Yanda zaka tsara mace a haduwar farko.
Idan kaga baby kaji tashiga ta ratsa zuciyarka kuma kanason yi mata magana kasan me Zakai?
To karanta
Dafarko dai kasami natsuwa sannan ka tabbata kaima kahadu ma’ana kadau wanka mai kyau saboda wanka yana daya daga cikin abunda ke sato maka zuciyara mace saboda sunasan namiji Mai Tsafta
Sannan karka yi mata magana sai ka tabbata gurin da babu mutane sosai don wata tana da alkunya Kuma ba girman mace mace bane Tsayawa a ko’ina.
Daka karasa gurinta dakaje sai kafara yi mata sallama Assalamu Alaiki baiwar Allah kamar yanda addininmu yatanadar nasan indai ta cika musulma zata amsamaka kaga kasamo hankalinta kenan sannan.
Sai kace baiwar Allah kiyi hakuri fah nasan ba mutuncin kyakkyawar mace wadda Batada makusa bane mai haiba da asali tatsaya ta kula namiji a yayin datake tafiya izuwa wani guri,amma kiyi hakuri nima bayin kaina bane wani sashen bangaren jikinane ya uzuramin dole sai nayi hakan tun yayin da idanuwana sukai arba da wannan kyakkyawar surar taki zuciyata tabani umarnin nazo na sameki nagaya maki wani sako.
Ina dauke da sako Mai muhimmanci wanda nakesan Sanar dake Karna cikaki da surutu nasan kina sauri ne saboda haka nake neman wata alfarma guda biyu zuwa ukku agunki inafatan Zaki temakeni .zata cema inajinka.
Don Allah menene sunan wannan Kyakkyawa Sannan sannan kitemakeni da Address dinki ?
Kidaure Nasan abunda na tambaya da girma Amman idan kikabani kintemaki bawan allah
Muddin tacika mace Mai Class zata gayama saboda Kayi komai dadai da yadda kowane Propetional Zaiyi