka nake neman wata alfarma guda biyu zuwa ukku agunki inafatan Zaki temakeni .zata cema inajinka.
Don Allah menene sunan wannan Kyakkyawa Sannan sannan kitemakeni da Address dinki ?
Kidaure Nasan abunda na tambaya da girma Amman idan kikabani kintemaki bawan allah
Muddin tacika mace Mai Class zata gayama saboda Kayi komai dadai da yadda kowane Propetional Zaiyi.
Amincin Allah da kariyarsa da yaddarsa su tabbata ga sarauniyar kyawawa.
Tauraruwa mai haskaka duniya.
Gani na zo gare ki ko na samu jin daddadan kalamanki masu sanya
nutsuwa ga mai sauraro.
Sannan na ga kyakkyawar surar da Allah ya ba ki wadda ke samar da farin ciki da nishadi ga mai kallo.
Taku kike tamkar sarauniya, ina so na yi amfani da wannan damar na bayyana mi ki yadda sonki yake a cikin zuciyata,
sonki ya bi jijiya ya ratsa tsoka ya fasa kashi da bargo da ke nake rayuwa sonki shi ne ya zamto jinin jikina.
Yabonki shi ne abincina begenki shi ne ruwan shana, kaunarki ita ta zamto min numfashina, ba zan iya rayuwa ba
idan babu ke.
Ke ce farin ciki na da tunaninki nake kwana da yabonki nake tashi da zancenki nake yini duk motsina na ki ne ke ce farin cikin zuciya ke ce abar alfaharina ke ce kadai idaniyana ke iya gani, ki tallafawa dan marayan da ya rasa duk wani farin ciki don ganin ya same ki.
Ke ce kadai za ki iya dawomin da farin cikina da walwalata da dariyata idan
kika ce ba kya sona zan rasa rayuwata.
By Dan marayan Zaki Prince muhammad
All my life I have searched but never found a girlfriend who is so perfect for me. With you I do not need to worry about the future ♥
Kalaman soyayya masu ratsa Zuciya
Cikin Zuciyata Bazan manta dake ba
Cikin Rayuwata Banga kamar ya keba
Har Ina mance kaina in banganki kusa daniba masoyiya
Assalamu Alaikum yan uwa masu albarka barkan muda wannan lokaci naku akoda yaushe
🌹PRINCE MUHAMMAD🌹
YAU DAI GA RUBUTUN NAWA ABINDA YA KUNSA KARANTA ZAKAJI DADINTA
Inah Masoya Akwai abubuwa da dama wadanda yinsu ko aikata su zaisa mace ta kara sonka
Wadannan abubuwan kuma kowane mutum zai iya yinsu domin ba maganar kudi a ciki bare ace wane mai kudi ne ko wane talaka ne.
Wadannan abubuwan sune kamar haka
1.) Baiwa mace kulawa a koda yaushe.
2.) Ka bata lokacinka.
3.) Ka dinga fadamata kalamai masu sanya-ya zuciya
4.) Ka dinga yabon ta a duk lokacinda tayimaka wani abu, musamman idan tayi kwalliya kacemata Kyakkyawa koda kuwa kyawon ta baikai hakan ba.
5.) ka rarrasheta tareda tausa-san kalamai musamman idan tana cikin halin kunci.
6.) Ka dinga kiranta da wani suna na daban kamar Sweetheart, Baby ko Honey.
7.) Ka turamata sakon mu kwana lafiya dauke da zafafan Kalaman Soyayya masu ratsa zuciya.
8.) Ka turamata sakon barka da safiya tin da safe kafin ta farka.
Dan uwa ka jaraba hakan zaka tabbatarda gaskiya ne.
BY PRINCE MUHAMMAD💗ON TOP KOWA NAKA
AM NOT A BEST, AMMA I WILL TRYING MY BEST
Assalamu Alaikum yan uwana alhummar annabi muhammad s a w barkan muda war HAKA barkan muda( JUMMA’A_KAREEM) Daga naku Prince muhammad KIRANA AKULLUM SHINE MUI AIKI DA LURA yaku Yan uwana
#Kirana_ayau_garekune_mata_
Ashe baki san kullum ana iya rubuta miki zunubi ba! Ko kina bacci ko kina ido biyu ko kina zaune a gidan ki ko kina halin tafiya ko kina yin wani aiki koda kuwa na ibada ne! Wai shin ko kin san mene ya jawo miki diban irin wannan zunubi haka a kullum?
To ba komai bane ya jawo miki hakan ba illa hotunan ki da kike ta sakawa a social media musamman irin wadan da suke bayyana tsiraicin ki kowa yana gani yana fadin duk irin abun da yaga dama a kan ki.
A don haka nake kira a gare mu ‘yan uwa mu guji aikata duk wani abu da zai ringa jawo muna tsinuwar Allah ko ta mutane musamman irin wacce za tayi ta bin mu a kullum har a bayan ran mu😭
Allah Ka Tsare Mu Aikata Duk Wani Abun Ki🤲🏻
Happy Jumma’at Kareem
I think being in love with life is a key to eternal youth.
Ina cikin matsanan cin so matsalan wacce nake Dan ita Bata Sanma ina yibane Dan ita
Sonki tamkar wani fure ne da idanuwa ke kawatuwa da kallonsa, hanci yaji kamshi, ruhi kuma ya samu nitsuwa
ɪᴅᴀɴ ʀᴀʏᴜᴡᴀ ʙᴀᴢᴀᴛᴀ ʏᴜᴡᴜ ʙᴀ ᴛᴀʀᴇ ᴅᴀ ɪsᴋᴀ ʙᴀ, ʜᴀᴋᴀ ɴɪᴍᴀ ʙᴀᴢᴀɴ ɪʏᴀ ʀᴀʏᴜᴡᴀ ʙᴀ ᴛᴀʀᴇ ᴅᴀ ᴋᴇʙᴀ ᴋᴇᴄᴇ ʀᴀʏᴜᴡᴀᴛᴀ ʏᴀ ɢɪᴍʙɪʏᴀ ᴛᴀ
Agajahub publishers